Sashe 57
Indo Sarƙa Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata mata na gani a cikin duhun bishiyoyi, fuskarta ɗauke da niƙab. A gaggauce ta ce, "Hadari da kyar na samu lambarka, dan Allah aikin wata yarinya zan baka, akwai adireshin gidansu dana makarantarsu a jikin takardar, banasan a samu matsala kawai ku kashe ta. Na turo muku Million biyu dan Allah banasan a samu matsala." Hadari ƙarɓa yayi yana murmushi ya ce, "Baki da damuwa Hadari baya jagwal, ki baza kunne nan da ƴan awanni zakiji sanarwar mutuwarta." da sauri ta bar gurin saboda batasan ta samu matsala.
Su Indo sun fito daga makaranta Direbansu ta hango, da sauri ta ƙarasa tana yiwa ƙawayenta sallama. Tana shiga mota wasu mutane da ke cikin wata baƙar mota suka rufawa motar su Indo baya, sai da suka fara barin cikin mutane waɗannan mutanen suka sha gaban motar su Indo. cikin tashin hankali Direban motar yake bin motar da kallo, Indo jikinta banda rawa babu abinda yake yi, mutum biyu ne suka fito daga motar hannunsu ɗauke da bindiga. cikin fargaba direban ya ce, "Humaira ya zamu yi?" Indo tace, "Mu gudu kawai, bani wayarka na kira Daddy." bata rufe baki ba suka ɗaga bindiga sama suna sakin harbi. Wayarsa babbar ya ɗauko ya miƙowa Indo, sai dai kash tana kira babu kuɗi a ciki. Da sauri ta miƙa masa cikin kiɗima ta ce, "Ba kuɗi musty, ba kuɗi" ƙaramar wayarsa me madanne ya miƙa mata, wanda alokacin tuni har sun ƙaraso wajen motar su Indo. Da sauri ta danna lambar Mahaifinta wanda yayi daidai da buɗe murfin ƙofar, da sauri indo ta tura wayar cikin aljihun wandon uniform ɗinta.
Ɗaya daga cikin ƴan fashin ne ya fisgo Indo yana kifeta da mari, da sauri Musty ya fito ya fara roƙonsu, wanda yayi dai-dai da ɗaukan wayar da Alhaji Khalil yayi, kiran da Indo tayi masa.
"Dan Allah maigida kuyi haƙuri kuyi mana rai" Mutumin da baka ganin komai a fuskarsa, sai ƙwayar idonsa ya ce, "Ɗan samari ba gurinka muka zo ba, mun zo ɗaukan wannan yarinyar ne" Jin maganar nan ba ƙaramin ɗaga hankali su yayi ba, Musty ya ce, "Dan Allah ku haɗa dani dan idan na koma bansan me zan cewa mahaifinta ba, wallahi bazan taɓa fita ba. Idan kuma kuɗi kuke so ko nawa ne Alhaji zai bayar..."Tun bai rufe baki ba mutumin ya sakar masa harbi a ƙafa yace, "Ga shaida nan na bar masa dan na rage masa wahalar nema, dan idan ba'a ganku ba gabaɗaya ɗauka za'ayi tana raye mukuma kwangilar kisa aka bamu" yana gama faɗa ya fisgi hannun Indo tana ihu, Musty durƙushe yake yana ɗaga hannu alamun a taimaka masa, yana ji yana gani suka tasa ƙeyar Indo a mota suka tafi da ita.
Musty na nan wani me mashin yazo wucewa ya ganshi tsugunne cikin jini, da sauri ya ƙarasa gunshi dan ganin halin da yake ciki, Musty hanya ya dinga nuna masa yana cewa, "Ka taimaka sun tafi da ita" mutumin tambayarsa ya yi, a take Musty ya bashi labarin abinda ya faru, taimaka masa yayi ya sashi a mota, sannan ya fita cen gurin mutane yayi yekuwar mutane suka taho suka ɗaukeshi suka wuce da shi asibiti.
Alhaji Khalil duk abinda yake faruwa akan kunnensa, sakamakon kiran da Indo tayi masa da wayar Musty bata katse ba. Jikinsa har rawa yake saboda tashin hankali, kiran wayar yake amma ba'a ɗauka ba. Da sauri ya kira Lambar Director ɗin makarantar su Indo, dan tsammaninsa a makaranta ne abinda ya faru. Saboda ruɗewa ya manta da lambar Musty ce aka kirashi, amma yana kiran Director ya shaida masa tuni ɗalibai sun jima da tafiya. Da sauri ya katse ya kira lambar kwamishinan ƴan sanda ya sanar da shi halin da ake ciki, Kwamishina cewa yayi ya tura masa lambar da aka kirashi da ita, zasu bibiyu sahun gurin da suke. Alhaji Khalil tura masa lambar yayi sannan ya fita daga cikin office ɗinsa, ya nufi ofishin Kwamishina dan ƙara jaddada masa. Gudu yake kamar zai tashi sama har a ƙarasa, lokacin da yaje tuni har sun fara tracking ɗin lambar kuma sun tura jami'ansu suna bibiyar sahun makasan da suka tafi da Indo.
Mutanen da suka ɗauki Indo wata hoda suka shaƙa mata, nan take jikinta ya saki ta faɗi ƙasa ba numfashi. Tafiya suka yi me ɗan nisa kamar zasu bar garin, sannan suka shiga cikin wani ƙasurgumin daji, basu wani shiga cen ciki ba sukayi parking ɗin motarsu. Zuwan su babu jimawa Indo ta fara farkowa, Ɗaukkota sukayi kamar wata ƙaramar yarinya, a ƙasa suka wurgar da ita zafin buguwar da taji yasa ta ƙarasa wartsakewa. A zabure ta miƙe zaune tana ja da baya nan take ta tuna abinda ya faru da ita, idanunta ne suka ciko da ƙwallah, haɗa hannuwanta biyu tayi cikin roƙo ta ce, "Ku dubi girman Allah kuyi haƙuri karku cutar dani" Hadari dake cen gefe da yake ƙarewa Indo kallo, ji yayi ta matuƙar birgeshi har zuciyarsa, takowa yayi har gabanta ya tsugunna a gabanta yana ƙarewa laɓɓanta kallo, tana ƙarasa magana yasa ɗan yatsansa a laɓɓanta, sannan ya ce, "Yarinya kwangila aka bamu mu kashe ki, daba dan haka ba dana ƙyaleki amma ba wannan alƙwari, na yaba da kyawunki ƙwarai." Indo girgiza kai ta farayi ta ce, "Duk wanda ya baku wannan kwangilar bansan me na tsare masa ba, tun ina jaririya yake farauta rayuwata ashe har yanzu baza'a barni na huta ba?" Sunkuyar da kai tayi ta ce, "Ku kashe ni kawai, saboda nasan ko baku kasheni yanzu ba dole zasu kasheni. Amma dan Allah inasan idan kun kasheni, ko da da daddare ne ku kai gawa ta ƙofar gidan Mahaifina ayi mun sutura, karku barni dokar daji dan Allah" Indo ta ƙarasa faɗa cikin karaya.
Hadari jikinsa ne yayi sanyi ba yau ya saba irin wannan aikin ba, amma lokaci ɗaya yaji tausayin yarinyar ya kamashi, ganin yanayinsa yasa ɗaya daga cikin yaransa ya ce, "Haba Megida karfa ka ɓata mana harka... " tun kafin ya ƙarasa magana Hadari ya sakar masa harbi a ciki take ya faɗi ko shurawa baiyi ba. Indo zaro ido tayi tana rushewa da kuka, Hadari hannu yasa ya tayar da Indo tsaye yace, "Bazamu kasheta ba zamu tafi da ita ƙasar nijar tunda a cen zamu yada zango, ni zan aureta..." be kai ga rufe baki ba suka ji motar ƴan sanda, suna shirin shiga mota su gudu suka fara sakar musu harbi, mutum biyu ne suka gudu aka kama mutum uku, amma a cikin wanɗanda aka kama harda Hadari.
Indo banda kuka babu abin da take yi, kamata sukayi suka saka a mota, suma su Hadari aka tasa ƙeyarsu zuwa Headquarter ƴan sanda. Alhaji Khalili bai sanar da Mahaifiyar Indo ba saboda yasan nan da nan hankalinta zai tashi, idan ba'ayi sa'a bama hawan jininta yana iya tashi. Sai dai ganin su Indo basu dawo ba yasa ta kira wayar Musty amma a kashe, wayar mijinta ta kira ta sanar dashi, a lokacin nuna mata yayi kamar bai san me yake faruwa ba, ya ce mata zai kira Director makarantasu. Bayan ƴan mintuna ya ƙara kiranta ya ce mata akwai abinda aka zaunar da ɗalibai ake musu, jikinta a sanyaye ta amsa amma wani tsagi daga cikin zuciyarta ya kasa amincewa da maganar mijinta, sai dai batasan ta ƙaryata shi yasa bata musa masa ba. Amma tasan idan har akwai wani muhimman abu da za'a tsaida ɗalibai tun kafin ranar Director yake buga takarda, kowanne ɗalibi ya kaiwa iyayensa. Fahad ne yazo ya same ta cikin jimami bayan ya tambayeta take sanar da shi abinda yake faruwa. Mukullin motarsa ya ɗauka ya nufi makarantar su Indo, domin ya ji ba'asin da za'a zaunar da yara har doshin magriba batare da sanin iyayensu ba. Sai dai yana zuwa ya samu makatarantar a rufe ko megadinta baya nan, da sauri ya kira lambar Kawunsa a nan yake sanar da shi abinda yake faruwa, tare da jan kunnensa akan karya sanarwa da Mahaifiyarta abinda ya faru.
Kai tsaye Fahad cen Headquarter ƴan sandan shima ya wuce hankali a tashe, Su Indo kuwa sai wajen ƙarfe takwas na dare suka ƙarasa Headquarter, lokacin da mahaifinta ya ganta ba ƙaramin farinciki yayi ba, ita kanta Indo rungume shi tayi ta rushe da kuka, cikin kuka ta ce, "Daddy wai me nayi musu da basa so na? Meyasa basa san suga ina rayuwa da Iyayena? Daddy me na aikata masu ne?" kukanta ne ya tsananta fuskarta tayi jawur, tausayinta ne ya kama Fahad saboda ya rasa me ta tsare musu da tun tana cikin tsuma take fuskantar barazana daga garesu, sai dai babban farin cikin da yayi da Allah yasa aka kamasu, yasan ko ba komai zasu faɗi wanda ya sasu wannan mugun aikin. Mahaifinta ƙara riƙeta yayi idanunsa na cikowa da ƙwalla, yasan shi dai duk tsawon rayuwarsa bai taɓa aikatawa wani mugun abun da zai yi masa sakayya da irin wannan abun ba.Godiya ya yi wa Allah, da Allah yasa aka kama waɗannan masu mugun aikin kuma a yanzu ne zai san waye wannan babban maƙiyin nashi.
Kallan Indo ya yi ya ce, "Ina Musty fa?" Indo ta ce, "Tun kafin su tafi dani suka harbe shi" A razane ya ce, "Yana ina yanzu?" Bata bashi amsa ba yaji ankirashi a waya, yana ɗauka aka sanar dashi asibitin da Musty yake da halin da yake ciki. A hanzarce yasa Fahad ya wuce da Indo gida, sai dai razanar da tayi yasa taƙi sakin Mahaifinta dan yanzu ma gani take idan sun tafi wani abu zai iya faruwa dasu. Ya lura da halin da Indo take ciki, cikin lallashi ya ce, "Humaira ba abinda zai faru kinji, kinga ankama su kuma in sha Allah ƙarshen matsalar tazo." Bakin ta na rawa ta ce, "Daddy a gabana suka harbi Musty, kuma a gabana suka kashe ɗan uwansu, nima fa sunce kasheni zasu yi" Fahad ne ya riƙo hannunta cikin tausayi ya ce, "Bazasu kashe ki ba kinji, zo mu wuce gida." Indo kamar wata ƙaramar yarinya, haka ta bishi suka shiga mota sai juye-juye take har suka ƙarasa gida.
Su Indo sun fito daga makaranta Direbansu ta hango, da sauri ta ƙarasa tana yiwa ƙawayenta sallama. Tana shiga mota wasu mutane da ke cikin wata baƙar mota suka rufawa motar su Indo baya, sai da suka fara barin cikin mutane waɗannan mutanen suka sha gaban motar su Indo. cikin tashin hankali Direban motar yake bin motar da kallo, Indo jikinta banda rawa babu abinda yake yi, mutum biyu ne suka fito daga motar hannunsu ɗauke da bindiga. cikin fargaba direban ya ce, "Humaira ya zamu yi?" Indo tace, "Mu gudu kawai, bani wayarka na kira Daddy." bata rufe baki ba suka ɗaga bindiga sama suna sakin harbi. Wayarsa babbar ya ɗauko ya miƙowa Indo, sai dai kash tana kira babu kuɗi a ciki. Da sauri ta miƙa masa cikin kiɗima ta ce, "Ba kuɗi musty, ba kuɗi" ƙaramar wayarsa me madanne ya miƙa mata, wanda alokacin tuni har sun ƙaraso wajen motar su Indo. Da sauri ta danna lambar Mahaifinta wanda yayi daidai da buɗe murfin ƙofar, da sauri indo ta tura wayar cikin aljihun wandon uniform ɗinta.
Ɗaya daga cikin ƴan fashin ne ya fisgo Indo yana kifeta da mari, da sauri Musty ya fito ya fara roƙonsu, wanda yayi dai-dai da ɗaukan wayar da Alhaji Khalil yayi, kiran da Indo tayi masa.
"Dan Allah maigida kuyi haƙuri kuyi mana rai" Mutumin da baka ganin komai a fuskarsa, sai ƙwayar idonsa ya ce, "Ɗan samari ba gurinka muka zo ba, mun zo ɗaukan wannan yarinyar ne" Jin maganar nan ba ƙaramin ɗaga hankali su yayi ba, Musty ya ce, "Dan Allah ku haɗa dani dan idan na koma bansan me zan cewa mahaifinta ba, wallahi bazan taɓa fita ba. Idan kuma kuɗi kuke so ko nawa ne Alhaji zai bayar..."Tun bai rufe baki ba mutumin ya sakar masa harbi a ƙafa yace, "Ga shaida nan na bar masa dan na rage masa wahalar nema, dan idan ba'a ganku ba gabaɗaya ɗauka za'ayi tana raye mukuma kwangilar kisa aka bamu" yana gama faɗa ya fisgi hannun Indo tana ihu, Musty durƙushe yake yana ɗaga hannu alamun a taimaka masa, yana ji yana gani suka tasa ƙeyar Indo a mota suka tafi da ita.
Musty na nan wani me mashin yazo wucewa ya ganshi tsugunne cikin jini, da sauri ya ƙarasa gunshi dan ganin halin da yake ciki, Musty hanya ya dinga nuna masa yana cewa, "Ka taimaka sun tafi da ita" mutumin tambayarsa ya yi, a take Musty ya bashi labarin abinda ya faru, taimaka masa yayi ya sashi a mota, sannan ya fita cen gurin mutane yayi yekuwar mutane suka taho suka ɗaukeshi suka wuce da shi asibiti.
Alhaji Khalil duk abinda yake faruwa akan kunnensa, sakamakon kiran da Indo tayi masa da wayar Musty bata katse ba. Jikinsa har rawa yake saboda tashin hankali, kiran wayar yake amma ba'a ɗauka ba. Da sauri ya kira Lambar Director ɗin makarantar su Indo, dan tsammaninsa a makaranta ne abinda ya faru. Saboda ruɗewa ya manta da lambar Musty ce aka kirashi, amma yana kiran Director ya shaida masa tuni ɗalibai sun jima da tafiya. Da sauri ya katse ya kira lambar kwamishinan ƴan sanda ya sanar da shi halin da ake ciki, Kwamishina cewa yayi ya tura masa lambar da aka kirashi da ita, zasu bibiyu sahun gurin da suke. Alhaji Khalil tura masa lambar yayi sannan ya fita daga cikin office ɗinsa, ya nufi ofishin Kwamishina dan ƙara jaddada masa. Gudu yake kamar zai tashi sama har a ƙarasa, lokacin da yaje tuni har sun fara tracking ɗin lambar kuma sun tura jami'ansu suna bibiyar sahun makasan da suka tafi da Indo.
Mutanen da suka ɗauki Indo wata hoda suka shaƙa mata, nan take jikinta ya saki ta faɗi ƙasa ba numfashi. Tafiya suka yi me ɗan nisa kamar zasu bar garin, sannan suka shiga cikin wani ƙasurgumin daji, basu wani shiga cen ciki ba sukayi parking ɗin motarsu. Zuwan su babu jimawa Indo ta fara farkowa, Ɗaukkota sukayi kamar wata ƙaramar yarinya, a ƙasa suka wurgar da ita zafin buguwar da taji yasa ta ƙarasa wartsakewa. A zabure ta miƙe zaune tana ja da baya nan take ta tuna abinda ya faru da ita, idanunta ne suka ciko da ƙwallah, haɗa hannuwanta biyu tayi cikin roƙo ta ce, "Ku dubi girman Allah kuyi haƙuri karku cutar dani" Hadari dake cen gefe da yake ƙarewa Indo kallo, ji yayi ta matuƙar birgeshi har zuciyarsa, takowa yayi har gabanta ya tsugunna a gabanta yana ƙarewa laɓɓanta kallo, tana ƙarasa magana yasa ɗan yatsansa a laɓɓanta, sannan ya ce, "Yarinya kwangila aka bamu mu kashe ki, daba dan haka ba dana ƙyaleki amma ba wannan alƙwari, na yaba da kyawunki ƙwarai." Indo girgiza kai ta farayi ta ce, "Duk wanda ya baku wannan kwangilar bansan me na tsare masa ba, tun ina jaririya yake farauta rayuwata ashe har yanzu baza'a barni na huta ba?" Sunkuyar da kai tayi ta ce, "Ku kashe ni kawai, saboda nasan ko baku kasheni yanzu ba dole zasu kasheni. Amma dan Allah inasan idan kun kasheni, ko da da daddare ne ku kai gawa ta ƙofar gidan Mahaifina ayi mun sutura, karku barni dokar daji dan Allah" Indo ta ƙarasa faɗa cikin karaya.
Hadari jikinsa ne yayi sanyi ba yau ya saba irin wannan aikin ba, amma lokaci ɗaya yaji tausayin yarinyar ya kamashi, ganin yanayinsa yasa ɗaya daga cikin yaransa ya ce, "Haba Megida karfa ka ɓata mana harka... " tun kafin ya ƙarasa magana Hadari ya sakar masa harbi a ciki take ya faɗi ko shurawa baiyi ba. Indo zaro ido tayi tana rushewa da kuka, Hadari hannu yasa ya tayar da Indo tsaye yace, "Bazamu kasheta ba zamu tafi da ita ƙasar nijar tunda a cen zamu yada zango, ni zan aureta..." be kai ga rufe baki ba suka ji motar ƴan sanda, suna shirin shiga mota su gudu suka fara sakar musu harbi, mutum biyu ne suka gudu aka kama mutum uku, amma a cikin wanɗanda aka kama harda Hadari.
Indo banda kuka babu abin da take yi, kamata sukayi suka saka a mota, suma su Hadari aka tasa ƙeyarsu zuwa Headquarter ƴan sanda. Alhaji Khalili bai sanar da Mahaifiyar Indo ba saboda yasan nan da nan hankalinta zai tashi, idan ba'ayi sa'a bama hawan jininta yana iya tashi. Sai dai ganin su Indo basu dawo ba yasa ta kira wayar Musty amma a kashe, wayar mijinta ta kira ta sanar dashi, a lokacin nuna mata yayi kamar bai san me yake faruwa ba, ya ce mata zai kira Director makarantasu. Bayan ƴan mintuna ya ƙara kiranta ya ce mata akwai abinda aka zaunar da ɗalibai ake musu, jikinta a sanyaye ta amsa amma wani tsagi daga cikin zuciyarta ya kasa amincewa da maganar mijinta, sai dai batasan ta ƙaryata shi yasa bata musa masa ba. Amma tasan idan har akwai wani muhimman abu da za'a tsaida ɗalibai tun kafin ranar Director yake buga takarda, kowanne ɗalibi ya kaiwa iyayensa. Fahad ne yazo ya same ta cikin jimami bayan ya tambayeta take sanar da shi abinda yake faruwa. Mukullin motarsa ya ɗauka ya nufi makarantar su Indo, domin ya ji ba'asin da za'a zaunar da yara har doshin magriba batare da sanin iyayensu ba. Sai dai yana zuwa ya samu makatarantar a rufe ko megadinta baya nan, da sauri ya kira lambar Kawunsa a nan yake sanar da shi abinda yake faruwa, tare da jan kunnensa akan karya sanarwa da Mahaifiyarta abinda ya faru.
Kai tsaye Fahad cen Headquarter ƴan sandan shima ya wuce hankali a tashe, Su Indo kuwa sai wajen ƙarfe takwas na dare suka ƙarasa Headquarter, lokacin da mahaifinta ya ganta ba ƙaramin farinciki yayi ba, ita kanta Indo rungume shi tayi ta rushe da kuka, cikin kuka ta ce, "Daddy wai me nayi musu da basa so na? Meyasa basa san suga ina rayuwa da Iyayena? Daddy me na aikata masu ne?" kukanta ne ya tsananta fuskarta tayi jawur, tausayinta ne ya kama Fahad saboda ya rasa me ta tsare musu da tun tana cikin tsuma take fuskantar barazana daga garesu, sai dai babban farin cikin da yayi da Allah yasa aka kamasu, yasan ko ba komai zasu faɗi wanda ya sasu wannan mugun aikin. Mahaifinta ƙara riƙeta yayi idanunsa na cikowa da ƙwalla, yasan shi dai duk tsawon rayuwarsa bai taɓa aikatawa wani mugun abun da zai yi masa sakayya da irin wannan abun ba.Godiya ya yi wa Allah, da Allah yasa aka kama waɗannan masu mugun aikin kuma a yanzu ne zai san waye wannan babban maƙiyin nashi.
Kallan Indo ya yi ya ce, "Ina Musty fa?" Indo ta ce, "Tun kafin su tafi dani suka harbe shi" A razane ya ce, "Yana ina yanzu?" Bata bashi amsa ba yaji ankirashi a waya, yana ɗauka aka sanar dashi asibitin da Musty yake da halin da yake ciki. A hanzarce yasa Fahad ya wuce da Indo gida, sai dai razanar da tayi yasa taƙi sakin Mahaifinta dan yanzu ma gani take idan sun tafi wani abu zai iya faruwa dasu. Ya lura da halin da Indo take ciki, cikin lallashi ya ce, "Humaira ba abinda zai faru kinji, kinga ankama su kuma in sha Allah ƙarshen matsalar tazo." Bakin ta na rawa ta ce, "Daddy a gabana suka harbi Musty, kuma a gabana suka kashe ɗan uwansu, nima fa sunce kasheni zasu yi" Fahad ne ya riƙo hannunta cikin tausayi ya ce, "Bazasu kashe ki ba kinji, zo mu wuce gida." Indo kamar wata ƙaramar yarinya, haka ta bishi suka shiga mota sai juye-juye take har suka ƙarasa gida.