Sashe 53
Idon Naira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mommy Dan Allah ki kwantar da hankalinki ki dawo daidai bamason ganinki hakan
Koma menene matsalar zata wuce zamu fuskanceta mu maganceta kaman yanda muka Saba tsayawa da juna,Amma Kuma mommy wace Amal din aka daurawa auren ayau??
Dago jajayen idanuwanta tayi ta kalli inda Amal ke tsaye tana jiran amsar da zataji tabawa Siddin.
Ahankali ta iya bude Baki murya a shaqe tace,
"Amal wannan da muke da ita guda daya gatanan.....
Kaman siddi batasan wacece Amal din ba ta waiwayo cikeda dinbin mamaki ta kalli Amal din zatayi magana Amal ta katseta da cewa,
"Aure fa kuke magana Mommy¿
As in aure aure irin na kowa da ake Masa???
Maida kallonta kan uncle Lulu tayi cikeda mamaki tana sake kasa gasgata abinda aka fada din tace,
"Uncle meyasa kayi magana Dan Allah Mana.
AQEEL ASAD daga inda yake Bai waiwayo ba ya nufi kofa hankalinsa kwance ya fice yabarsu sbd bayajin akwai sauran bayanin da Bata ganeba idanma Bata gane dinba zasu Mata bayanin dazaisa ta gane din.
Bayansa uncle Lulu yabi da kallo fuska a Dan yamutse da tunanin Yaya Kuma zai tafi ya barsu da bayani baya shine yayi Aika aikar gabaki daya.
Dawo da kallonsa yayi kan Amal Yana Dan Jin tausayin abinda zai fada Matan, cikeda kulawa da tausasa harshe yace,
"Baby Aurenki AQEEL ASAD yayi ayau,
Kudin aljihunsa ya cire tareda kamo hannunta zai Dora Mata ta zame tana kallonsa da idanuwanta dake cikowa da hawayen tashin hankali,mamaki da baqin ciki tareda firgita.
"Wannan shine sadakinki Amal" uncle Lulu yafada Yana kallon idanuwanta dake kokarin cika da hawayen baqin ciki da zafi zai tsanani,
"Sweetie kiyi hakuri....
Uncle aure fa kace?
Auren Dole kukai mun?
Kallon Mommy tayi sai kawai takasa cewa komai ta juya ta fice dakin da sbd zuciyarta harbawa takeyi da qarfi da ciwo..
Kai tsaye dakinta ta nufa tana kokarin rufewa mommynta ta tare kofar tareda shigowa idanuwanta cikeda rauni da tausayin 'yarta takasa magana sai rungumeta datayi Tana cewa,
"Kiyi hakuri Amal,
Bada niya ko cutatarwa akai Miki hakan ba Nima fin qarfina akai Akan hakan Amma ban taba tunanin yimiki auren Dole ba ko irin wannan na rashin tsammanin, I'm so sorry sweetie....
Kasa rike kukan dayake cin zuciyarta Amal tayi sbd duk yanda taso daurewa sbd takasa yarda da abinda suke fada din takasa daurewa, zuciyarta takasa riqewa Dan Haka ta saki wani irin silent kuka ajikin mommyn tana girgiza kai alamar bazata iyaba,bazata iya karban wannan abinda suke fada din ba.
Tausayintane yasake cika zuciyar mahaifiyarta ta sake rungumeta zuciya a karye tana cewa,
"Kiyi hakuri Amal Dina Zaki iya,
Zaki iya insha Allah,
Allah zai kawo mafita sbd Shi kadaine yasan dalilin hakan,
Shine ya qaddara hakan,
Please sweetie karkiyi irin wannan kukan Zaki sake karyamun zuciya.
Amal bazata iya magana ba sbd kuka takeyi sosai Wanda takeson abinda ya danne maqoshi da zuciyarta ya fada tukuna tasamu damar borewa wannan auren dasuke magana Dan bazata taba iyawaba,
Bazata Yi wannan aurenba dasuke magana,
Bazata taba son aurenba bare wainda suke cikin rayuwar auren,
AQEEL ASAD fa suke magana,
Mata ne dashi harda budurwar 'ya,
Mutuminda mahaifiyarsa tayiwa tata mahaifiyar tsanarda ko kafiri batawa irinta.
Kokarin tsayar da kukan dayaci qarfinta takeyi ta dago da idanuwanta dasukai jajir harma da fuskarta ta kalli mommyn muryarta a shaqe tace,
"Mommy wallahi bazan iyaba,
Kisaka ya sakeni batareda min wahalarda juna dukanmuba,
Bazan iyaba Mommy,
Wannan ba aure bane fitinace aka hada kawai,
Wlh bana sonsa ko kadan nidai ko kallonsa bazan iyayiba a matsayin mijina sbd ban taba fatan auren me mataba kinsani bare shi da mahaifiyarsa bazata taba karbanaba kaman yanda bazan karba dantaba.
Mommy kisa ya sakeni banason auren indai dashine..
Rintse idanuwa Haj Zainab tayi tana girgiza kai ahankali murya a sanyaye tace,
"Kiyi hakuri Amal bazan iyaba,
AQEEL nada iko fiyeda yanda kike tunani akanki,
AQEEL shine Wanda ya daukeki a duniya ya rada Miki asalin sunanki,.shine Wanda yakesonki fiyeda yanda kowa yakesonki a duniya bayan Ni Dana haifeki,
Bazan iya tirsasaba sbd yayi iko akanki,
Ya zartar da wannan hukuncin ne sbd ya tabbatarda Babu Wanda zai iya yin hakan akanki bayan shi,
I'm sorry my princess Amma Nima duk yanda nake qin wannan auren nasan bazan sauya komaiba tunda yariga ya rataya Miki igiyoyin aurensa akanki.
Hakuri zakiyi mu rungumi wannan sabuwar qaddarar muga inda zata kaimu tukuna kafin Allah yakawo Mana mafitarta..
Sake fashewa da wani sabon kuka Mai tsananin qona Rai da zafin zuci datake Jin kamar zuciyarta zata Kama da wuta.
Kallonta Haj Zainab takeyi idanuwanta na kokarin tsayar da nata hawayen ta sake kamota zatayi magana AMAL din ta girgiza kai ahankali tana kokarin tsayar da nata hawayen itama tace,
"Mommy bazaki iya Bata Masa ba ko quntata Masa shiyasa bazaki iya cewa ya sakar Miki 'yarkiba??
Wane matsayi ne yakedashi Acikin zuciyarki Wanda yafi na ni 'yarki da Kika Haifa,
Shi din fa 'dan maqiyanki ne wainda Basu taba sonki ba bare kaunarki....
Cikin tsawa da Hana bayyanarda zafin maganar tata ta katseta da cewa,
"Shut up Amal,
Hankalinki zai Bata ne sbd auren Dole yafara akanki ne?
Bakece farkoba bakuma Zaki zama qarsheba,
AQEEL ya aureki ne sbd ya Isa dake,
Koni dana haifekin bazan iya hanasa ba bare ke da aka Haifa din,
Idan inada ikon warware auren zakima San anyi ne?da tun lokacinda aka daura Zan sa a warware din,
Karki Bari bacin rai yasa Naga laifinki sweetie kiyi hakuri nasan tako Ina Babu inda aka kyauta Miki Amma AQEEL nada matsayi da girma a rayuwata da zuciyata da ba ke ba koni ya aurar wa wani bazan iya bijirewa duk tsanata kuwa da abin bare ke,
Nace Miki komai zai daidaita
Zan samo Mana mafita Akan lamarin Amma ba irin wannan da kike tunani ba...
Sassauta muryarta tayi cikin sanyi da kulawa tareda kauna da soyayyar 'yarta tana kallon yanda Amal din ke kallonta kamar yau tafara ganinta cikeda mamaki da tsoron irin kaunar AQEEL ASAD Mai tsananin girma datake hangowa Acikin idanuwa da kalaman mahaifiyarta,
Wace irin kaunace wannan Mai tattareda mamaki da tsoro da baqin ciki tareda kishi take ganin mahaifiyarta nawa 'dan matarda tasan a duniya tafi kaunar masifa da hasara akan Zainab din.
Kasa cewa komai tayi sbd sanyi da jikinta yayi na ganin abinda yake neman shallake tunaninta,
Ahankali ta saka bayan hannunta ta share hawayenta dake gudu sun kasa tsayawa ta bude Baki a hankali tace,
"Mommy meyasa kike sonsa da yawa Haka?
Rufe Ido tayi ta bude tareda miqewa ta nufi kofa ta fice sbd tasan Amal bazata taba yarda da komaiba cikin sauki bare su nutsu su samo ganin inda hanyar bullewa take garesu da wannan auren Kamar yanda tasan mutuwarta dolece tasan umma da umman AQEEL din Koda zasu rasa lafiyarsu bazasu yarda da wannan aurenba bare har ayi tinanin mafita a natse,
Masiface kwance a qasa tasani,
Zasu tashi tsaye da kyau su tabbatarda wannan auren Bai 'daga daga inda yakeba,
Koda zasu rasa komai bazasu taba karban 'yarta amatsayin matar AQEEL ASAD ba,
They can go to Any length to Make sure Amal Idon Nera tabar rayuwar AQEEL ASAD a wulaqance Wanda itama Koda zata rasa komai da kowa bazata yarda su lalata rayuwar 'yarta ba kamar yanda suka tabbatarda tata tagama lalacewa tako wane bangare har Saida taqare a titi gidan karuwai Acikin karuwai da prison cikin masu manyan laifukanda ko labari Bata taba ji ba,
Idan har bazai warware aurenba to itama bazata yarda 'yarta tabar gabanta ba taje koinaba sai taga yanda iyayensa suka tarba auren tukuna,
Saita Gama ganin kalar haukar data shigesu akan auren sbd suna taba Mata yarinya wannan karon rigimar da ake neman magancewarce zata Gama girmama ta zama wani abin Kuma,
Ita Bata da damuwar duk yanda duniya zataji sunanta ya lalace sbd Daman qaurin sunan ne da ita
AQEEL ASAD din kawai takeji kada duniyarsa takoma abar bugawa a jarida Koda yaushe Amma tunda kusan hakan kowa ya zaba bazata quntata rayuwarta ta quntata ta 'yartaba
Aure dai an daura to zata zuba Ido taga abinda zai biyo baya daga garesu.
Ficewa tai dakin tabar Amal wadda itama kukanta ya tsaya sbd abinda ya tsaya ya danne Mata zuciya akan yanda mommyn ta zabi kasa baqanta ran AQEEL ASAD akan nata,
Bazata sake maganar komai Akan aurenba tunda batama yarda da aurenba Dan Haka suda suka daura Saji da maganar Amma Babu Wani aure da zata dorawa kanta.
Bayan fitar mommyn kasa taurin ran tayi wani sabon kukan ya yunquro Mata ahankali sbd anrigda anyi Mata wata irin cuta da illa a rayuwa Koda an warware sbd har abadanta AQEEL ASAD shine Wanda akasan yafara aurenta.
Kuka takeyi ahankali jikinta koina Yana daukan zafi da mutuwar jikin.
Mommy na fita Kai tsaye Palo ta sama uncle Lulu daketa amsa wayoyin Taya murna Babu qaqqautawa daga mutanenda duk sai daga baya suke samun labarin daurin auren Wanda Babu Wanda ya taba Tunanin zasu iya samun Saar mutum irin AQEEL ASAD ba ya shigo cikin ahalinsu ya zama sirikinsu ba sbd Shi din dasu Kamar doya da manja ne rayuwarsu tayi hannun Riga data juna nesa ba kusaba.
Wasu kuwa Kiran dasukeyi Dan tabbatarda labaran ne cewan Dagaske AQEEL ASAD ne yayi nasarar aure Amal Idon NERAr dasukaita burin auraba Dan cike burinsu na mallakarta ta zama tasu sbd son da kusan duk suke Mata da shaawar aurenta.
##MAMUH#
#LOVE/ROMANCE/MARRIAGE
#SISTERSLIFE
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
41
SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!
Koma menene matsalar zata wuce zamu fuskanceta mu maganceta kaman yanda muka Saba tsayawa da juna,Amma Kuma mommy wace Amal din aka daurawa auren ayau??
Dago jajayen idanuwanta tayi ta kalli inda Amal ke tsaye tana jiran amsar da zataji tabawa Siddin.
Ahankali ta iya bude Baki murya a shaqe tace,
"Amal wannan da muke da ita guda daya gatanan.....
Kaman siddi batasan wacece Amal din ba ta waiwayo cikeda dinbin mamaki ta kalli Amal din zatayi magana Amal ta katseta da cewa,
"Aure fa kuke magana Mommy¿
As in aure aure irin na kowa da ake Masa???
Maida kallonta kan uncle Lulu tayi cikeda mamaki tana sake kasa gasgata abinda aka fada din tace,
"Uncle meyasa kayi magana Dan Allah Mana.
AQEEL ASAD daga inda yake Bai waiwayo ba ya nufi kofa hankalinsa kwance ya fice yabarsu sbd bayajin akwai sauran bayanin da Bata ganeba idanma Bata gane dinba zasu Mata bayanin dazaisa ta gane din.
Bayansa uncle Lulu yabi da kallo fuska a Dan yamutse da tunanin Yaya Kuma zai tafi ya barsu da bayani baya shine yayi Aika aikar gabaki daya.
Dawo da kallonsa yayi kan Amal Yana Dan Jin tausayin abinda zai fada Matan, cikeda kulawa da tausasa harshe yace,
"Baby Aurenki AQEEL ASAD yayi ayau,
Kudin aljihunsa ya cire tareda kamo hannunta zai Dora Mata ta zame tana kallonsa da idanuwanta dake cikowa da hawayen tashin hankali,mamaki da baqin ciki tareda firgita.
"Wannan shine sadakinki Amal" uncle Lulu yafada Yana kallon idanuwanta dake kokarin cika da hawayen baqin ciki da zafi zai tsanani,
"Sweetie kiyi hakuri....
Uncle aure fa kace?
Auren Dole kukai mun?
Kallon Mommy tayi sai kawai takasa cewa komai ta juya ta fice dakin da sbd zuciyarta harbawa takeyi da qarfi da ciwo..
Kai tsaye dakinta ta nufa tana kokarin rufewa mommynta ta tare kofar tareda shigowa idanuwanta cikeda rauni da tausayin 'yarta takasa magana sai rungumeta datayi Tana cewa,
"Kiyi hakuri Amal,
Bada niya ko cutatarwa akai Miki hakan ba Nima fin qarfina akai Akan hakan Amma ban taba tunanin yimiki auren Dole ba ko irin wannan na rashin tsammanin, I'm so sorry sweetie....
Kasa rike kukan dayake cin zuciyarta Amal tayi sbd duk yanda taso daurewa sbd takasa yarda da abinda suke fada din takasa daurewa, zuciyarta takasa riqewa Dan Haka ta saki wani irin silent kuka ajikin mommyn tana girgiza kai alamar bazata iyaba,bazata iya karban wannan abinda suke fada din ba.
Tausayintane yasake cika zuciyar mahaifiyarta ta sake rungumeta zuciya a karye tana cewa,
"Kiyi hakuri Amal Dina Zaki iya,
Zaki iya insha Allah,
Allah zai kawo mafita sbd Shi kadaine yasan dalilin hakan,
Shine ya qaddara hakan,
Please sweetie karkiyi irin wannan kukan Zaki sake karyamun zuciya.
Amal bazata iya magana ba sbd kuka takeyi sosai Wanda takeson abinda ya danne maqoshi da zuciyarta ya fada tukuna tasamu damar borewa wannan auren dasuke magana Dan bazata taba iyawaba,
Bazata Yi wannan aurenba dasuke magana,
Bazata taba son aurenba bare wainda suke cikin rayuwar auren,
AQEEL ASAD fa suke magana,
Mata ne dashi harda budurwar 'ya,
Mutuminda mahaifiyarsa tayiwa tata mahaifiyar tsanarda ko kafiri batawa irinta.
Kokarin tsayar da kukan dayaci qarfinta takeyi ta dago da idanuwanta dasukai jajir harma da fuskarta ta kalli mommyn muryarta a shaqe tace,
"Mommy wallahi bazan iyaba,
Kisaka ya sakeni batareda min wahalarda juna dukanmuba,
Bazan iyaba Mommy,
Wannan ba aure bane fitinace aka hada kawai,
Wlh bana sonsa ko kadan nidai ko kallonsa bazan iyayiba a matsayin mijina sbd ban taba fatan auren me mataba kinsani bare shi da mahaifiyarsa bazata taba karbanaba kaman yanda bazan karba dantaba.
Mommy kisa ya sakeni banason auren indai dashine..
Rintse idanuwa Haj Zainab tayi tana girgiza kai ahankali murya a sanyaye tace,
"Kiyi hakuri Amal bazan iyaba,
AQEEL nada iko fiyeda yanda kike tunani akanki,
AQEEL shine Wanda ya daukeki a duniya ya rada Miki asalin sunanki,.shine Wanda yakesonki fiyeda yanda kowa yakesonki a duniya bayan Ni Dana haifeki,
Bazan iya tirsasaba sbd yayi iko akanki,
Ya zartar da wannan hukuncin ne sbd ya tabbatarda Babu Wanda zai iya yin hakan akanki bayan shi,
I'm sorry my princess Amma Nima duk yanda nake qin wannan auren nasan bazan sauya komaiba tunda yariga ya rataya Miki igiyoyin aurensa akanki.
Hakuri zakiyi mu rungumi wannan sabuwar qaddarar muga inda zata kaimu tukuna kafin Allah yakawo Mana mafitarta..
Sake fashewa da wani sabon kuka Mai tsananin qona Rai da zafin zuci datake Jin kamar zuciyarta zata Kama da wuta.
Kallonta Haj Zainab takeyi idanuwanta na kokarin tsayar da nata hawayen ta sake kamota zatayi magana AMAL din ta girgiza kai ahankali tana kokarin tsayar da nata hawayen itama tace,
"Mommy bazaki iya Bata Masa ba ko quntata Masa shiyasa bazaki iya cewa ya sakar Miki 'yarkiba??
Wane matsayi ne yakedashi Acikin zuciyarki Wanda yafi na ni 'yarki da Kika Haifa,
Shi din fa 'dan maqiyanki ne wainda Basu taba sonki ba bare kaunarki....
Cikin tsawa da Hana bayyanarda zafin maganar tata ta katseta da cewa,
"Shut up Amal,
Hankalinki zai Bata ne sbd auren Dole yafara akanki ne?
Bakece farkoba bakuma Zaki zama qarsheba,
AQEEL ya aureki ne sbd ya Isa dake,
Koni dana haifekin bazan iya hanasa ba bare ke da aka Haifa din,
Idan inada ikon warware auren zakima San anyi ne?da tun lokacinda aka daura Zan sa a warware din,
Karki Bari bacin rai yasa Naga laifinki sweetie kiyi hakuri nasan tako Ina Babu inda aka kyauta Miki Amma AQEEL nada matsayi da girma a rayuwata da zuciyata da ba ke ba koni ya aurar wa wani bazan iya bijirewa duk tsanata kuwa da abin bare ke,
Nace Miki komai zai daidaita
Zan samo Mana mafita Akan lamarin Amma ba irin wannan da kike tunani ba...
Sassauta muryarta tayi cikin sanyi da kulawa tareda kauna da soyayyar 'yarta tana kallon yanda Amal din ke kallonta kamar yau tafara ganinta cikeda mamaki da tsoron irin kaunar AQEEL ASAD Mai tsananin girma datake hangowa Acikin idanuwa da kalaman mahaifiyarta,
Wace irin kaunace wannan Mai tattareda mamaki da tsoro da baqin ciki tareda kishi take ganin mahaifiyarta nawa 'dan matarda tasan a duniya tafi kaunar masifa da hasara akan Zainab din.
Kasa cewa komai tayi sbd sanyi da jikinta yayi na ganin abinda yake neman shallake tunaninta,
Ahankali ta saka bayan hannunta ta share hawayenta dake gudu sun kasa tsayawa ta bude Baki a hankali tace,
"Mommy meyasa kike sonsa da yawa Haka?
Rufe Ido tayi ta bude tareda miqewa ta nufi kofa ta fice sbd tasan Amal bazata taba yarda da komaiba cikin sauki bare su nutsu su samo ganin inda hanyar bullewa take garesu da wannan auren Kamar yanda tasan mutuwarta dolece tasan umma da umman AQEEL din Koda zasu rasa lafiyarsu bazasu yarda da wannan aurenba bare har ayi tinanin mafita a natse,
Masiface kwance a qasa tasani,
Zasu tashi tsaye da kyau su tabbatarda wannan auren Bai 'daga daga inda yakeba,
Koda zasu rasa komai bazasu taba karban 'yarta amatsayin matar AQEEL ASAD ba,
They can go to Any length to Make sure Amal Idon Nera tabar rayuwar AQEEL ASAD a wulaqance Wanda itama Koda zata rasa komai da kowa bazata yarda su lalata rayuwar 'yarta ba kamar yanda suka tabbatarda tata tagama lalacewa tako wane bangare har Saida taqare a titi gidan karuwai Acikin karuwai da prison cikin masu manyan laifukanda ko labari Bata taba ji ba,
Idan har bazai warware aurenba to itama bazata yarda 'yarta tabar gabanta ba taje koinaba sai taga yanda iyayensa suka tarba auren tukuna,
Saita Gama ganin kalar haukar data shigesu akan auren sbd suna taba Mata yarinya wannan karon rigimar da ake neman magancewarce zata Gama girmama ta zama wani abin Kuma,
Ita Bata da damuwar duk yanda duniya zataji sunanta ya lalace sbd Daman qaurin sunan ne da ita
AQEEL ASAD din kawai takeji kada duniyarsa takoma abar bugawa a jarida Koda yaushe Amma tunda kusan hakan kowa ya zaba bazata quntata rayuwarta ta quntata ta 'yartaba
Aure dai an daura to zata zuba Ido taga abinda zai biyo baya daga garesu.
Ficewa tai dakin tabar Amal wadda itama kukanta ya tsaya sbd abinda ya tsaya ya danne Mata zuciya akan yanda mommyn ta zabi kasa baqanta ran AQEEL ASAD akan nata,
Bazata sake maganar komai Akan aurenba tunda batama yarda da aurenba Dan Haka suda suka daura Saji da maganar Amma Babu Wani aure da zata dorawa kanta.
Bayan fitar mommyn kasa taurin ran tayi wani sabon kukan ya yunquro Mata ahankali sbd anrigda anyi Mata wata irin cuta da illa a rayuwa Koda an warware sbd har abadanta AQEEL ASAD shine Wanda akasan yafara aurenta.
Kuka takeyi ahankali jikinta koina Yana daukan zafi da mutuwar jikin.
Mommy na fita Kai tsaye Palo ta sama uncle Lulu daketa amsa wayoyin Taya murna Babu qaqqautawa daga mutanenda duk sai daga baya suke samun labarin daurin auren Wanda Babu Wanda ya taba Tunanin zasu iya samun Saar mutum irin AQEEL ASAD ba ya shigo cikin ahalinsu ya zama sirikinsu ba sbd Shi din dasu Kamar doya da manja ne rayuwarsu tayi hannun Riga data juna nesa ba kusaba.
Wasu kuwa Kiran dasukeyi Dan tabbatarda labaran ne cewan Dagaske AQEEL ASAD ne yayi nasarar aure Amal Idon NERAr dasukaita burin auraba Dan cike burinsu na mallakarta ta zama tasu sbd son da kusan duk suke Mata da shaawar aurenta.
##MAMUH#
#LOVE/ROMANCE/MARRIAGE
#SISTERSLIFE
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
41
SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!