Sashe 33
Aaminat Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da yamma gafda za'akai Amarya
Gidan su Fati faɗa ya ɓarke tsakanin dangin Abba da na Mama, saka makon ɓatan wayar ƴar ƙanwar Abba, Mama sai zage-zage take kamar mahaukaciya wai an ɗorawa dangin ta sata, haka sukaita turnuƙu ana bala'i, ɗaya daga cikin dangin Abba ta ce "ai Bara'atu kinyi asara ƴaƴa a lalace, ke a tambaɗe, Abinci agidannan gagarar mu yayi saidai kuci keda gaiyar tsiyarki," ta ƙarasa maganar tana huci, rai a ɓace Bara'atu (Mama) ta ce "ni kike cewa atambade to wallahi ƙaryar ki, ni zaki duba kicewa ƴaƴa a lalace,??.. to ai basukai na wadda ta ɗora ƴaƴan akan karuwanci ba, garani na basu tarbiya," wata shewa dangin Abba suka sa,, Jamila ƙanwar Abba ta kalli Umma gami da cewa "to tsohuwar munafuka ai anyi walƙiya mungan ki, yanzu munsan sharri kikewa Umma agidan nan kuma da tanan ƙaryarki ki hanamu Abinci," sakin baki Mama tayi sakaka tana kallon su, ta kasa cewa komai, hakan ya ƙara turnuƙeta, su Alawiyya da ma suna cen suna nasu faɗan, Mama kuwa ganin batayi nasara ba, yasa ta nufi ɗaki, fakan-fakan sharaf-sharaf tana kuka, dangin Abba kuwa tuni sun haɗa kayansu sunce barin gidan zasuyi, kaɗan ne suka zauna suma don ya zama dolen su ne,
Umman Nazir Autar su Umma da Anti maman su Siyama, sai Aaminat da take cikin shirin Atamfa mai kyau da tsada, riga da zani, sai ƙaton mayafin da aka rufeta ruf,, tana zaune agefen gado tana kuka, Umman Nazir ta ce "Aaminat kibi mijinki, kibi duk abinda ya ce indai hakan bai saɓawa addini ba, kiyi biyayya wa iyayan mijinki yanzu sune iyayanki, kinji, ki kyauta tawa dangin Mijinki,, kar inji kar ingani kinyi abinda bai kamata ba kinji ko,"
Auta ta ce "komai yayi zafi maganin sa Allah duk abinda za'ayi miki, toki kauda kai wata rana sai labari, mahaƙurci mawadaci, kiyi koyi da halin mahaifiyarki ki zama mai haƙurin gaske ki jure ki cije,"
Banda kuka ba abinda Aaminat take, Anti ta muskuta gami da cewa "nasanki da kafiya wani lokacin, to ki daina kinji, yi nayi bari na bari, karki kuskura ki ɗauki zigar ƙawaye duk abinda zasuce miki kiyi watsi da shi, kibi mijinki sau da ƙafa, kinji ƴata"
haka sukaci gaba da yi mata faÉ—a, da nasihohi, masu ratsa jiki,
Maman Humaira ce ta shigo da sallama suka amsa, Anti ta duba gami da cewa "masu É—aukar Amarya suna jira ance ku fito da ita," "to yanzu ma kuwa in sha Allahu ga mu nan", Anti ta faÉ—a, Maman Humaira ta juya zuwa wajen Æ´an É—aukar Amarya,
Siyama ce ta shigo ɗakin tana kuka, Aaminat tana jin kukan Siyama ta ƙara fashewa da kuka, da gudu Siyama ta rungume Aaminat tana wani kuka mai tsuma zuciya, cikin muryar kuka Siyama ta ce "Aaminat yanzu rabuwa zamuyi zaki tafi ki barni," Aaminat kuwa ta kasa koda magana sai kuka, ko ɗaga harshe ta kasa, da sunan tayi magana, Umman Nazir ce ta kama hannun Aminat, Auta ta janye Siyama, sukansu su Umman Nazir ɗin saida suka share hawaye, duk wanda yaga yadda Siyama da Aaminat suke ɓarzar kuka saiya tausaya musu, gashi sun shaƙu, "dan Allah kudaina kuka kunji kuyi haƙuri rabuwa ta zama dole saidai ziyara," wani kukan Aaminat ta ƙara rushewa da shi, Umman Bazir taja Aaminat, dan kuwa daƙirewa tayi,
Ɗakin da Umma da su Baba Usman suke, suka shiga da Aaminat, durƙusawa tayi kan guiwoyinta tana kuka kamar ranta zai fita, cikin tausayawa Umman Nazir ta ce "kiyiwa mahaifiyarki sallama ki nemi yafiyarta," cikin sarƙaƙƙiyar murya mai cike da ban tausayi ta ce "U ....u....u...umm..umma ki yafemin!!!!!!" cike da jarumta Umma ta ce "ba kiyi min laifin komai ba Aaminat Allah yayi miki albarka, Allah ya baku zaman lafiya" mutanen ɗakin suka amsa da Ameen,, Anti ta ce "to Umma zamu tafi da Aaminat ɗakinta kuyi sallama," murya na rawa Aaminat ta ce "Um...umma zan tafi ki yafe min dan Allah," "Allah ya tsare hanya, ya kaiku lafiya," hannun Aaminat suka kama zasu tasheta saidai sukeji ta riƙe, Umma gamm, haka sukaita ƙwarbe da ita kana suka samu nasarar raba Aaminat da Umma, kai tsaye mota suka shige kowa ya shiga mota suka kama hanyar gidan Amarya,
Æangaren Fati ma tuni an tafi da ita,
Basu ɓata lokaci ba suka ƙarasa gidan su Yarima jagora akayi musu zuwa ɓangaren Ammi, gaisawa sukayi sannan sukayi ƴan addu'oi, Anti ta ce "ga Amana nan mun kawo muku, idan tayi ba dai-dai ba ku gyara mata ku nuna mata, dan Allah, duk abinda tayi in me kyaune kune in mara kyaune kune, mudai ga Amana nan mun baku," Anti Zainab ta muskuta gami da cewa "in sha Allahu zaku samemu masu gaskiya da ruƙon Amana, kuma in Allah yayarda mun zama ɗaya ƴarmu ce", cike da gamsuwa sukayi sallama suka raka Aaminat ɗakin ta dake wani sashi na gidan,
Basu daÉ—e ba kowa ya kama gaban sa suka koma gidan, Siyama Umaima Iman Ameera, su kai É—aina agidan suna taya Aaminat zama,
Bayan na É—an wani lokaci
suna zaune agefen Gado sukaji sallama, amsawa sukayi sannan suka bashi izinin shigowa,
Sabir yana ƴar dariya ya ce "ƴan mata, mai guri yazo sai mai tabarma ya naɗe," tsaki Siyama tayi gami da cewa "ai ba cewa mukayi zamu zauna ba," dariya yayi dama kunnasu yake sonyi kuma ya kunna, "kuma babu wadda zamu mayar, wayace baku bi manya kun koma gida ba" Siyama taja tsaki cike da baƙinciki Iman ta dube shi ta ce "kaga malam ka tattara ya naka ya naka ka bamu waje musha iska," dariya yayi cike da tsokana irin tasa ya ce "ni ai gidan mune kune zaku tattara komatsanku ku bar mana gida",.... zai ƙarayin magana yaji Sallamar su Yarima, da sauri ya ce "yanzu dama zan fito" Sulaiman ya ce "na mata na mata kawai tun ɗazu daga aike kanemi waje kayi zaman ka," ɗan sosa sumar kansa yayi, su Umaima suka gaida Yarima, Siyama kuwa ko kallon sa batayi ba, ta figi Jakar ta ta na "cewa sai ku tashi mu tafi tunda ba gidan ku bane," ba musu suka tashi, Yarima ya ɗan murmusa gami da cewa Iman "mai akayiwa Siyama ne" murmushi tayi gami da cewa "wai fishi take ka rabata da Aminiyar ta," murmusawa yayi gami da cewa "haka dama rayuwar take sai haƙuri," batace komaiba tabi bayan su Umaima, Yarima ya dubi su Sabir ya ce "to ku kuma mai kuke jira," dariya suka sa, sannan Sabir ya ce "babu abinda muke jira tafiya zamuyi" "to sai ku tafi" Yarima ya faɗa yana hararar su, fita sukayi, Sabir ya wuce harabar gidan, yana zuwa ya tarar su Siyama sun shiga motar Iman sun tafi sai ƙyellinsu ya hango ta get, baiji daɗin hakan ba so yayi sun ƙara casuwa, hakan yasa ya juya y nufi ɗakin da suka sauka,
Æan garen su Yarima kuma saidai na ce Asuba ta gari,,
Indo â¤â€ðŸ©¹ Salma
[8/9, 1:33 PM] INDO: *AAMEENAT*
(Bazawara)
Littafin HaÉ—aka ne💪ðŸ¾
Ayeesha Abdulkareem
*INDO*
Daga MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
Tare da
Salma Abdulkareem
*AUTAR JARUMAI*
Daga JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION
Shafi 28
Bayan Biki da kwana uku kowa da ya halarci taron Bikin ya koma gidan sa, su Umma ma sun koma gida taro ya tashi lafiya Alhamdulillah,
Sanye take cikin dakakken leshi fari ɗinkin buba yaji adon duwatsu masu sheƙi da ƙelli, a hankali da nutsuwa take sakkowa daga benen dake ƙaton Falon, wanda yaji kayan more rayuwa, da kayan alatu iri-iri, komai na Falon pink da fari ne, kama daga kan kujeru kwalliyar Falon, komai pink da fari ne, kai Falon fa ya haɗu iya haɗuwa ya tsaru, Ma sha Allah, zama tayi akan ɗaya daga cikin luntsuma-luntsuman kujerun Falon, kai dagani kasan an zuba kuɗaɗa na tashin hankali, wani tattausain murmushi ne ya kufce mata, har saida fararen haƙoranta suka baiyana, sallamar da akayi ce ta fargar da ita tayi saurin haɗe fuska, ƙarasowa yayi cike da jin daɗi da farin ciki, ya ce "wa na kama???" ya faɗa yana dariya, murmusawa tayi kafin ta buɗe baki ta ce "yanzu ma ai baka kamani ba," "haka zakice ko??" "A'a nifa banyi magana ba," "mai kika ce??" ya faɗa yana zuba mata wani sihirtaccen kallo mai rikitarwa, murya ƙasa-ƙasa ta ce "ce wa nayi sannu da zuwa" dariya yayi gami da cewa "Aaminat wato kin rainani ko" "ni na isa in raina ka," murmusawa yayi, batare da ya ce komai ba, shirune ya ɗan ratsa na wani lokaci kafin Yarima ya ce "ni zan wuce Asibiti kije sashin su Ammi ki zauna kafin na dawo" "to" ta ce tana tashi, kallon ta yayi gami da cewa "saura kuma inna dawo kiyi zamanki ki ƙi zuwa," dariya tayi, yaɗan harareta harara mai tafe da saƙonnin so, kala-kala, wani murmushi ne ya kufce mata tayi saurin rufe fuskar ta da tafukan hannunta, juyawa yayi ya fara tafiya cikin nutsuwa, bayan sa tabi, ma'ajiyar motocin gidan ta rakashi, sannan ta juya ta koma,
.
.Fati tana zaune a hamshaƙin Falon ta tana latsa waya, Ahmad ne ya shigo, wani kallo yayi mata mai cike da ma'anoni, sannan ya zauna kusa da ita, cikin yauƙi ta ce "Baby na sannu fa" "yauwa ya gidan,??" "lafiya" wani musmushi ya kumayi mai cike da tsantsar ma'ana, tashi yayi zai wuce ta ce "gaskiya mota nakeson ka siyamin," "mota kuma??" "eh mota ko bazaka siya ba?" murmusawa yayi gami da cewa "yaufa kwananki uku agidan nan, mai ki ke ci na baka na zuba, Habibti na" cingam ɗin bakinta ta tauna tare da "cewa shikenan"
haka sukaci gaba da ƴar hira tana nuna masa son duniya ƙarara, shima ya na nuna mata na sa salon.
Gidan su Fati faɗa ya ɓarke tsakanin dangin Abba da na Mama, saka makon ɓatan wayar ƴar ƙanwar Abba, Mama sai zage-zage take kamar mahaukaciya wai an ɗorawa dangin ta sata, haka sukaita turnuƙu ana bala'i, ɗaya daga cikin dangin Abba ta ce "ai Bara'atu kinyi asara ƴaƴa a lalace, ke a tambaɗe, Abinci agidannan gagarar mu yayi saidai kuci keda gaiyar tsiyarki," ta ƙarasa maganar tana huci, rai a ɓace Bara'atu (Mama) ta ce "ni kike cewa atambade to wallahi ƙaryar ki, ni zaki duba kicewa ƴaƴa a lalace,??.. to ai basukai na wadda ta ɗora ƴaƴan akan karuwanci ba, garani na basu tarbiya," wata shewa dangin Abba suka sa,, Jamila ƙanwar Abba ta kalli Umma gami da cewa "to tsohuwar munafuka ai anyi walƙiya mungan ki, yanzu munsan sharri kikewa Umma agidan nan kuma da tanan ƙaryarki ki hanamu Abinci," sakin baki Mama tayi sakaka tana kallon su, ta kasa cewa komai, hakan ya ƙara turnuƙeta, su Alawiyya da ma suna cen suna nasu faɗan, Mama kuwa ganin batayi nasara ba, yasa ta nufi ɗaki, fakan-fakan sharaf-sharaf tana kuka, dangin Abba kuwa tuni sun haɗa kayansu sunce barin gidan zasuyi, kaɗan ne suka zauna suma don ya zama dolen su ne,
Umman Nazir Autar su Umma da Anti maman su Siyama, sai Aaminat da take cikin shirin Atamfa mai kyau da tsada, riga da zani, sai ƙaton mayafin da aka rufeta ruf,, tana zaune agefen gado tana kuka, Umman Nazir ta ce "Aaminat kibi mijinki, kibi duk abinda ya ce indai hakan bai saɓawa addini ba, kiyi biyayya wa iyayan mijinki yanzu sune iyayanki, kinji, ki kyauta tawa dangin Mijinki,, kar inji kar ingani kinyi abinda bai kamata ba kinji ko,"
Auta ta ce "komai yayi zafi maganin sa Allah duk abinda za'ayi miki, toki kauda kai wata rana sai labari, mahaƙurci mawadaci, kiyi koyi da halin mahaifiyarki ki zama mai haƙurin gaske ki jure ki cije,"
Banda kuka ba abinda Aaminat take, Anti ta muskuta gami da cewa "nasanki da kafiya wani lokacin, to ki daina kinji, yi nayi bari na bari, karki kuskura ki ɗauki zigar ƙawaye duk abinda zasuce miki kiyi watsi da shi, kibi mijinki sau da ƙafa, kinji ƴata"
haka sukaci gaba da yi mata faÉ—a, da nasihohi, masu ratsa jiki,
Maman Humaira ce ta shigo da sallama suka amsa, Anti ta duba gami da cewa "masu É—aukar Amarya suna jira ance ku fito da ita," "to yanzu ma kuwa in sha Allahu ga mu nan", Anti ta faÉ—a, Maman Humaira ta juya zuwa wajen Æ´an É—aukar Amarya,
Siyama ce ta shigo ɗakin tana kuka, Aaminat tana jin kukan Siyama ta ƙara fashewa da kuka, da gudu Siyama ta rungume Aaminat tana wani kuka mai tsuma zuciya, cikin muryar kuka Siyama ta ce "Aaminat yanzu rabuwa zamuyi zaki tafi ki barni," Aaminat kuwa ta kasa koda magana sai kuka, ko ɗaga harshe ta kasa, da sunan tayi magana, Umman Nazir ce ta kama hannun Aminat, Auta ta janye Siyama, sukansu su Umman Nazir ɗin saida suka share hawaye, duk wanda yaga yadda Siyama da Aaminat suke ɓarzar kuka saiya tausaya musu, gashi sun shaƙu, "dan Allah kudaina kuka kunji kuyi haƙuri rabuwa ta zama dole saidai ziyara," wani kukan Aaminat ta ƙara rushewa da shi, Umman Bazir taja Aaminat, dan kuwa daƙirewa tayi,
Ɗakin da Umma da su Baba Usman suke, suka shiga da Aaminat, durƙusawa tayi kan guiwoyinta tana kuka kamar ranta zai fita, cikin tausayawa Umman Nazir ta ce "kiyiwa mahaifiyarki sallama ki nemi yafiyarta," cikin sarƙaƙƙiyar murya mai cike da ban tausayi ta ce "U ....u....u...umm..umma ki yafemin!!!!!!" cike da jarumta Umma ta ce "ba kiyi min laifin komai ba Aaminat Allah yayi miki albarka, Allah ya baku zaman lafiya" mutanen ɗakin suka amsa da Ameen,, Anti ta ce "to Umma zamu tafi da Aaminat ɗakinta kuyi sallama," murya na rawa Aaminat ta ce "Um...umma zan tafi ki yafe min dan Allah," "Allah ya tsare hanya, ya kaiku lafiya," hannun Aaminat suka kama zasu tasheta saidai sukeji ta riƙe, Umma gamm, haka sukaita ƙwarbe da ita kana suka samu nasarar raba Aaminat da Umma, kai tsaye mota suka shige kowa ya shiga mota suka kama hanyar gidan Amarya,
Æangaren Fati ma tuni an tafi da ita,
Basu ɓata lokaci ba suka ƙarasa gidan su Yarima jagora akayi musu zuwa ɓangaren Ammi, gaisawa sukayi sannan sukayi ƴan addu'oi, Anti ta ce "ga Amana nan mun kawo muku, idan tayi ba dai-dai ba ku gyara mata ku nuna mata, dan Allah, duk abinda tayi in me kyaune kune in mara kyaune kune, mudai ga Amana nan mun baku," Anti Zainab ta muskuta gami da cewa "in sha Allahu zaku samemu masu gaskiya da ruƙon Amana, kuma in Allah yayarda mun zama ɗaya ƴarmu ce", cike da gamsuwa sukayi sallama suka raka Aaminat ɗakin ta dake wani sashi na gidan,
Basu daÉ—e ba kowa ya kama gaban sa suka koma gidan, Siyama Umaima Iman Ameera, su kai É—aina agidan suna taya Aaminat zama,
Bayan na É—an wani lokaci
suna zaune agefen Gado sukaji sallama, amsawa sukayi sannan suka bashi izinin shigowa,
Sabir yana ƴar dariya ya ce "ƴan mata, mai guri yazo sai mai tabarma ya naɗe," tsaki Siyama tayi gami da cewa "ai ba cewa mukayi zamu zauna ba," dariya yayi dama kunnasu yake sonyi kuma ya kunna, "kuma babu wadda zamu mayar, wayace baku bi manya kun koma gida ba" Siyama taja tsaki cike da baƙinciki Iman ta dube shi ta ce "kaga malam ka tattara ya naka ya naka ka bamu waje musha iska," dariya yayi cike da tsokana irin tasa ya ce "ni ai gidan mune kune zaku tattara komatsanku ku bar mana gida",.... zai ƙarayin magana yaji Sallamar su Yarima, da sauri ya ce "yanzu dama zan fito" Sulaiman ya ce "na mata na mata kawai tun ɗazu daga aike kanemi waje kayi zaman ka," ɗan sosa sumar kansa yayi, su Umaima suka gaida Yarima, Siyama kuwa ko kallon sa batayi ba, ta figi Jakar ta ta na "cewa sai ku tashi mu tafi tunda ba gidan ku bane," ba musu suka tashi, Yarima ya ɗan murmusa gami da cewa Iman "mai akayiwa Siyama ne" murmushi tayi gami da cewa "wai fishi take ka rabata da Aminiyar ta," murmusawa yayi gami da cewa "haka dama rayuwar take sai haƙuri," batace komaiba tabi bayan su Umaima, Yarima ya dubi su Sabir ya ce "to ku kuma mai kuke jira," dariya suka sa, sannan Sabir ya ce "babu abinda muke jira tafiya zamuyi" "to sai ku tafi" Yarima ya faɗa yana hararar su, fita sukayi, Sabir ya wuce harabar gidan, yana zuwa ya tarar su Siyama sun shiga motar Iman sun tafi sai ƙyellinsu ya hango ta get, baiji daɗin hakan ba so yayi sun ƙara casuwa, hakan yasa ya juya y nufi ɗakin da suka sauka,
Æan garen su Yarima kuma saidai na ce Asuba ta gari,,
Indo â¤â€ðŸ©¹ Salma
[8/9, 1:33 PM] INDO: *AAMEENAT*
(Bazawara)
Littafin HaÉ—aka ne💪ðŸ¾
Ayeesha Abdulkareem
*INDO*
Daga MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
Tare da
Salma Abdulkareem
*AUTAR JARUMAI*
Daga JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION
Shafi 28
Bayan Biki da kwana uku kowa da ya halarci taron Bikin ya koma gidan sa, su Umma ma sun koma gida taro ya tashi lafiya Alhamdulillah,
Sanye take cikin dakakken leshi fari ɗinkin buba yaji adon duwatsu masu sheƙi da ƙelli, a hankali da nutsuwa take sakkowa daga benen dake ƙaton Falon, wanda yaji kayan more rayuwa, da kayan alatu iri-iri, komai na Falon pink da fari ne, kama daga kan kujeru kwalliyar Falon, komai pink da fari ne, kai Falon fa ya haɗu iya haɗuwa ya tsaru, Ma sha Allah, zama tayi akan ɗaya daga cikin luntsuma-luntsuman kujerun Falon, kai dagani kasan an zuba kuɗaɗa na tashin hankali, wani tattausain murmushi ne ya kufce mata, har saida fararen haƙoranta suka baiyana, sallamar da akayi ce ta fargar da ita tayi saurin haɗe fuska, ƙarasowa yayi cike da jin daɗi da farin ciki, ya ce "wa na kama???" ya faɗa yana dariya, murmusawa tayi kafin ta buɗe baki ta ce "yanzu ma ai baka kamani ba," "haka zakice ko??" "A'a nifa banyi magana ba," "mai kika ce??" ya faɗa yana zuba mata wani sihirtaccen kallo mai rikitarwa, murya ƙasa-ƙasa ta ce "ce wa nayi sannu da zuwa" dariya yayi gami da cewa "Aaminat wato kin rainani ko" "ni na isa in raina ka," murmusawa yayi, batare da ya ce komai ba, shirune ya ɗan ratsa na wani lokaci kafin Yarima ya ce "ni zan wuce Asibiti kije sashin su Ammi ki zauna kafin na dawo" "to" ta ce tana tashi, kallon ta yayi gami da cewa "saura kuma inna dawo kiyi zamanki ki ƙi zuwa," dariya tayi, yaɗan harareta harara mai tafe da saƙonnin so, kala-kala, wani murmushi ne ya kufce mata tayi saurin rufe fuskar ta da tafukan hannunta, juyawa yayi ya fara tafiya cikin nutsuwa, bayan sa tabi, ma'ajiyar motocin gidan ta rakashi, sannan ta juya ta koma,
.
.Fati tana zaune a hamshaƙin Falon ta tana latsa waya, Ahmad ne ya shigo, wani kallo yayi mata mai cike da ma'anoni, sannan ya zauna kusa da ita, cikin yauƙi ta ce "Baby na sannu fa" "yauwa ya gidan,??" "lafiya" wani musmushi ya kumayi mai cike da tsantsar ma'ana, tashi yayi zai wuce ta ce "gaskiya mota nakeson ka siyamin," "mota kuma??" "eh mota ko bazaka siya ba?" murmusawa yayi gami da cewa "yaufa kwananki uku agidan nan, mai ki ke ci na baka na zuba, Habibti na" cingam ɗin bakinta ta tauna tare da "cewa shikenan"
haka sukaci gaba da ƴar hira tana nuna masa son duniya ƙarara, shima ya na nuna mata na sa salon.