Sashe 13
Idon Naira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Malam Sanda yasa Aqeel matashi ne Mai nutsuwa da hangen nesa tareda tunani na masu ilimi Dan haka baiyi wani dogon Jan lokaciba yace idan Zainab din ta Aminta da aurensa shikenan Allah yabasu hakuri da zaman lafiya.
Take ya sanar masa ta Aminta Dan haka a washe gari ya karbi sadakin Maminsa a hannun baba Malam Sanda ya shigo dasu sai alokacin ya tunkari Haj maryamah da zancen sbd kamar aikin Gama ya riga ya Gama
Dan Idan ba Hakan yayiba tun farko ya tunkareta bazata aminceba da wuri zatai watsi da zancen.
Malam Sanda kuwa da baisan cewar Zainab din qanwar Haj maryamah bace baiyi tunanin Zainab nada dangiba Dan kuwa Dama kusan kowa sanin marainiya Mai Aiki ake Mata wadda aka dauko tun Tana yarinya har girman yanzu shiyasa ma ya amince da auren Dan shima ya bada tasa gudunmawar gurin inganta rayuwarta.
***
Tsit palon Haj maryamah ya dauka sbd wutar da itama ta Dan dauke ta wucin gadi,
Kudin sadakin Zainab da Aqeel din yake nuna Mata take kallon agabanta zuciyarta na neman toshewa da rashin iska na zallan mamaki da firgici.
Maida kallonta tayi kan Aqeel ahankali Tana nazarin yanda yariga yayi nisa aduk wani lamarin daya shafi Zainab baya shakkar kowa bare tsoron bacin ranta.
Daqyar ta iya bude bakinta tace"
Zainab tasan ta zancen??
"Tasani Amma nine na tilasa Mata amincewar......
Sbd Kaine ka haifeta ko?
To meye amfanin samuna da zancen yanzu Bayan kun riga kunyi shawara har Kai ubanta ka karba sadakinta.
Dan rintse idanuwa yayi ahankali Yana sauke Kai daga kallonta Dan a kala manta Yana iya jiyo tsananin fushinta da bacin ranta.
Kasa cewa komai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta tabarsa a palon sbd wani tiriri da zafi zuciyarta ta dauka.
Sosai taji zuciyarta tayi zafi da Zainab,
Tafara gajiya da yanda take baa matsayin kowaba agurin Dan data dauka cikinsa ta haifa akan Zainab,
Ya maidata kwata kwata a Bayan Zainab,
Zainab itace first priority dinsa kafin ita,
To meye amfanin Zainab a rayuwarsa da zata fi Masa uwar data haifesa.
Sbd yanda ranta yayi tsananin baci daga shi har Zainab Babu Wanda takuma magana dashi ta dauki fushi Sosai.
Zainab kuwa batasan meyake faruwa ba Dan batamasan cewa harya karba sadakinba.
A bangaren Aqeel kuwa ganin yanda Haj maryamah tadauki zafi matuqa akan zancen yasashi sanarda Baba malam Sanda a daura auren zuwa jumaa Tunda saura kwana biyar juma'ar tayi.
Sai alokacin ya sanarda Mamin tasa yakuma Bata sadakinta a hannunta.
Shiru tayi tsawon mintuna tareda shiga tunani kafin ta tambayasa Haj maryamah Bata kirata tayi Mata maganar ba Bayan Dole saida izininsu da saka hannunsu zaayi duk wani lamarin.
Haka ya share zancenta Dan yasan Maminsa bazata amincewa aurenba kamar yanda yasan bazata taba aurar da ita dinba
Shikuwa bazai iya barin rayuwarta ta qare a Hakan ba tinda ba baiwarsu bace itama uwarsa ce,
Idan a baya batada gata ayanzu daya San Kansa shine zai zama gatanta daga Nan har lokacinda zai bar duniya inshallah.
Hankalin Haj maryamah bai Gama tashina da tsananin bacin rai saida Malam Sanda da Kansa yayi magana da ita ya sanar Mata yanda sukai da Aqeel tareda Bata tabbacin jumaa zaa daura auren.
Kudi ya fidda ya ajiye Mata daidai qarfinsa akan asiyawa Zainab din sitira.
Haj maryamah harsuka Gama magana ya tafi batasan haqiqanin me take cewaba Dan kuwa Aqeel yagama kasheta da mamaki wato har dangin mahaifinsa yasa malam Sanda yayi magana dasu akan auren Zainab din acan akai neman aure na manya aka sake bawa Aqeel qwarin gwiwar wannan aikin alkhairin daya hada tareda saka Masa albarka.
Kasa danne tsananin bacin ranta tai Dan bazata iyaba,
Duk wani rashin mahimmancinta ga danta ya nunawa duniya Tunda ya yanke wanan hukuncin shi kadai ya zartar.
Umma takira Tana hawayen qunci ta sanar Mata komai Tana jaddada laifin akan Zainab da zata iya yarda da buqatar Aqeel ta aure batareda saninsu ba.
Ita kanta umma mamaki Mai girma tashiga Jin Zainab dince zatai aure bada saninsuba,
Kenan duk kokarin dasukeyi akanta Bata ganiba shine ta zabi 'dan da aka Haifa a gabanta ya aurar da ita ga tafaffen malaminsa da baa San asalinsaba,baasan danginsaba baida kowa.
Wannan karon ummar da kanta ta Kira Zainab tayi Mata fadanda Bata taba yimata irinsaba...
Sai alokacin Zainab tasan da basusan da zancenba ashe
Hankalinta tashi yayi da fadan umma Dan kuwa maganganu marasa dadi da raunana zuciya ta fada Mata Wanda yasata kuka sosai.
Haj maryamah ta nufa dan Bata hakuri akan lamarin Amma Kuma bacin ran Haj maryamah din yafi na Umma Dan kuwa Kai tsaye ko wannan karon tabata zabi akan idan hartayi auren Wanda baasan asalinsaba Babu ruwansu da ita sun rabu kenan har abada.
Hankalin Zainab ya tashi Dan haka Bata tsaya shawara ko tunaniba tace ta hakura da auren ta fasa.
Hakan ya daki ran Aqeel sosai tareda Jin bacin rai da kunyar halayen mahaifiyarsa...
Daga umma har Haj maryamah Babu Wanda yayiwa Zainab sassaucin bayyanarda bacin ransa Dan haka tashiga wani mummanan Hali na damuwa da qunci tareda 'dacin zuciya Mai tsanani.
Halinda tashiga yasa Aqeel akaro na farko tsayawa da raayinsa akan na ummansa da ummarta.
Dukkanin harkar tafiyarsa karatu ya sokesu da Kansa tareda sanarda mahaifiyarsa ya fasa tafiya koina.
Babbar sabuwar rigima lamarin ya koma Wanda ya haddasa bacin rayuka tareda koke kokenda yawanci Zainab ce tafi Yi Dan ita aka yabawa laifin wannan karon har dangin mahaifin Aqeel din ita suka dorawa aka ringa tofa Mata maganganun gori marasa dadi.
Karshe dai da rigima taqi qarewa har saida umma tazo da nata bacin ran hakama haj Maryamah har gadon asibiti sbd jininta daya hau sosai Dan kuwa tashin hankalin da bacin ran Aqeel babu wanda bai ganiba qarshe dai kusan Zainab din yakeda niyar zaba akan kowa Dan haka tashin hankalin Zainab da baqin jininta saiya qaru.
Dangin mahaifin Aqeel dinma sai suka maida zancen Kuma akan Haj maryamah suna sukar tarbiyarta da wadda tabawa Aqeel din tako Ina duk sai komai ya qara lalacewa.
A ranarda taga yanda Haj maryamah ke zubda hawaye akan Aqeel zai jikinta yayi sanyi Dan kuwa tasan zubar hawayen uwa ga danta fitinace garesa Dan haka ta yanke shawarar dakatar da duka tashin hankalin dayake gudana....Dan haka ta amince da auren Malam Sanda tabar gidan har abada kamar yanda Haj maryamah tace..
Amincewarta zata sakata nesa da Aqeel Wanda Hakan zai basa damar jituwa da shakuwar kauna da mahaifiyarsa dake ganin itace ta zama sanadin da Babu kauna Mai tsanani tsakaninta da danta.
##MAMUH#
#DR SHAYKH AQEEL ASAD
#AMAL IDON NERA
#LOVE/ROMANCE
#LIFE#SISTERS
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
10
Daga umma har haj Maryamah da Aqeel din Kansa Babu Wanda bai girgixa matuqaba da matakinda Zainab din ta daukaba a Karo na farko a rayuwart datai ikon kanta.
Kasa gasgatawa umma da haj Maryamah sukai farko
sbd Babu Wanda acikinsu yayi tunanin zata iya bude baki ma tayi wata maganar Bayan ban hakuri dazataitayi.
Umma cikeda mamakinta tace,
" Zainab kin fahimci abinda ake nufi ne da zakiyi gaban kanki da ikon kanki?
Magana fa ake akan Aqeel da duka tarbiyarkice da kikai masa anan yake nunawa Babu Wanda ya Isa dashi sai ke
Haka kika nuna Masa ko Zainab?
Babu me mahimmanci agurinsa sai ke da kikai wahala dashi
Mu duk bama sonsa,
Uwarsa data haifesa ma bata Sansa saike Tunda kece kika haifesa
Gashi yanzu ana magana Zaki zaqe kice aurenki kika zaba zakiyi Bayan kin lalata alaqar uwa da 'danta Zaki tattara ki tafi ko????
Ni ban Isa ba akanki da bazaki tsaya kiji raayinaba a zancen auren idan na yarda idan ban yardaba kin zaba aurenki da kanki..
Daga qarshe dai gashinan duk Rikon amanar danai Miki kin nunamin ba nice na haifekiba.
Maganganun umma ba zuciyar Zainab kawai suke duka harda gangar jikinta datayi sanyi Tana daukar rawa da zafi sbd acikin bacin Rai da mamakin butulcin da ita ake ganin tayi ummar ke maganar,
Haj maryamah kuwa idanuwanta jajir suke sbd kukan datai na bacin Rai da Dana sanin barwa Zainab danta da Yana qarami.
Aqeel kuwa Kansa a qasa yake yanajin ciwo da radadin kalaman da ake fadawa Mamin Amma Kuma tarbiyarsa ba irin wadda zai iya musu ko sai'insa da manyansa bane,
Yasani komai zai fada bazasu bar Mamin da fada da maganganu marasa dadi ba
Yayi yayi sun kasa fahimtarsa saima laifi dayake qarawa Mamin idan Yana tsaya Mata Dan haka yayi shiru zuciyarsa data Mamin dake tsayayar hawaye da girmamata suna dukan zucuyarsu.
Zainab Bata iya ko motsawaba Bayan hawayenta dake gangarowa kan fuskarta,
A yanda zuciyarta da gangar jikinta sukai sanyi ta tabbatarda ta gaji,
Rauninta yayi yawa,
Batason fitina,
Batason koyaushe ta zama sanadin fadan Antynta da 'danta,
Har abada bazata taba son Aqeel dinta ya samu raunin karatun da su Haj maryamah din ke cewan shine ci gabansa,
Wannan sadaukarwar ta amincewa da auren ta zabi subarta har abada sbd Aqeel din tayita sbd matuqar Basu aminta da aurenba tasan kome zaayi bazai tafiba Dan shi din Dan kaifi daya ne,
Suma Kuma tasan bazasu taba amincewa da auren nataba sbd Babu Wanda zai iya yiwa Haj maryamah din bauta yanda takeso har abada kamarta....
Dan haka wannan hukuncin data zabarwa kanta shine mafita da maslahar ahalin gidan gabaki daya da hankalinsu ya tashi akan fashij tafiya karatun Aqeel din.
Sbd su Kansa dangin mahaifinsa a yanda suka dauki zafi da akace itace take zigasa Hakan
Sun bada tabbacin matuqar Aqeel bai tafi karatun ba zata bar gidan.
Tayi kukan da koyaushe aka tashi yiwa rayuwarta barazana sai ayi Mata barazanar Kora...
Take ya sanar masa ta Aminta Dan haka a washe gari ya karbi sadakin Maminsa a hannun baba Malam Sanda ya shigo dasu sai alokacin ya tunkari Haj maryamah da zancen sbd kamar aikin Gama ya riga ya Gama
Dan Idan ba Hakan yayiba tun farko ya tunkareta bazata aminceba da wuri zatai watsi da zancen.
Malam Sanda kuwa da baisan cewar Zainab din qanwar Haj maryamah bace baiyi tunanin Zainab nada dangiba Dan kuwa Dama kusan kowa sanin marainiya Mai Aiki ake Mata wadda aka dauko tun Tana yarinya har girman yanzu shiyasa ma ya amince da auren Dan shima ya bada tasa gudunmawar gurin inganta rayuwarta.
***
Tsit palon Haj maryamah ya dauka sbd wutar da itama ta Dan dauke ta wucin gadi,
Kudin sadakin Zainab da Aqeel din yake nuna Mata take kallon agabanta zuciyarta na neman toshewa da rashin iska na zallan mamaki da firgici.
Maida kallonta tayi kan Aqeel ahankali Tana nazarin yanda yariga yayi nisa aduk wani lamarin daya shafi Zainab baya shakkar kowa bare tsoron bacin ranta.
Daqyar ta iya bude bakinta tace"
Zainab tasan ta zancen??
"Tasani Amma nine na tilasa Mata amincewar......
Sbd Kaine ka haifeta ko?
To meye amfanin samuna da zancen yanzu Bayan kun riga kunyi shawara har Kai ubanta ka karba sadakinta.
Dan rintse idanuwa yayi ahankali Yana sauke Kai daga kallonta Dan a kala manta Yana iya jiyo tsananin fushinta da bacin ranta.
Kasa cewa komai tayi ta miqe ta shige bedroom dinta tabarsa a palon sbd wani tiriri da zafi zuciyarta ta dauka.
Sosai taji zuciyarta tayi zafi da Zainab,
Tafara gajiya da yanda take baa matsayin kowaba agurin Dan data dauka cikinsa ta haifa akan Zainab,
Ya maidata kwata kwata a Bayan Zainab,
Zainab itace first priority dinsa kafin ita,
To meye amfanin Zainab a rayuwarsa da zata fi Masa uwar data haifesa.
Sbd yanda ranta yayi tsananin baci daga shi har Zainab Babu Wanda takuma magana dashi ta dauki fushi Sosai.
Zainab kuwa batasan meyake faruwa ba Dan batamasan cewa harya karba sadakinba.
A bangaren Aqeel kuwa ganin yanda Haj maryamah tadauki zafi matuqa akan zancen yasashi sanarda Baba malam Sanda a daura auren zuwa jumaa Tunda saura kwana biyar juma'ar tayi.
Sai alokacin ya sanarda Mamin tasa yakuma Bata sadakinta a hannunta.
Shiru tayi tsawon mintuna tareda shiga tunani kafin ta tambayasa Haj maryamah Bata kirata tayi Mata maganar ba Bayan Dole saida izininsu da saka hannunsu zaayi duk wani lamarin.
Haka ya share zancenta Dan yasan Maminsa bazata amincewa aurenba kamar yanda yasan bazata taba aurar da ita dinba
Shikuwa bazai iya barin rayuwarta ta qare a Hakan ba tinda ba baiwarsu bace itama uwarsa ce,
Idan a baya batada gata ayanzu daya San Kansa shine zai zama gatanta daga Nan har lokacinda zai bar duniya inshallah.
Hankalin Haj maryamah bai Gama tashina da tsananin bacin rai saida Malam Sanda da Kansa yayi magana da ita ya sanar Mata yanda sukai da Aqeel tareda Bata tabbacin jumaa zaa daura auren.
Kudi ya fidda ya ajiye Mata daidai qarfinsa akan asiyawa Zainab din sitira.
Haj maryamah harsuka Gama magana ya tafi batasan haqiqanin me take cewaba Dan kuwa Aqeel yagama kasheta da mamaki wato har dangin mahaifinsa yasa malam Sanda yayi magana dasu akan auren Zainab din acan akai neman aure na manya aka sake bawa Aqeel qwarin gwiwar wannan aikin alkhairin daya hada tareda saka Masa albarka.
Kasa danne tsananin bacin ranta tai Dan bazata iyaba,
Duk wani rashin mahimmancinta ga danta ya nunawa duniya Tunda ya yanke wanan hukuncin shi kadai ya zartar.
Umma takira Tana hawayen qunci ta sanar Mata komai Tana jaddada laifin akan Zainab da zata iya yarda da buqatar Aqeel ta aure batareda saninsu ba.
Ita kanta umma mamaki Mai girma tashiga Jin Zainab dince zatai aure bada saninsuba,
Kenan duk kokarin dasukeyi akanta Bata ganiba shine ta zabi 'dan da aka Haifa a gabanta ya aurar da ita ga tafaffen malaminsa da baa San asalinsaba,baasan danginsaba baida kowa.
Wannan karon ummar da kanta ta Kira Zainab tayi Mata fadanda Bata taba yimata irinsaba...
Sai alokacin Zainab tasan da basusan da zancenba ashe
Hankalinta tashi yayi da fadan umma Dan kuwa maganganu marasa dadi da raunana zuciya ta fada Mata Wanda yasata kuka sosai.
Haj maryamah ta nufa dan Bata hakuri akan lamarin Amma Kuma bacin ran Haj maryamah din yafi na Umma Dan kuwa Kai tsaye ko wannan karon tabata zabi akan idan hartayi auren Wanda baasan asalinsaba Babu ruwansu da ita sun rabu kenan har abada.
Hankalin Zainab ya tashi Dan haka Bata tsaya shawara ko tunaniba tace ta hakura da auren ta fasa.
Hakan ya daki ran Aqeel sosai tareda Jin bacin rai da kunyar halayen mahaifiyarsa...
Daga umma har Haj maryamah Babu Wanda yayiwa Zainab sassaucin bayyanarda bacin ransa Dan haka tashiga wani mummanan Hali na damuwa da qunci tareda 'dacin zuciya Mai tsanani.
Halinda tashiga yasa Aqeel akaro na farko tsayawa da raayinsa akan na ummansa da ummarta.
Dukkanin harkar tafiyarsa karatu ya sokesu da Kansa tareda sanarda mahaifiyarsa ya fasa tafiya koina.
Babbar sabuwar rigima lamarin ya koma Wanda ya haddasa bacin rayuka tareda koke kokenda yawanci Zainab ce tafi Yi Dan ita aka yabawa laifin wannan karon har dangin mahaifin Aqeel din ita suka dorawa aka ringa tofa Mata maganganun gori marasa dadi.
Karshe dai da rigima taqi qarewa har saida umma tazo da nata bacin ran hakama haj Maryamah har gadon asibiti sbd jininta daya hau sosai Dan kuwa tashin hankalin da bacin ran Aqeel babu wanda bai ganiba qarshe dai kusan Zainab din yakeda niyar zaba akan kowa Dan haka tashin hankalin Zainab da baqin jininta saiya qaru.
Dangin mahaifin Aqeel dinma sai suka maida zancen Kuma akan Haj maryamah suna sukar tarbiyarta da wadda tabawa Aqeel din tako Ina duk sai komai ya qara lalacewa.
A ranarda taga yanda Haj maryamah ke zubda hawaye akan Aqeel zai jikinta yayi sanyi Dan kuwa tasan zubar hawayen uwa ga danta fitinace garesa Dan haka ta yanke shawarar dakatar da duka tashin hankalin dayake gudana....Dan haka ta amince da auren Malam Sanda tabar gidan har abada kamar yanda Haj maryamah tace..
Amincewarta zata sakata nesa da Aqeel Wanda Hakan zai basa damar jituwa da shakuwar kauna da mahaifiyarsa dake ganin itace ta zama sanadin da Babu kauna Mai tsanani tsakaninta da danta.
##MAMUH#
#DR SHAYKH AQEEL ASAD
#AMAL IDON NERA
#LOVE/ROMANCE
#LIFE#SISTERS
*_ZAFAFA BIYAR_*
*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano
*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul
*IDON NERA*🔥
Mamuhgee
*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma
*KI KULANI*🔥
Miss xoxo
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN
0022419171
Maryam sani
Access bank
Shedarka ta 09033181070
MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+22799643131
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
10
Daga umma har haj Maryamah da Aqeel din Kansa Babu Wanda bai girgixa matuqaba da matakinda Zainab din ta daukaba a Karo na farko a rayuwart datai ikon kanta.
Kasa gasgatawa umma da haj Maryamah sukai farko
sbd Babu Wanda acikinsu yayi tunanin zata iya bude baki ma tayi wata maganar Bayan ban hakuri dazataitayi.
Umma cikeda mamakinta tace,
" Zainab kin fahimci abinda ake nufi ne da zakiyi gaban kanki da ikon kanki?
Magana fa ake akan Aqeel da duka tarbiyarkice da kikai masa anan yake nunawa Babu Wanda ya Isa dashi sai ke
Haka kika nuna Masa ko Zainab?
Babu me mahimmanci agurinsa sai ke da kikai wahala dashi
Mu duk bama sonsa,
Uwarsa data haifesa ma bata Sansa saike Tunda kece kika haifesa
Gashi yanzu ana magana Zaki zaqe kice aurenki kika zaba zakiyi Bayan kin lalata alaqar uwa da 'danta Zaki tattara ki tafi ko????
Ni ban Isa ba akanki da bazaki tsaya kiji raayinaba a zancen auren idan na yarda idan ban yardaba kin zaba aurenki da kanki..
Daga qarshe dai gashinan duk Rikon amanar danai Miki kin nunamin ba nice na haifekiba.
Maganganun umma ba zuciyar Zainab kawai suke duka harda gangar jikinta datayi sanyi Tana daukar rawa da zafi sbd acikin bacin Rai da mamakin butulcin da ita ake ganin tayi ummar ke maganar,
Haj maryamah kuwa idanuwanta jajir suke sbd kukan datai na bacin Rai da Dana sanin barwa Zainab danta da Yana qarami.
Aqeel kuwa Kansa a qasa yake yanajin ciwo da radadin kalaman da ake fadawa Mamin Amma Kuma tarbiyarsa ba irin wadda zai iya musu ko sai'insa da manyansa bane,
Yasani komai zai fada bazasu bar Mamin da fada da maganganu marasa dadi ba
Yayi yayi sun kasa fahimtarsa saima laifi dayake qarawa Mamin idan Yana tsaya Mata Dan haka yayi shiru zuciyarsa data Mamin dake tsayayar hawaye da girmamata suna dukan zucuyarsu.
Zainab Bata iya ko motsawaba Bayan hawayenta dake gangarowa kan fuskarta,
A yanda zuciyarta da gangar jikinta sukai sanyi ta tabbatarda ta gaji,
Rauninta yayi yawa,
Batason fitina,
Batason koyaushe ta zama sanadin fadan Antynta da 'danta,
Har abada bazata taba son Aqeel dinta ya samu raunin karatun da su Haj maryamah din ke cewan shine ci gabansa,
Wannan sadaukarwar ta amincewa da auren ta zabi subarta har abada sbd Aqeel din tayita sbd matuqar Basu aminta da aurenba tasan kome zaayi bazai tafiba Dan shi din Dan kaifi daya ne,
Suma Kuma tasan bazasu taba amincewa da auren nataba sbd Babu Wanda zai iya yiwa Haj maryamah din bauta yanda takeso har abada kamarta....
Dan haka wannan hukuncin data zabarwa kanta shine mafita da maslahar ahalin gidan gabaki daya da hankalinsu ya tashi akan fashij tafiya karatun Aqeel din.
Sbd su Kansa dangin mahaifinsa a yanda suka dauki zafi da akace itace take zigasa Hakan
Sun bada tabbacin matuqar Aqeel bai tafi karatun ba zata bar gidan.
Tayi kukan da koyaushe aka tashi yiwa rayuwarta barazana sai ayi Mata barazanar Kora...