Sashe 60
Idon Naira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
46
Yau sai kusan yamma ta Gama abinda takeyi a cikin makaranta Dan Haka tana fitowa daga lectures Kai tsaye mota ta nufa a Dan gajiye.
Doguwar A shape ce ajikinta na atampa navy blue wadda tayi Mata kyau sosai sai qaramin Chantilly veil da bvlgari handbag,
Fuskarta ba kwalliyar komai akai
Ta nufo motar tana kalla batareda tayi mamakin sauya motar da Ahmed yayi ba numbern motocin gidansa yasa take ganewa duk lokacinda Ahmed ya sauyo motar daukarta.
Kai tsaye ta qaraso motar
Ahmed ya fito da sauri ya bude Mata kamar yanda ya Saba
A natse ta shiga ba zato tagansa a Bayan zaune cikin milk Yadi Mai taushi da tsadan gaske,
Gabaki daya sanyayyan qamshinsa ya Gama rikita motar
Ba zato ta kallesa da idanuwanta dasuka Dan matse
Bai juyo ya kalleta ba waya yake amsawa ahankali cikin nutsuwa.
Jan motar Ahmed yayi suka bar cikin makarantar
dauke idanuwanta tayi gabaki daya tareda maidawa kan hanya fuskarta ba sakewa ko kadan.
Gama wayarsa yayi ya ajiye ahankali tareda waiwayowa kadan ya kalli gefenta idanuwansa akan qaramin gyalenta dayake gefe daya kawai.
Jin idanuwansa na yawo ajikinta yasata kasa motsi tana Jin zafi na saukar Mata.,
Maida idanuwansa yayi kan farar fatar wuyanta dake bayyane.
Ahankali ya dauke idonsa akai ya bude Baki a natse yace,
Meye wannan din da Kika yafo??
Shiru tayi Masa batareda ta juyoba ko amsawa.
Sake maimaita tambayarsa yayi Nan ma takuma yimasa shiru.
Maida kallonsa kadan yai kan Ahmed Kai tsaye yace,
"Mu wuce gidan Karatu.
Juyowa tayi ahankali Jin abinda yafada taqi kallon fuskarsa dake sake sakar Mata zafi ahankali itama tace,
"Ku ajiye Ni Zan hau drp na qarasa.
Bakinta da yayi maganar ya kalla itama Jin baice komaiba yasata juyowa ta kalli fuskarsa idanuwansu suka hadu a fuske ta Dan janye nata Idon tana kokarin sake magan ya katseta da cewa,
"Meye wannan ajikinki nace??
Jikin nata ta kalla a sace taga gyalenta yake kalla dan Haka saita qi cewa komai.
Ahmed tuni ya kama hanyar gidan Karatu ganin baida niyar sake magana shima saita sake juyowa ta kallesa tana son magana Amma izzarta na hanata Dan Haka tai shiru tareda dauke kanta itama.
Babban gate din gidan Ahmed shige da motar bayan an wangale musu kofar gate din.
Danne zuciyarta tayi yaqi juyowa ta kallesa
Dan jiran takeyi ya fita motar Ahmed ya wuce da ita gida.
Ahmed na parking ya bude motar ya fice Dan Basu guri.
Fitar Ahmed yasata juyowa ta kalli gaban motar zatayi magana ya zuba Mata fararen idanuwansa takasa cewa komai cikin mamakin abinda ya tsaya jira a motar ta Dan kalli gefensa zatayi magana ya katseta ta hanyar bude motar ya fice ba tsammani taji ya bude ta gefenda take cikin kulawa.
Qin juyowa tayi ta kalli kofarma gabaki daya saita fiddo wayarta ta saka Kiran Ahmed Wanda daga shi har securities duka suka bace bat daga harabar gidan suka koma daga waje.
Wayar Ahmed na ringing ya daga ko magana baiyiba AQEEL ASAD ya saka hannuwansa masu tsayi ya karbe wayar daga hannunta cikin nutsuwa tareda sunkuyawa ya dauketa gabaki daya ya nufi ciki ita Yana kallon fuskarta dake bayyanarda fushi da bacin Rai me tsanani.
Bai ajiyeta koinaba sai tsakiyar master bedroom dinsa dake gidan
Yana ajiyeta ta fizge jikinta a zafafe ta nufi kofa ko Isa batayiba Yakuma dawo da ita ta baya
Duk yanda yake kaucewa haduwar jikinsa da nata saida suka hadu sosai ta bayanta ya matseta cikin jikinsa ahankali yana sauraron yanda take kokawar kwacewa.
Fuskarsa yakai wuyanta ya shaqi qamshi data tashi jikinta Mai sanyi na
Boadicea kafin yakai bakinsa kunnenta ahankali ya furta,
Menene wannan din Kika yafa??
Cak ta tsaya daga mutsu mutsun datakeyi sbd numfashin daya sakar Mata Mai zafi a kunne da wuyanta
Yasa zafi sauko Mata tako Ina..
Bai janye bakin nasa daga kunnentaba yasake cewa,
"Uhumm Ina jiranki??
Rintse Ido tayi ta bude qamshinsa da numfashinsa da jikinsa dayake zagaye da nata yasata Jin numfashinta Kamar Yana toshewa ahankali ta zare jikinta tareda matsawa gaba batareda ta bari ta juyoba.
Qarasowa yayi ya Kama hannunta ya dawo da ita kan lafiyayyar sofan sake dakin nasa ya zauna tareda kokarin zaunar da ita Amma ta kafe taqi zaunawar...
Tashi yayi tsaye gabanta kirjinsa na gap da gugar nata ta daga qafa zatayi baya yakai hannunsa ya yangota ahankali ta fado jikinsa ya riqeta da kyau ba tareda ya matsetaba Kamar Wanda bayason takura qashinta.
Haduwarsu hakan yasa numfashinta sake toshewa taqi yarda ta dago Dan batason kallon fuskarsa.
Idanuwansa ya zuba mata Yana Jin gyalen nata data fita dashi Yana yankar zuciyarsa Amma taurin kanta da kafiyarta ya hanata bude Baki tayi magana.
Wuyanta yake kalla zuwa fuskarta dataki kallonsa.
Hannunsa yakai ahankali zai taba gyalen nata tayi saurin dagowa suka hada ido.
Bazata iya jure kallonsa ba Dan Haka ta motsa zata qwace jikinta kirjinsu Yakuma Mannuwa Dana juna..
Ahankali ya janyeta daga jikin nasa da Kansa yana dauke kallonsa daga kanta.
Yana sakinta ta bude kofar bedroom din ta fice fuskarta na bayyanarda bacin Rai da fushi Amma zuciyarta bugawa takeyi da qarfi sbd tsoro da mamakin abinda ya faru din.
Mota ta nufa Kai tsaye ta Shiga ta zauna sai alokacin tasamu numfashinta yafara warwarewa.
Saida tayi mintina hudu a motar kafin ya fito a kame cikin nutsuwa kwarjininsa na qara bayyana Kamar bashine yayi abinda yayi aciki dinba.
Motar yanufa Kai tsaye yashiga daga ita harshi Babu Wanda ya kalli juna saidai qamshinsa datake ji maqale jikinta shima akwai nata qamshin daya mannewa kayansa.
Ahmed yakira a waya da sauri ya taho yashiga motar ya tada suka fice.
Kai tsaye gidan IDON NERA suka nufa akai Amal din kafin ya wuce gidansa Dan dawowarsa kenan daga airport yakira Ahmed din yazo ya daukesa malam Rabiu Kuma ya wuce Kai Al-Amin da gida.
****Haj Maryamah da umma suna Isa gidan IDON NERA Kai tsaye securities suka qi bude musu gate Saida suka sanar da Haj Zainab wadda tayi shiru da mamakin Jin su waye din.
Numfashi ta sauke kafin tace abari su shigo din
Daman tasan zaayi hakan
Sunma Dade Basu zo ba Dan Bata dauka zasuyi shiru har tsawon lokacinba.
Parking sukayi a harabar gidan
Bilkees ce ta tuqo su Kuma bada mufeeda sukazo ba yau din.
Itama haj Zainab tana kashe wayarta daga gate din ta miqe ta sauko kasa Dan Jin meya kawosu gidan Dan idanma akan auren AQEEL ne kofa zata nuna musu su can suyi dashi
Babu Wanda zai kasheta lokacinta baiyiba tana zaune lafiya cikin iyalinta.
Harta sauko Basu qaraso cikiba Dan Haka ta nufi kofa zata taresu tin acan harabar suyi acan saigashi sun shigo Bilkees ce agaba tana yiwa koina gidan kallon qazanta da qyama.
Haj Maryamah da umma ne a baya
wannan karon fuskokinsu Babu alamar sauki da gaske sukeson akawo karshen komai.
Batayi wahalar cewa su zaunaba da tasan ba zaman zsuyib ba Kai tsaye tace,
Lafiya dai inace ba???
Itama Haj Maryamah Bata tsaya batawa kanta lokaciba sbd ta gaji Kai tsaye tace,
"Kin shayar da AQEEL nononki nakeson ji daga bakinki.......
Wani kallo Haj Zainab ta dago tabi Haj Maryamah din dashi cikeda matsanancin mamakin dayafi na koyaushe,
Bata taba tunanin tsanar dasuke Mata takaisu ga rasa ilimin addinin dasuke dashiba.
Siddi data biyo mommyn tana bayanta ta fito bayanta itama cikeda mamaki tace,
"Nono kuma?
Kunsa me kuke fada kuwa?
Shayarda Shi na nufin aurensu ya haramta kenan fa??.....
Katseta Haj Maryamah tayi cikin fushi Mai tsanani da bacin Rai tace,
"Ki ringa tsayar da Yayanki inda Ina magana sbd tarbiyarsu daban take data yayan da muka sani,
Dake nake magana
Amsa Kuma nakeso idan ba hakanba kotu ce zatayimun maganin duk wani mummunan aikinki akan Dana tun Yana qanqaninsa.......
Cikin fushin dayafi na Haj Maryamah din Zainab ta katseta da cewa,
"Indai wannan shine halin yayan da kike magana akai to abarmin yayana ayanda suke din haka sbd jahilci da kaucewa Allah kawai nake hangowa a wannan rayuwar da kike fada..
Katseta itama umma tayi da cewa,
"Amsa aka tambaya ba rayuwar 'yayanki ba Zainab Idon Nera,
Kin shayar da AQEEL nononki ne Kuma sbd son abun duniya Kika Bari ya auri 'yarki da sukasha nono daya
Dan Haka auren ya haramta Babu Wani sauran Bata lokaci a warwaresa kawai.......
"Meyake faruwa Anan?" Sukaji anfada daga bayansu
Dukkaninsu suka juyo gabaki dayansu suna kallonsa.
Ganinsa tareda Amal wadda itama kallo daya tayi musu a ranta dayake baci da baqin cikin ganinsu tace,
"Meyasa duk haukan tsoffin Nan ya motsa anan suke zuwa su sauketa??¿
Bilkees da ganin AQEEL ASAD dinta da Amal din tare yasata sakin Baki zuciyarta na tsalle bakinta na neman bushewa sbd saninsu baya gari tsawon kwanakin to da ita yatafi kokuma Daman baiyi tafiyar bane Yana Nan ya tare???..
Cabdijam" suka fada dukkaninsu atare su ukun
Da Haj Maryamah da umma da Bilkees wadda tafara Jin zafi na shigota ta ko Ina.
Da mamakin ganinsu a gidan shima yasake maimaita tambayarsa fuskarsa akan mahaifiyarsa wadda take kallonsa cikin fushi.
A natse kamewarsa na tsananta ya sake kallonsu kafin ya kalli Mami wadda tagama girgiza da haukarsu ta wannan karon yace,
"Meyake faruwa Anan??....
Zuciyar Bilkees data gama konewa da baqin ciki da takaici babu shakka ko tauna zancen sbd gwara yaji yasan aurensa ya haramta da Amal
Tasan ba lallai sunsha nononba tunanin su umman ne kawai Amma gwara ace sunsha din auren ya watse kowa ya huta...
Kai tsaye tace,
"Maminka ta shayar dakai kana yaro Dan Haka aurenka da......
Wani irin kallon daya juya yayi matane yasa kalmomin bakinta watsewa suna gagara haduwa sbd duk abinda takeyi duk haukarka kallonsa daban ne..
Haj Maryamah dataga Bilkees din ta rude saita qarasa zancen da cewa,
"Aurenka ya haramta anan saika sakar Mata 'yarta....
Ita kanta Amal wani matsanancin mamaki tashiga Jin zancen gabanta yayi wani irin faduwa ta juya ahankali ta kalli mommynta wadda shima ita ya zubawa fararen idanuwansa dasuka sauya take yana jiran maganarta wadda kalma daya zata bude Baki tayi ya fahimci gaskiyar zancen.
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
46
Yau sai kusan yamma ta Gama abinda takeyi a cikin makaranta Dan Haka tana fitowa daga lectures Kai tsaye mota ta nufa a Dan gajiye.
Doguwar A shape ce ajikinta na atampa navy blue wadda tayi Mata kyau sosai sai qaramin Chantilly veil da bvlgari handbag,
Fuskarta ba kwalliyar komai akai
Ta nufo motar tana kalla batareda tayi mamakin sauya motar da Ahmed yayi ba numbern motocin gidansa yasa take ganewa duk lokacinda Ahmed ya sauyo motar daukarta.
Kai tsaye ta qaraso motar
Ahmed ya fito da sauri ya bude Mata kamar yanda ya Saba
A natse ta shiga ba zato tagansa a Bayan zaune cikin milk Yadi Mai taushi da tsadan gaske,
Gabaki daya sanyayyan qamshinsa ya Gama rikita motar
Ba zato ta kallesa da idanuwanta dasuka Dan matse
Bai juyo ya kalleta ba waya yake amsawa ahankali cikin nutsuwa.
Jan motar Ahmed yayi suka bar cikin makarantar
dauke idanuwanta tayi gabaki daya tareda maidawa kan hanya fuskarta ba sakewa ko kadan.
Gama wayarsa yayi ya ajiye ahankali tareda waiwayowa kadan ya kalli gefenta idanuwansa akan qaramin gyalenta dayake gefe daya kawai.
Jin idanuwansa na yawo ajikinta yasata kasa motsi tana Jin zafi na saukar Mata.,
Maida idanuwansa yayi kan farar fatar wuyanta dake bayyane.
Ahankali ya dauke idonsa akai ya bude Baki a natse yace,
Meye wannan din da Kika yafo??
Shiru tayi Masa batareda ta juyoba ko amsawa.
Sake maimaita tambayarsa yayi Nan ma takuma yimasa shiru.
Maida kallonsa kadan yai kan Ahmed Kai tsaye yace,
"Mu wuce gidan Karatu.
Juyowa tayi ahankali Jin abinda yafada taqi kallon fuskarsa dake sake sakar Mata zafi ahankali itama tace,
"Ku ajiye Ni Zan hau drp na qarasa.
Bakinta da yayi maganar ya kalla itama Jin baice komaiba yasata juyowa ta kalli fuskarsa idanuwansu suka hadu a fuske ta Dan janye nata Idon tana kokarin sake magan ya katseta da cewa,
"Meye wannan ajikinki nace??
Jikin nata ta kalla a sace taga gyalenta yake kalla dan Haka saita qi cewa komai.
Ahmed tuni ya kama hanyar gidan Karatu ganin baida niyar sake magana shima saita sake juyowa ta kallesa tana son magana Amma izzarta na hanata Dan Haka tai shiru tareda dauke kanta itama.
Babban gate din gidan Ahmed shige da motar bayan an wangale musu kofar gate din.
Danne zuciyarta tayi yaqi juyowa ta kallesa
Dan jiran takeyi ya fita motar Ahmed ya wuce da ita gida.
Ahmed na parking ya bude motar ya fice Dan Basu guri.
Fitar Ahmed yasata juyowa ta kalli gaban motar zatayi magana ya zuba Mata fararen idanuwansa takasa cewa komai cikin mamakin abinda ya tsaya jira a motar ta Dan kalli gefensa zatayi magana ya katseta ta hanyar bude motar ya fice ba tsammani taji ya bude ta gefenda take cikin kulawa.
Qin juyowa tayi ta kalli kofarma gabaki daya saita fiddo wayarta ta saka Kiran Ahmed Wanda daga shi har securities duka suka bace bat daga harabar gidan suka koma daga waje.
Wayar Ahmed na ringing ya daga ko magana baiyiba AQEEL ASAD ya saka hannuwansa masu tsayi ya karbe wayar daga hannunta cikin nutsuwa tareda sunkuyawa ya dauketa gabaki daya ya nufi ciki ita Yana kallon fuskarta dake bayyanarda fushi da bacin Rai me tsanani.
Bai ajiyeta koinaba sai tsakiyar master bedroom dinsa dake gidan
Yana ajiyeta ta fizge jikinta a zafafe ta nufi kofa ko Isa batayiba Yakuma dawo da ita ta baya
Duk yanda yake kaucewa haduwar jikinsa da nata saida suka hadu sosai ta bayanta ya matseta cikin jikinsa ahankali yana sauraron yanda take kokawar kwacewa.
Fuskarsa yakai wuyanta ya shaqi qamshi data tashi jikinta Mai sanyi na
Boadicea kafin yakai bakinsa kunnenta ahankali ya furta,
Menene wannan din Kika yafa??
Cak ta tsaya daga mutsu mutsun datakeyi sbd numfashin daya sakar Mata Mai zafi a kunne da wuyanta
Yasa zafi sauko Mata tako Ina..
Bai janye bakin nasa daga kunnentaba yasake cewa,
"Uhumm Ina jiranki??
Rintse Ido tayi ta bude qamshinsa da numfashinsa da jikinsa dayake zagaye da nata yasata Jin numfashinta Kamar Yana toshewa ahankali ta zare jikinta tareda matsawa gaba batareda ta bari ta juyoba.
Qarasowa yayi ya Kama hannunta ya dawo da ita kan lafiyayyar sofan sake dakin nasa ya zauna tareda kokarin zaunar da ita Amma ta kafe taqi zaunawar...
Tashi yayi tsaye gabanta kirjinsa na gap da gugar nata ta daga qafa zatayi baya yakai hannunsa ya yangota ahankali ta fado jikinsa ya riqeta da kyau ba tareda ya matsetaba Kamar Wanda bayason takura qashinta.
Haduwarsu hakan yasa numfashinta sake toshewa taqi yarda ta dago Dan batason kallon fuskarsa.
Idanuwansa ya zuba mata Yana Jin gyalen nata data fita dashi Yana yankar zuciyarsa Amma taurin kanta da kafiyarta ya hanata bude Baki tayi magana.
Wuyanta yake kalla zuwa fuskarta dataki kallonsa.
Hannunsa yakai ahankali zai taba gyalen nata tayi saurin dagowa suka hada ido.
Bazata iya jure kallonsa ba Dan Haka ta motsa zata qwace jikinta kirjinsu Yakuma Mannuwa Dana juna..
Ahankali ya janyeta daga jikin nasa da Kansa yana dauke kallonsa daga kanta.
Yana sakinta ta bude kofar bedroom din ta fice fuskarta na bayyanarda bacin Rai da fushi Amma zuciyarta bugawa takeyi da qarfi sbd tsoro da mamakin abinda ya faru din.
Mota ta nufa Kai tsaye ta Shiga ta zauna sai alokacin tasamu numfashinta yafara warwarewa.
Saida tayi mintina hudu a motar kafin ya fito a kame cikin nutsuwa kwarjininsa na qara bayyana Kamar bashine yayi abinda yayi aciki dinba.
Motar yanufa Kai tsaye yashiga daga ita harshi Babu Wanda ya kalli juna saidai qamshinsa datake ji maqale jikinta shima akwai nata qamshin daya mannewa kayansa.
Ahmed yakira a waya da sauri ya taho yashiga motar ya tada suka fice.
Kai tsaye gidan IDON NERA suka nufa akai Amal din kafin ya wuce gidansa Dan dawowarsa kenan daga airport yakira Ahmed din yazo ya daukesa malam Rabiu Kuma ya wuce Kai Al-Amin da gida.
****Haj Maryamah da umma suna Isa gidan IDON NERA Kai tsaye securities suka qi bude musu gate Saida suka sanar da Haj Zainab wadda tayi shiru da mamakin Jin su waye din.
Numfashi ta sauke kafin tace abari su shigo din
Daman tasan zaayi hakan
Sunma Dade Basu zo ba Dan Bata dauka zasuyi shiru har tsawon lokacinba.
Parking sukayi a harabar gidan
Bilkees ce ta tuqo su Kuma bada mufeeda sukazo ba yau din.
Itama haj Zainab tana kashe wayarta daga gate din ta miqe ta sauko kasa Dan Jin meya kawosu gidan Dan idanma akan auren AQEEL ne kofa zata nuna musu su can suyi dashi
Babu Wanda zai kasheta lokacinta baiyiba tana zaune lafiya cikin iyalinta.
Harta sauko Basu qaraso cikiba Dan Haka ta nufi kofa zata taresu tin acan harabar suyi acan saigashi sun shigo Bilkees ce agaba tana yiwa koina gidan kallon qazanta da qyama.
Haj Maryamah da umma ne a baya
wannan karon fuskokinsu Babu alamar sauki da gaske sukeson akawo karshen komai.
Batayi wahalar cewa su zaunaba da tasan ba zaman zsuyib ba Kai tsaye tace,
Lafiya dai inace ba???
Itama Haj Maryamah Bata tsaya batawa kanta lokaciba sbd ta gaji Kai tsaye tace,
"Kin shayar da AQEEL nononki nakeson ji daga bakinki.......
Wani kallo Haj Zainab ta dago tabi Haj Maryamah din dashi cikeda matsanancin mamakin dayafi na koyaushe,
Bata taba tunanin tsanar dasuke Mata takaisu ga rasa ilimin addinin dasuke dashiba.
Siddi data biyo mommyn tana bayanta ta fito bayanta itama cikeda mamaki tace,
"Nono kuma?
Kunsa me kuke fada kuwa?
Shayarda Shi na nufin aurensu ya haramta kenan fa??.....
Katseta Haj Maryamah tayi cikin fushi Mai tsanani da bacin Rai tace,
"Ki ringa tsayar da Yayanki inda Ina magana sbd tarbiyarsu daban take data yayan da muka sani,
Dake nake magana
Amsa Kuma nakeso idan ba hakanba kotu ce zatayimun maganin duk wani mummunan aikinki akan Dana tun Yana qanqaninsa.......
Cikin fushin dayafi na Haj Maryamah din Zainab ta katseta da cewa,
"Indai wannan shine halin yayan da kike magana akai to abarmin yayana ayanda suke din haka sbd jahilci da kaucewa Allah kawai nake hangowa a wannan rayuwar da kike fada..
Katseta itama umma tayi da cewa,
"Amsa aka tambaya ba rayuwar 'yayanki ba Zainab Idon Nera,
Kin shayar da AQEEL nononki ne Kuma sbd son abun duniya Kika Bari ya auri 'yarki da sukasha nono daya
Dan Haka auren ya haramta Babu Wani sauran Bata lokaci a warwaresa kawai.......
"Meyake faruwa Anan?" Sukaji anfada daga bayansu
Dukkaninsu suka juyo gabaki dayansu suna kallonsa.
Ganinsa tareda Amal wadda itama kallo daya tayi musu a ranta dayake baci da baqin cikin ganinsu tace,
"Meyasa duk haukan tsoffin Nan ya motsa anan suke zuwa su sauketa??¿
Bilkees da ganin AQEEL ASAD dinta da Amal din tare yasata sakin Baki zuciyarta na tsalle bakinta na neman bushewa sbd saninsu baya gari tsawon kwanakin to da ita yatafi kokuma Daman baiyi tafiyar bane Yana Nan ya tare???..
Cabdijam" suka fada dukkaninsu atare su ukun
Da Haj Maryamah da umma da Bilkees wadda tafara Jin zafi na shigota ta ko Ina.
Da mamakin ganinsu a gidan shima yasake maimaita tambayarsa fuskarsa akan mahaifiyarsa wadda take kallonsa cikin fushi.
A natse kamewarsa na tsananta ya sake kallonsu kafin ya kalli Mami wadda tagama girgiza da haukarsu ta wannan karon yace,
"Meyake faruwa Anan??....
Zuciyar Bilkees data gama konewa da baqin ciki da takaici babu shakka ko tauna zancen sbd gwara yaji yasan aurensa ya haramta da Amal
Tasan ba lallai sunsha nononba tunanin su umman ne kawai Amma gwara ace sunsha din auren ya watse kowa ya huta...
Kai tsaye tace,
"Maminka ta shayar dakai kana yaro Dan Haka aurenka da......
Wani irin kallon daya juya yayi matane yasa kalmomin bakinta watsewa suna gagara haduwa sbd duk abinda takeyi duk haukarka kallonsa daban ne..
Haj Maryamah dataga Bilkees din ta rude saita qarasa zancen da cewa,
"Aurenka ya haramta anan saika sakar Mata 'yarta....
Ita kanta Amal wani matsanancin mamaki tashiga Jin zancen gabanta yayi wani irin faduwa ta juya ahankali ta kalli mommynta wadda shima ita ya zubawa fararen idanuwansa dasuka sauya take yana jiran maganarta wadda kalma daya zata bude Baki tayi ya fahimci gaskiyar zancen.