Sashe 31
Aaminat Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ammi ce zaune a kan kujera a Falon ta tana latsa waya, Anti Zainab ta shigo da sallama, Ammi ta amsa tare da cewa "Anti ina Yarima ya shige ne tin ɗazu nake neman sa" "kinsan sa baya son hayaniya kuma gidan namu ya fara cika" "to banda abinsa ai shiya tara taron" Anti Zainab ta zauna kusa da Ammi tana cewa "washh wallahi na gaji" "sannu ai da gajiya" Kausar ce ta shigo da sallama, Anti ta amsa gami da cewa "daga ina haka naganki da kaya niƙi-niƙi???" "daga wajen mai ɗinki nake " "kije ki watsa ruwa kizo kici Abinci" "to Anti" Ammi ta miƙe gami da cewa "bari naje madafa naga ya aikin yake tafiya" "to nima yanzu zanzo" Anti ta faɗa tana kashingiɗa,
"Aaminat tana kwance a ɗakin su Iman tana kuka taji wayarta tana ruri, banza tayiwa wayar ta cigaba da kukanta, saida kiran ya katse wani ya shigo sannan ta ɗauki wayar batare da ta duba maikiran ba, karawa tayi akunne, batare da tayi magana ba, "Salamu'alaiki" murya a daƙile ta ce "Amin wa alaikassalam" murmusawa yayi, gami da cewa "Aaminat kin shirya ne" "A'a" "saboda me baki shirya ba shida tayi fa" "nifa nace maka babu inda zanje" "Aaminat kiyi haƙuri dan Allah kije in bakije ba bansan yadda zancewa dangi na ba kuma nace musu zaki je" ɗan ƙaramin tsaki tayi, "Aminat dan Allah ki tausaya min kije," "nifa bazani ba ai ba wannan ne Aure na nafar koba kaga ai ba saina wani je ba" wata zazzafar ajiyar zuciya ya sauke tare da rintse ido, sun ɗauki minti yakai biyu babu wanda yayi magana, Yarima ne yayi ta maza yace "shikenan tunda bazaki ba saiki zauna, kiyi abinda kika ga dama tinda ba a'isa dake ba," yana gama faɗin haka ya kashe kiran rai aɓace, dan kuwa Aminat ta fara ɓata mai rai, kusan kwana biyar yana fama da ita amma taƙi yarda,
Aminat kuwa kuka ta ƙara fashewa dashi, dai-dai lokacin Siyama Umaima Iman suka kutso kai ɗakin, turusss sukayi ganin Aaminat ta zage tana ɓarzar kuka, da sauri sukayi kanta suna cewa "maiyafaru??" banza tayi dasu, Umaima ta ce "ya Aminat baki da lafiya ne ko wani abu akayi miki??" cikin kuka tace "babu komai" "to maiya faru kike kuka??" share hawaye tayi tare da cewa "Yarima ne wai sainnaje gurin Dinner kuma ni banason zuwa" sheƙewa sukayi da dariya ta saki baki tana kallon su, Simaya ta ce "amma kin bani dariya, akan haka kika zauna kina ta kuka sai kace wadda akace za'a kashe" Aaminat ta shiga goge hawayen gami da cewa "kukan ma baza'a bar mutum yayi mai daɗi ba, sai an takura masa" "iyeeee kukan ma hada mai daɗi ko???" tsaki tayi taja ƙaton bargo ta rufa, wayar ta ce ta fara kuwwa ya duba mai kiran da mamakin ta sai taga wata number ba irin ta ƙasar nan ba, saida ta kusa yankewa sannan ta ɗauka, tare da sallama, amsawa yayi, cikin nutsuwa ya ce "maiyasa bazakije wajen shagalin bkinki ba" wani dummmm taji zuciyar ta tayi, adiririce ta ce "A...a...a....Abdul kaine" "nine Yaya dan Allah kiyi mana alfarma kije dan Allah" tana dariya dariya kuka kuka ta ce "to zani amma bazan daɗe ba, Abdul ka dawo don Allah" "to kitashi kishirya kuma dan Allah ki daina wahalarmin Aminina bana jin daɗin hakan, idan lokacin dawowata ya yi zan dawo" wasu sabbin hawaye ne suka fara sabuwar zarya akan tausasan kumatunta, ta ce "to zan daina" "to Allah ya sanya alkairi ya kauda fitina amma kin ɓatawa Abubakar rai kikira sa ki bashi haƙuri" "to" ta ce daga haka sukayi sallama,
Umaima ta kalli Aaminat ta ce "gaskiya ki rage abinda kikewa yaya Abubakar gobe iyanzu fa kina gidan sa," "nima dai haka nagani haka kawai saita dinga tsangwamar bawan Allah" Aaminat kuwa banda cokalo baki babu abinda take, Ameeera ce ta shigo tana cewa "ga mai kwalliyar nan ta ƙaraso", "to ki ƙaraso da ita nan ɗaki" Iman ta faɗa Siyama ta kalli Aaminat, cikin sanyin murya ta ce "kije kiyi wanka lokaci yana ja", tashi Aaminat tayi ta shiga wanka,
bata jima ba ta fito daga wankan, zama tayi akan ƴar ƙaramar kujera, ta fara shafa mayuka masu ƙamshi da tsada, tin kafin ayi mata kwalliyar ta ɗau harama don kuwa ta sha gyara, fatarta ta yi suɓula sai ƙyalli da walƙiya take ta yi wani ɓulɓul, tana gamawa "Umaima ta kalli mai kwalliyar ta ce kije ki fara yimata", Aaminat ta ce "nifa ba saianyi mini Make-up ba" "ai kuwa dolenki ayi tunjiya kike faman wahalar da mutane dan iskanci, komai akace saiki ce ke bazakiyi ba to dole sai anyi kwalliyar nan" "yauwa maman Humaira tin ɗazu take ta butsewa taƙi yarda" wadda aka kira da maman Humaira ta ƙara ɗaure fuska babu alamun wasa, ta ce "maza ki farayi mata,"... ta makawa Aaminat harara ta ce "idan kika kuskura nadawo na tarar, baki zauna anyi miki ba sainayi rugu-rugu dake ja'ira" tana gama faɗin haka ta juya ta ficewar ta,
dan dole aka fara yiwa Aaminat Make-up anayi tana butsarewa, ko ta cokalo baki gaba tana mita,,
Fati ta shirya cikin tsadadden Leshi marun doguwar riga gown sai walwali take tayi kyau sosai san kowa ƙin wanda ya rasa, cikin yauƙi da yanga da jinkanta, take takawa har suka isa kofar gida inda aka aje motar ango da abokansa, kofar maya aka buɗe mata ta shiga, Direban ya fara jan motar a hankali suka ɗauki hanya,
cikin ɗan lokaci aka gama Make-up ɗin Aaminat wata riga Umaima ta miƙo mata, ta ce "kiyi kisa" batare da tace komai ba ta karɓi rigar ta fara sawa, Dogowar riga ce Baƙa da yarfin golden, mai irin buguzum ɗin nan irin ta indiawa, tayi mata mugun kyau tamkar wata sarauniyar kyawa-wa, takalmi golden tasa da wata ƴar ƙaramar jaka mai ƙyalli da sheƙi, wani ɗan ƙaramin mayafi, Siyama ta miƙo mata, ta karɓa ta yana a saman kanta, Iman da Umaima suka ɗauki wasu tsadaddun turaruka masu mugun ƙarfi da ƙamshi suka fara fesa mata kamar bazasu daina ba, Siyama ce ta kama hannunta cikin sanyi ta ce "muje ko" tirjewa tayi taƙi ta fiya, Siyama ta saita dai-dai kunnan ta ta ce "Aaminat kiyi haƙuri ki bamu haɗin kai dan Allah, karkiyi gardama," wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke,, sannan ta fara ɗaga ƙafar ta cikin nutsuwa, ahankali take takawa, kamar mai tsoron takawa, a haka suka isa babban ɗakin da Umma take ita da ƴan uwan ta da sauran mutane, suna shiga ɗakin ya kaure da buɗa, ahankali ta ƙarasa inda Umma take, kai ta kifa akan cinyar Umma, Umma ta shafa bayanta ta ce "Aaminat Allah yayi miki albarka ta shi kuje" ƙin tashi tayi saida Umaima ta kama hannun ta ya ɗagata, bayan anyi kamu, suka nufi ƙofar fita,
Aharabar gidan suka tsaya, inda wata jibgegeyar mota mai tadar gaske take Baƙa ce motar daganin motar kasan ba ta ƙanana mutane bace, wani kyak-kyawan saurayi ne ya buɗe ƙofar baya, kasan cewar duhu ya farayi hakan yasa bata lura da mutu ko babu ba ta shiga motar cikin nutsuwa, ahankali ta rufe murfin ƙofar, sannan ya zagaya ya shiga mazaunin Direba, su Siyama ma tasu motar suka shiga,, cikin nutsuwa Direban ya fara jan motar suka fita daga get ɗin gidan, saida suka hau titi, sannan Aaminat taji motsin mutum akusa da ita, matsawa tayi, gefe, wani ni'imtaccen murmushi ya saki, tare da lumshe ido, waya ya ɗauko ya kunna fitilar wayar, ya haska Aaminat yana wani tattausan murmushi, cikin nutsuwa ya kai hannun sa ya yaye gelen da ta rufe fuskarta, hawaye ne shaɓe-shaɓe kwance afuskarta, cikin tattausar muryarsa mai daɗin sauraro ya ce "sorry ki daina kuka, banason ganin zubar hawayen ki," wani numfashi taje ta sauke tare da, sauke nannauyar ajiyar zuciya, wani maraitaccen murmushi ya sakar mata, sannan ya miƙo mata tissue, ya ce kishare hawayan ki bana son ganin ki kina kuka dan Allah ki daina karki sa kanki ciwon kai,..." ya numfasa kafin ya ce "Aaminat dan Allah ki karɓa ki shara hawayan ki, kidaina kuka karki ɓata kwalliyarki," ƙin kaɓa tayi saima wasu hawayen da suke ƙara shararowa, cikin nutsuwa, Yarima ya fara share mata hawayen yana hura mata iska da bakin sa, hakan yasa ta fara jera ajiyar zuciya akai-akai, gyaran muryar da Sabir yayi ce ta dawo da Yarima cikin hayyacin sa,, Sabir ya kwashe da dariya gami da cewa "ya Abubakar dama ka iya soyyaya haka,???" tsaki Yarima yayi ya ce "kai ina wasa da kai???" "A'a wallahi salon nakane yake matsa ni" "kai Sabir ka fiya sa ido, dama hankalin ka yana kanmu ka saki tuƙin ko??" ƴar dariya yayi ya ce "ai dama shiyasa nace ni zan jaku" "ai kuwa idan na ƙarajin tarinka saina..." muryar Aaminat ce ta katse masa magana, jin tana cewa "kun isheni da surutu" murmusawa yayi ya ce "ranki ya daɗe tuba muke, mun daina" shiru tayi batace komai ba hakan yasa suma sukaja nasu bakunan suka tsuke,
Æan garen su Fati kuwa suna isa aka fara cashewa ana rawa kamar ba gobe,
"Aaminat tana kwance a ɗakin su Iman tana kuka taji wayarta tana ruri, banza tayiwa wayar ta cigaba da kukanta, saida kiran ya katse wani ya shigo sannan ta ɗauki wayar batare da ta duba maikiran ba, karawa tayi akunne, batare da tayi magana ba, "Salamu'alaiki" murya a daƙile ta ce "Amin wa alaikassalam" murmusawa yayi, gami da cewa "Aaminat kin shirya ne" "A'a" "saboda me baki shirya ba shida tayi fa" "nifa nace maka babu inda zanje" "Aaminat kiyi haƙuri dan Allah kije in bakije ba bansan yadda zancewa dangi na ba kuma nace musu zaki je" ɗan ƙaramin tsaki tayi, "Aminat dan Allah ki tausaya min kije," "nifa bazani ba ai ba wannan ne Aure na nafar koba kaga ai ba saina wani je ba" wata zazzafar ajiyar zuciya ya sauke tare da rintse ido, sun ɗauki minti yakai biyu babu wanda yayi magana, Yarima ne yayi ta maza yace "shikenan tunda bazaki ba saiki zauna, kiyi abinda kika ga dama tinda ba a'isa dake ba," yana gama faɗin haka ya kashe kiran rai aɓace, dan kuwa Aminat ta fara ɓata mai rai, kusan kwana biyar yana fama da ita amma taƙi yarda,
Aminat kuwa kuka ta ƙara fashewa dashi, dai-dai lokacin Siyama Umaima Iman suka kutso kai ɗakin, turusss sukayi ganin Aaminat ta zage tana ɓarzar kuka, da sauri sukayi kanta suna cewa "maiyafaru??" banza tayi dasu, Umaima ta ce "ya Aminat baki da lafiya ne ko wani abu akayi miki??" cikin kuka tace "babu komai" "to maiya faru kike kuka??" share hawaye tayi tare da cewa "Yarima ne wai sainnaje gurin Dinner kuma ni banason zuwa" sheƙewa sukayi da dariya ta saki baki tana kallon su, Simaya ta ce "amma kin bani dariya, akan haka kika zauna kina ta kuka sai kace wadda akace za'a kashe" Aaminat ta shiga goge hawayen gami da cewa "kukan ma baza'a bar mutum yayi mai daɗi ba, sai an takura masa" "iyeeee kukan ma hada mai daɗi ko???" tsaki tayi taja ƙaton bargo ta rufa, wayar ta ce ta fara kuwwa ya duba mai kiran da mamakin ta sai taga wata number ba irin ta ƙasar nan ba, saida ta kusa yankewa sannan ta ɗauka, tare da sallama, amsawa yayi, cikin nutsuwa ya ce "maiyasa bazakije wajen shagalin bkinki ba" wani dummmm taji zuciyar ta tayi, adiririce ta ce "A...a...a....Abdul kaine" "nine Yaya dan Allah kiyi mana alfarma kije dan Allah" tana dariya dariya kuka kuka ta ce "to zani amma bazan daɗe ba, Abdul ka dawo don Allah" "to kitashi kishirya kuma dan Allah ki daina wahalarmin Aminina bana jin daɗin hakan, idan lokacin dawowata ya yi zan dawo" wasu sabbin hawaye ne suka fara sabuwar zarya akan tausasan kumatunta, ta ce "to zan daina" "to Allah ya sanya alkairi ya kauda fitina amma kin ɓatawa Abubakar rai kikira sa ki bashi haƙuri" "to" ta ce daga haka sukayi sallama,
Umaima ta kalli Aaminat ta ce "gaskiya ki rage abinda kikewa yaya Abubakar gobe iyanzu fa kina gidan sa," "nima dai haka nagani haka kawai saita dinga tsangwamar bawan Allah" Aaminat kuwa banda cokalo baki babu abinda take, Ameeera ce ta shigo tana cewa "ga mai kwalliyar nan ta ƙaraso", "to ki ƙaraso da ita nan ɗaki" Iman ta faɗa Siyama ta kalli Aaminat, cikin sanyin murya ta ce "kije kiyi wanka lokaci yana ja", tashi Aaminat tayi ta shiga wanka,
bata jima ba ta fito daga wankan, zama tayi akan ƴar ƙaramar kujera, ta fara shafa mayuka masu ƙamshi da tsada, tin kafin ayi mata kwalliyar ta ɗau harama don kuwa ta sha gyara, fatarta ta yi suɓula sai ƙyalli da walƙiya take ta yi wani ɓulɓul, tana gamawa "Umaima ta kalli mai kwalliyar ta ce kije ki fara yimata", Aaminat ta ce "nifa ba saianyi mini Make-up ba" "ai kuwa dolenki ayi tunjiya kike faman wahalar da mutane dan iskanci, komai akace saiki ce ke bazakiyi ba to dole sai anyi kwalliyar nan" "yauwa maman Humaira tin ɗazu take ta butsewa taƙi yarda" wadda aka kira da maman Humaira ta ƙara ɗaure fuska babu alamun wasa, ta ce "maza ki farayi mata,"... ta makawa Aaminat harara ta ce "idan kika kuskura nadawo na tarar, baki zauna anyi miki ba sainayi rugu-rugu dake ja'ira" tana gama faɗin haka ta juya ta ficewar ta,
dan dole aka fara yiwa Aaminat Make-up anayi tana butsarewa, ko ta cokalo baki gaba tana mita,,
Fati ta shirya cikin tsadadden Leshi marun doguwar riga gown sai walwali take tayi kyau sosai san kowa ƙin wanda ya rasa, cikin yauƙi da yanga da jinkanta, take takawa har suka isa kofar gida inda aka aje motar ango da abokansa, kofar maya aka buɗe mata ta shiga, Direban ya fara jan motar a hankali suka ɗauki hanya,
cikin ɗan lokaci aka gama Make-up ɗin Aaminat wata riga Umaima ta miƙo mata, ta ce "kiyi kisa" batare da tace komai ba ta karɓi rigar ta fara sawa, Dogowar riga ce Baƙa da yarfin golden, mai irin buguzum ɗin nan irin ta indiawa, tayi mata mugun kyau tamkar wata sarauniyar kyawa-wa, takalmi golden tasa da wata ƴar ƙaramar jaka mai ƙyalli da sheƙi, wani ɗan ƙaramin mayafi, Siyama ta miƙo mata, ta karɓa ta yana a saman kanta, Iman da Umaima suka ɗauki wasu tsadaddun turaruka masu mugun ƙarfi da ƙamshi suka fara fesa mata kamar bazasu daina ba, Siyama ce ta kama hannunta cikin sanyi ta ce "muje ko" tirjewa tayi taƙi ta fiya, Siyama ta saita dai-dai kunnan ta ta ce "Aaminat kiyi haƙuri ki bamu haɗin kai dan Allah, karkiyi gardama," wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke,, sannan ta fara ɗaga ƙafar ta cikin nutsuwa, ahankali take takawa, kamar mai tsoron takawa, a haka suka isa babban ɗakin da Umma take ita da ƴan uwan ta da sauran mutane, suna shiga ɗakin ya kaure da buɗa, ahankali ta ƙarasa inda Umma take, kai ta kifa akan cinyar Umma, Umma ta shafa bayanta ta ce "Aaminat Allah yayi miki albarka ta shi kuje" ƙin tashi tayi saida Umaima ta kama hannun ta ya ɗagata, bayan anyi kamu, suka nufi ƙofar fita,
Aharabar gidan suka tsaya, inda wata jibgegeyar mota mai tadar gaske take Baƙa ce motar daganin motar kasan ba ta ƙanana mutane bace, wani kyak-kyawan saurayi ne ya buɗe ƙofar baya, kasan cewar duhu ya farayi hakan yasa bata lura da mutu ko babu ba ta shiga motar cikin nutsuwa, ahankali ta rufe murfin ƙofar, sannan ya zagaya ya shiga mazaunin Direba, su Siyama ma tasu motar suka shiga,, cikin nutsuwa Direban ya fara jan motar suka fita daga get ɗin gidan, saida suka hau titi, sannan Aaminat taji motsin mutum akusa da ita, matsawa tayi, gefe, wani ni'imtaccen murmushi ya saki, tare da lumshe ido, waya ya ɗauko ya kunna fitilar wayar, ya haska Aaminat yana wani tattausan murmushi, cikin nutsuwa ya kai hannun sa ya yaye gelen da ta rufe fuskarta, hawaye ne shaɓe-shaɓe kwance afuskarta, cikin tattausar muryarsa mai daɗin sauraro ya ce "sorry ki daina kuka, banason ganin zubar hawayen ki," wani numfashi taje ta sauke tare da, sauke nannauyar ajiyar zuciya, wani maraitaccen murmushi ya sakar mata, sannan ya miƙo mata tissue, ya ce kishare hawayan ki bana son ganin ki kina kuka dan Allah ki daina karki sa kanki ciwon kai,..." ya numfasa kafin ya ce "Aaminat dan Allah ki karɓa ki shara hawayan ki, kidaina kuka karki ɓata kwalliyarki," ƙin kaɓa tayi saima wasu hawayen da suke ƙara shararowa, cikin nutsuwa, Yarima ya fara share mata hawayen yana hura mata iska da bakin sa, hakan yasa ta fara jera ajiyar zuciya akai-akai, gyaran muryar da Sabir yayi ce ta dawo da Yarima cikin hayyacin sa,, Sabir ya kwashe da dariya gami da cewa "ya Abubakar dama ka iya soyyaya haka,???" tsaki Yarima yayi ya ce "kai ina wasa da kai???" "A'a wallahi salon nakane yake matsa ni" "kai Sabir ka fiya sa ido, dama hankalin ka yana kanmu ka saki tuƙin ko??" ƴar dariya yayi ya ce "ai dama shiyasa nace ni zan jaku" "ai kuwa idan na ƙarajin tarinka saina..." muryar Aaminat ce ta katse masa magana, jin tana cewa "kun isheni da surutu" murmusawa yayi ya ce "ranki ya daɗe tuba muke, mun daina" shiru tayi batace komai ba hakan yasa suma sukaja nasu bakunan suka tsuke,
Æan garen su Fati kuwa suna isa aka fara cashewa ana rawa kamar ba gobe,