Sashe 9
Aaminat Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Abdulkareem
Kowa a Falon hira ya ke cikin nishaÉ—i amma banda shi, ya yi shiru ya na tunanin Aaminat rabonsa da ganinta tin ranar Bikin Bilkisu hakan ya sa duk ya shiga damuwa, abin da ya fi tashin hankalinsa ma rabuwar da su ka yi baram baram bai san a halin da ya jefata ba.
Abdulmajid ya ƙare masa kallo kafin ya ce "Kai tunanin me ka ke ne?? ba na son ɗorawa kai wahala, kai dai ba ka da wani haufi a rayuwa sai dai in kai ka jawowa kanka abin da zai sa ka tagumi." ya ɗan murmusa cikin son kauda zancen ya ce "Ba abin da ya dame ni, kawai jina nake kamar an yi min dukan tsiya, wai yaushe za mu je Abuja ne??" Abdussalam ya ce "Wallahi Ƙarya yake, ku tuhume shi, na lura kwanakin nan ba iya yau ba ma duk ya bi ya wani firgici, ku ce ya ɗaga rigarsa ku ga yadda ƙashin haƙarƙarinsa su ka fito, duk ya bi ya rarrame amma don kafiya idan ance akwai abin da ya dame shi sai ya ce aa." Ƙasa ya yi da kai don kuwa ba shi da ta cewa Zuciyarsa ta wani mugun karaya, yanzu kuwa ya ce musu Aaminat ya ke so ta dalilinta ya shiga wannan halin, Allah ne kaɗai ya san abin da zai faru, Abdurrahim ne ya katse masa tunanin da cewa "ka Sunkuyar da kai Hakan na nufin dai da gaske ka tsumbula kanka cikin Aradu." girgiza kai ya yi zai yi magana hawaye suka fara zuba sharrrr, ya yi saurin sunkuyar da kai ya na ƙoƙarin goge su. Abdussamad ya tashi ya dawo kusa da shi ya zauna, cikin lallami ya ce "Abdulkareem, ba ka da wasu tamkar mu Ƴan uwanka, mu ne dolenka, kar ka ɓoye mana abin da ke damunka ka faɗa mana." Ummi da ta ke binsu da ido sai a lokacin ta ce "Gaskiya ne Auta, ka faɗa ko da da temakon da zamu iya yi maka, don nima na lura abin har ya fara yawa musamman a cikin wannan Ƙadamin." Murmushi me tafi da hawaye ya yi kafin ya ce "Ba zan iya cewa ga abin da ya ke damuna ba, don Allah ku zuba min ido kawai Sabi da ba ku da abin da za ku magance min damuwata" kallon kallo su ka yi kafin Abdulmajid ya ce "Abin har ya yi tsauri ne haka?? Auta ko ba a haiyacinka kake ba? ka na tunanin duk cikinmu akwai abin da zai gagara mu yi maka??" Ya rausayar da kai kafin ya ce "Ba za ku taɓa Fahimta ba YaYa, ita fa rayuwa komai matsayinsa daban, wani abin da kuɗi ake sayensa wani kuwa ko da kaine mafi kuɗi a Duniya sai ya gagareka ba za ka iya saya ba, kuma a rayuwa ba za ka ce ko da yaushe sai dai ka yi farin ciki ba, akwai Launi kala-kala a Cikin rayuwa, hakan ya na daga cikin jarrabawar ɗan Adam, duk cikar ka da kaiwarka akwai abin da ka rasa kuma ka ke da burin samunsa, don Allah a rufe wannan maganar." dukkansu sakin bakuna su ka yi su na kallonsa cike da mamaki da kuma nazarin inda kalamansa su ka dosa sai dai sun kasa fahimta me yake nufi, Nana Kadija ta ce "Ya Audu ya na da gaskiya fa, a cikin kalamansa babu na banza, a rufe zancen kawai." goge hawayensa ya yi sannan ya dalla mata harara ya ce "Ban hana ki kirana Audun nan ba??" "To ai naga Sunanka ne" "Ki na buƙatar rasa haƙoranki ko??" ta yi farrr da ido ta ce "Ba zan rasa komai ba ai dai sunanka ne kuma ba zan dena faɗe ba." filo ya ɗauka ya wurga mata ta doka tsalle ta koma kusa da Ummi, ya yi ƙwafa kafin ya miƙe ya ce "Ni waje ma zan fita" Abdussamad ya ce "Sai ka dawo!" tin da ya fita magana sai ɗaiɗai a Falon sakamakon da da suka cika shi da surutu, kowa nazarin kalaman Abdulkareem ya ke har Ita Kanta Ummi, abin da su ke ta tambayar kansu shine menene ya sa shi faɗen hakan?
Tin daga ranar da Fati ta faɗi cewa Abdulkareem ya kai Aaminat gidan biki komai ya ƙara rincaɓe mata, Umma ta ɗauki Fushi da ita Mama kuwa tsakaninta da ita sai dai habaici da nuna ƙyama a cewarsu itama ta iskance, Ba ta da aiki sai na kuka sai kuma aikace aikacen tsakar gida wanda ba mai yi sai ita, Ta na son fita amma ta na tsoron ta yi mugun Katari da Abdul, yau dai ta yanke shawarar fita da tsakar rana don ta san a Lokacin yawanci ba ya zama, Ta yi sallama aƙalla biyar kafin Siyama ta amsa ba tare da ta kalleta ba hankalinta na kan wayar hannunta, Aaminat ta ce "Siyama meke damunki haka ne? sai sallama nake kamar ba ki da kunnuwa" ajiye wayar ta yi ta ja numfashi kafin ta ce "Hmm ba a magana Ƙawata, wai Ina ki ka shiga ne kwana biyu?, wani littafi nake karantawa Abin tausayi wallahi, kin ganni nan yanzu na gama sharar ƙwalla, Anti ba ta nan sai ni kaɗai a gidan kuma ba ni da aiki, ai gaskiya Novel ya na temakawa sosai sabi da ya na ɗebe kewa, dan dai bakya ra'ayinsa ne da kin rage wannan koke-koken naki." Aaminat ta ce "Novel wannan ai sai ke Siyama, amma kuma shi ne har da kuka? me ya yi zafi haka?'' "Hmm! ai dole na yi kuka, kema sai kin koka in ki ka ji abin da ke faruwa." "To wai ya sunan littafin? me ya faru kuma?" Siyama ta ce "Sai kin gyara zamanki in kina so sai in baki labari." Aaminat ta murmusa kafin ta ce "Na daɗe ban yi hira da mutane ba ma bare na yi nishaɗi, kema kin dena shigar min, yanzu dai bani labarin ko zan ji daɗi." Siyama ta gyara zama sannan ta ce "Ke ni wallahi ba na son mugun kallon da Mamanku take min, ga habaice habaicen jaraba, yanzu dai ki saurari labari, Sunan Littafin DOGON YARO Marubuciyar sunanta Ayeesha Abdulkareem INDO CE ."
© INDO CE & AUTAR JARUMAI
[7/26, 2:46 PM] INDO: *AAMEENAT*
(Bazawara)
Littafin HaÉ—aka ne💪ðŸ¾
Ayeesha Abdulkareem
*INDO*
Daga ELEGANT ONLINE WRITER'S
Tare da
Salma Abdulkareem
*AUTAR JARUMAI*
Daga JARUMAI WRITER'S
Shafi 8
Kowa a Falon hira ya ke cikin nishaÉ—i amma banda shi, ya yi shiru ya na tunanin Aaminat rabonsa da ganinta tin ranar Bikin Bilkisu hakan ya sa duk ya shiga damuwa, abin da ya fi tashin hankalinsa ma rabuwar da su ka yi baram baram bai san a halin da ya jefata ba.
Abdulmajid ya ƙare masa kallo kafin ya ce "Kai tunanin me ka ke ne?? ba na son ɗorawa kai wahala, kai dai ba ka da wani haufi a rayuwa sai dai in kai ka jawowa kanka abin da zai sa ka tagumi." ya ɗan murmusa cikin son kauda zancen ya ce "Ba abin da ya dame ni, kawai jina nake kamar an yi min dukan tsiya, wai yaushe za mu je Abuja ne??" Abdussalam ya ce "Wallahi Ƙarya yake, ku tuhume shi, na lura kwanakin nan ba iya yau ba ma duk ya bi ya wani firgici, ku ce ya ɗaga rigarsa ku ga yadda ƙashin haƙarƙarinsa su ka fito, duk ya bi ya rarrame amma don kafiya idan ance akwai abin da ya dame shi sai ya ce aa." Ƙasa ya yi da kai don kuwa ba shi da ta cewa Zuciyarsa ta wani mugun karaya, yanzu kuwa ya ce musu Aaminat ya ke so ta dalilinta ya shiga wannan halin, Allah ne kaɗai ya san abin da zai faru, Abdurrahim ne ya katse masa tunanin da cewa "ka Sunkuyar da kai Hakan na nufin dai da gaske ka tsumbula kanka cikin Aradu." girgiza kai ya yi zai yi magana hawaye suka fara zuba sharrrr, ya yi saurin sunkuyar da kai ya na ƙoƙarin goge su. Abdussamad ya tashi ya dawo kusa da shi ya zauna, cikin lallami ya ce "Abdulkareem, ba ka da wasu tamkar mu Ƴan uwanka, mu ne dolenka, kar ka ɓoye mana abin da ke damunka ka faɗa mana." Ummi da ta ke binsu da ido sai a lokacin ta ce "Gaskiya ne Auta, ka faɗa ko da da temakon da zamu iya yi maka, don nima na lura abin har ya fara yawa musamman a cikin wannan Ƙadamin." Murmushi me tafi da hawaye ya yi kafin ya ce "Ba zan iya cewa ga abin da ya ke damuna ba, don Allah ku zuba min ido kawai Sabi da ba ku da abin da za ku magance min damuwata" kallon kallo su ka yi kafin Abdulmajid ya ce "Abin har ya yi tsauri ne haka?? Auta ko ba a haiyacinka kake ba? ka na tunanin duk cikinmu akwai abin da zai gagara mu yi maka??" Ya rausayar da kai kafin ya ce "Ba za ku taɓa Fahimta ba YaYa, ita fa rayuwa komai matsayinsa daban, wani abin da kuɗi ake sayensa wani kuwa ko da kaine mafi kuɗi a Duniya sai ya gagareka ba za ka iya saya ba, kuma a rayuwa ba za ka ce ko da yaushe sai dai ka yi farin ciki ba, akwai Launi kala-kala a Cikin rayuwa, hakan ya na daga cikin jarrabawar ɗan Adam, duk cikar ka da kaiwarka akwai abin da ka rasa kuma ka ke da burin samunsa, don Allah a rufe wannan maganar." dukkansu sakin bakuna su ka yi su na kallonsa cike da mamaki da kuma nazarin inda kalamansa su ka dosa sai dai sun kasa fahimta me yake nufi, Nana Kadija ta ce "Ya Audu ya na da gaskiya fa, a cikin kalamansa babu na banza, a rufe zancen kawai." goge hawayensa ya yi sannan ya dalla mata harara ya ce "Ban hana ki kirana Audun nan ba??" "To ai naga Sunanka ne" "Ki na buƙatar rasa haƙoranki ko??" ta yi farrr da ido ta ce "Ba zan rasa komai ba ai dai sunanka ne kuma ba zan dena faɗe ba." filo ya ɗauka ya wurga mata ta doka tsalle ta koma kusa da Ummi, ya yi ƙwafa kafin ya miƙe ya ce "Ni waje ma zan fita" Abdussamad ya ce "Sai ka dawo!" tin da ya fita magana sai ɗaiɗai a Falon sakamakon da da suka cika shi da surutu, kowa nazarin kalaman Abdulkareem ya ke har Ita Kanta Ummi, abin da su ke ta tambayar kansu shine menene ya sa shi faɗen hakan?
Tin daga ranar da Fati ta faɗi cewa Abdulkareem ya kai Aaminat gidan biki komai ya ƙara rincaɓe mata, Umma ta ɗauki Fushi da ita Mama kuwa tsakaninta da ita sai dai habaici da nuna ƙyama a cewarsu itama ta iskance, Ba ta da aiki sai na kuka sai kuma aikace aikacen tsakar gida wanda ba mai yi sai ita, Ta na son fita amma ta na tsoron ta yi mugun Katari da Abdul, yau dai ta yanke shawarar fita da tsakar rana don ta san a Lokacin yawanci ba ya zama, Ta yi sallama aƙalla biyar kafin Siyama ta amsa ba tare da ta kalleta ba hankalinta na kan wayar hannunta, Aaminat ta ce "Siyama meke damunki haka ne? sai sallama nake kamar ba ki da kunnuwa" ajiye wayar ta yi ta ja numfashi kafin ta ce "Hmm ba a magana Ƙawata, wai Ina ki ka shiga ne kwana biyu?, wani littafi nake karantawa Abin tausayi wallahi, kin ganni nan yanzu na gama sharar ƙwalla, Anti ba ta nan sai ni kaɗai a gidan kuma ba ni da aiki, ai gaskiya Novel ya na temakawa sosai sabi da ya na ɗebe kewa, dan dai bakya ra'ayinsa ne da kin rage wannan koke-koken naki." Aaminat ta ce "Novel wannan ai sai ke Siyama, amma kuma shi ne har da kuka? me ya yi zafi haka?'' "Hmm! ai dole na yi kuka, kema sai kin koka in ki ka ji abin da ke faruwa." "To wai ya sunan littafin? me ya faru kuma?" Siyama ta ce "Sai kin gyara zamanki in kina so sai in baki labari." Aaminat ta murmusa kafin ta ce "Na daɗe ban yi hira da mutane ba ma bare na yi nishaɗi, kema kin dena shigar min, yanzu dai bani labarin ko zan ji daɗi." Siyama ta gyara zama sannan ta ce "Ke ni wallahi ba na son mugun kallon da Mamanku take min, ga habaice habaicen jaraba, yanzu dai ki saurari labari, Sunan Littafin DOGON YARO Marubuciyar sunanta Ayeesha Abdulkareem INDO CE ."
© INDO CE & AUTAR JARUMAI
[7/26, 2:46 PM] INDO: *AAMEENAT*
(Bazawara)
Littafin HaÉ—aka ne💪ðŸ¾
Ayeesha Abdulkareem
*INDO*
Daga ELEGANT ONLINE WRITER'S
Tare da
Salma Abdulkareem
*AUTAR JARUMAI*
Daga JARUMAI WRITER'S
Shafi 8