← Book details Idon Naira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 100

Sashe 39

Idon Naira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Motarsa na parking cikin harabar babban gidansa ya fito ya nufi sashen mahaifiyarsa Kai tsaye kaman yanda ya Saba duk ya dawo saiya fara zuwa ya gaidata yake Isa nasa sashen sbd ba lallai ta sake ganinsaba sai gobe Kuma Daman a wuni kafin ya fita yake zuwa su gaisa sai Kuma idan ya dawo.

Wayarsa ce tayi ringing Yana gap da Isa palon ummansa
Ya daga wayar cikin nutsuwa..,

"Sir I just forwarded you all the informations.

Kashe wayar yayi tareda bude sakon,

Hotonta yakeson gani kawai kafin sauran informations din..

Yana saka qafarsa ta dama a palon Haj Maryamah dake zaune ta zuba Masa ido tana jiran shigowarsa adaidai lokacin hoton Zainab ya bude fes akan screen din tsadaddiyar wayarsa..cak ya tsaya batareda ya qarasa saka qafarsa cikin palon ba.

Wayar ya zubawa fararen idanuwansa dasuka sauya atake,

Komai nasa tsayawa yayi cak idanuwansa suna qara sauyawa,

Kasa motsawa yai sbd gabobinsa da zuciyarsa da suka tsaya cak na wucin gadi...

Kallonsa Haj Maryamah takeyi cikeda mamaki tana ambatar sunanta ganin yanda yayi kamar Wanda yaga matacce yadawo duniya...

Bayajin komai bare yaji sunansa da umman ke Kira...

Miqewa tsaye tayi cikeda tsoron daya cika zuciyarta itama na ganinsa a wannan halin zuciyarta da jikinta na sanyi ta nufosa....

Bata qarasaba ya juya ya koma hanyar daya shigo ta fita idanuwansa na kadawa jajir..

Cak ta tsaya itama daga inda take batareda ta qarasa inda ya Bari dinba jikinta na wani irin sanyi zuciyarta na Shiga tsoro Haka kawai.

Jamilu driver na kokarin Isa gate gurin securities yana juyowa ya hango Mai gidan nasa tafe
da sauri ya juya ya Isa motar ya bude Masa Yana bude Baki zaiyi magana AQEEL ASAD ya katsesa Kai tsaye da cewa,

"Ikeja GRA right now..

Ok Shaykh.

Rufe kofar yayi ya zagaya da sauri ya shiga tareda tayarwa ba Bata lokaci da ribas ya fita gidan suka hau titi da wani irin gudu suka Kama hanyar ikeja GRA Kamar yanda Al-Amin ya turo Masa address din.

Hotonta ne yake yawo cikin Kansa da idanuwansa,

Rintse kyawawan idanuwansa dasukai jajir yai wani daci dake zuciyarsa Yana gauraya bakinsa tareda qafar da yawunsa dasukai daci.

Babu yanda Maminsa zata koma a duniya ya kasa ganeta,
Shekarun da sukai a rabe bazasu taba goge masa asalin kamannintaba dasuke Zane a zuciyarsa da rayuwarsa duk canji da sauyawar da zatayi.

****Haj Zainab kuwa suna baro gurin Kai tsaye gida suka nufa zuciyarta na sake daukan nauyi da wani irin 'daci data manta yanda yake a zuciya.

Lulu daya shiga damuwar halinda ta Shiga din ya kalleta Yana sake tambayarta ko zasu tafi asibitin ne.

Ahankali ta girgiza Masa Kai tana kokarin dawowa hayyacinta sbd ganin yanda ya damu saidai Amon muryar AQEEL ASAD ya daki zuciyarta mugun dukanda takasa daidaita kanta.

Suna Isa gida tayi bedroom dinta da sauri ta rufe kanta tana dafe zuciyarta dake zafi da radadi.

Siddi ce dake zaune palon ta miqe tabita tana Kiran sunanta cikeda so da kulawa tana cewa,

"Mommy are you ok??
Mommy meya sameki?
Mommy please meyake faruwa?
Bakida lafiya ne?

Kasa magana Haj Zainab tayi sai kokarin hana kanta shiga shock takeyi.

Amal ce tashigo dakin itama tana kallon mommyn sbd tana shigowa Bilkisu ta sanar da ita kamar mommyn ba lafiya taji siddi na daga murya.

Qarasowa tayi ta zauna gefen mommyn ta riqo hannayenta biyu tana kallon siddi tace,

"Meya sameta?
Mommyn menene?
Wani abin ya faru ne?

Rintse idanuwanta dasuka fara kokarin sauyawa tayi tana tunanin Meye hadinta dasu AQEEL din da zata damu Kuma?
Ai rayuwarta batada wani Hadi Koda amafarkine bare a zahiri,

'yayanta da 'dan uwanta Lulu sune kadai jininta Kuma abinda ya Kamata ta damu akansa...

Ta manta tayi alqawarin rufe babin rayuwar Zainab Yar malam adamu,
Yanzu Haj Zainab IDON NERA ce wannan.

Bude idanuwanta tayi tareda sauke numfashi Mai sanyi ta dafe goshinsa tareda kallon 'yayan nata dasuka daga hankalinsu gabaki daya.

Wani kyakkyawan murmushi tasaki tana kallon idanuwansu musamman AMAL datake jiran bayanin komai..

Zame hannunta tayi daga na AMAL ta shafa Fuskar Siddi da tafi AMAL rauni tace,

"Babyna ahakan Zaki zama uwar da muketa fata da burin ki zama
Kina komawa kamar baby daga Kinga mommynki cikin ciwo.

Dawo da kallonta tayi kan kyakkwar Fuskar AMAL mai daukan hankali tana murmushi tace,

"Am ok sweetie and everything is fine karki damu,

Wani case mukaje da uncle dinku suka Bata Mana Rai Amma ankai karshen matsalar komai yazama tarihi Babu abinda zai taba sauya Mana rayuwar farin cikinmu da kwanciyar hankalinmu.

Ajiyar zuciya suka sauke dukkaninsu Amal na cewa,

"I love you Mom.

Kallonsu tayi itama tana dariya tace,

"I love you both.

Uncle Lulu ne yashigo tareda Dr tayo daya Kira Dan yakasa nutsuwa da yanayin Zainab din.

Ganinsu ahakan yasashi sauke numfashin samun nutsuwa suka dawo palon dukkaninsu Dr tayo ya dubata yace jininta ne kawai ya Dan hau shima ba wani abin damuwa bane.

Dr tayo na tafiya AMAL ta miqe ta nufi bedroom dinta ta tube ta Shiga toilet.

Wanka tai ta fito ta Sanya doguwar Riga Mara hannu Kamar yanda ta Saba ire irensu ne kayan datafi sakawa idan tana gida.

Qaramar hula ce da Bata Gama rufe kanta ba a kanta sai slippers data saka ta fito taci abinci tana miqewa tsaye zata nufi sama inda su mommyn suke Bilkisu ta tareta da cewa,

"Anty AMAL Pelo yakira wai mommy tayi baqo.

Bata tsayaba tace,

Zan fada Mata.

Sama ta wuce ta tadda mommyn tana waya Mai mahummanci Dan Haka ta dawo qasan tace kice musu yajira tana waya.

AMAL na sake Hawa sama ko zama batayiba wayarta tayi ringing tana dagawa Bata Gama sauraron abinda ake fadaba tace,

"Waye AQEEL ASAD din?.....

Haj Zainab dake waya da sauri ta waiwayo gefen AMAL din tana cewa,

"Wake magana a wayar??

Kashe wayar Amal Tai tace,

"Daga gate ne Wai AQEEL ASAD na gidan Kuma gurinki yazo.

Itama Haj Zainab kashe tata wayar tayi batareda damuwa ko wani shock ba tace,

"Ina fama da ciwon kai inaga suce banajin Dadi bazan samu saukowaba.

Kai tsaye Amal din ta isar da sakon ta waya tareda fada musu karsu Kuma kiranta itama batason damuwa.
##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
29
Wayarta ta dauka taci gaba dayi duk da Rabin hankalinta na kan sunan baqon da akace yazo gurinta,

MUHAMMAD AQEEL ASAD Wanda tasani a baya kokuwa wani AQEEL ASAD din ne daban,

Koma wanne daga ciki batajin tanada himmar ganinsa ko magana dashi,
Kamar yanda alaqarsu ta yanke to hakama batada abinyi ko tattaunawa dashi.

Fincike zancen gabaki daya tayi a ranta tareda cigaba da wayarta hankali kwance harta Gama ta maido hankalinta kansu Amal suka cigaba da fira cikin Jin Dadi da kwanciyar hankali.

AQEEL ASAD dayake kofar babban gate din gidan hankalinsa yagama tashi ya fita nutsuwarsa gabaki daya

IDON NERA kawai yakeson gani a gabansa Dan da idonsa ya tabbatarda Maminsa ce IDON NERAr da ake fada,

Idon NERAr datayi mummunan suna a duniyar da bama zai iya fadaba,

Maminsa ce matarda akewa kirari da sunan da tambarin uwar karuwai?
Maminsa ce me aurarrakin da basa kirguwa.....

Ina Little MARYAMAH dinsa???

Su waye yayan nata biyu da ake fada?
Waye MARYAMAH din Baba sandan sa aciki??
Waye Mai aure aure acikinsu Kuma waye Hayat yakeso acikinsu???

Rintse idanuwansa yayi suna wani irin radadin Jan dasukai
Kansa juyawa yakeyi Yana Sara Masa tako Ina...

Wannan Idon Nera din kawai yakeson gani shi,
Ganinta kawai a gabansa zai tabbatar Masa da waye ita,Maminsa kokuwa wata daban¿

Baisan lokacinda suka daukaba a gurin suna jiran abasu damar shiga gidan kokuma ta fito din Amma Babu alamar ko daya,

Tun Rabiu driver na jiran fitowar sako daga ciki harya bude motar ya fito yabawa maigidan nasa guri sbd ganin mummunan yanayin dayake ciki,

Gurin securities na gate din Rabiu yazo ya sake magana tareda Yar magiyar asake isarda sakon zuwansu ga hajiyar..

Suna Kira Kai tsaye ta sanar dasu bazataga kowaba ayau din batajin Dadi.

Daqyar malam Rabiu ya dawo motar ganin har yamma tayi suna gurin ya shigo motar ya rufe tareda Dan waiwayowa kadan cikin girmamawa yace,

"Shaykh Ansake Kira Dan isar da zuwan naka
hajiya Idon Nera din batajin Dadi akace,
ko zaa kaika gida ka huta kafin asake dawowar???

Rintse idanuwansa yayi Yana Hana rauninsa bayyanuwa a fili ya gyada Kai Kawai sbd yasan malam Rabiu din Dole zai gashi duk da tsawon awannin dasukai agurin motars kunne take sbd AC dan bazai iya zama cikin zafi ba.

Hanyar gida suka nufa Yana Jin damuwarsa da tashin hankalin dake cikeda Ransa Yana qaruwa,

Meyasa taqi ganinsa,
Da gaske batada lafiya dinne?

Innalillahi wainna ilayhi rajiun,
Maminsa fa ake maganar shugaba Kuma uwa da gatan Karuwai....

Wannan wata babbar jarabtace da Allah yakewa imaninsa,

A rayuwarsa sunan karuwanci da Karuwai Bai taba Hawa harshensa bama bare ya taba ganinsu harma ace gashi ga su,

Idan ta tabbata Maminsa ce IDON NERAr datayi suna da shahara a wannan sunan dayake baqin ciki da Jin ciwon ambata Yaya zai iya kallonta,
Tayaya zai kalli MARYAMAH wadda yayi alqawarin inganta rayuwarta da zama gatanta tako Ina ya cike gurbin uba,Yaya,Kuma dangin uba agareta.

Har suka kusa Isa gida bai fita cikin tashin hankali da firgicin dayake cikiba,

Bazai iya Isa gidansa a yanayin dayake cikiba Dan Haka a hankali ya bude Baki cikin shaqaqqiyar murya yace akaisa gidan hutu da karatunsa.
Chapter 39 · 0% Book details