Sashe 41
Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Idanunsa ƙir a kaina fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce. "Welcome Madam, ban san sunan da zan ba wa ranar yau ba saboda tsananin farincikin da nake ciki." Ban ba shi amsa ba har sai da na zauna na rufo motar sannan na ce. "Ya na ji muryarka a dashe? Ba dai mura ce ta kama mini kai ba?" Ya ce. "Ita ce mana, wannan zirga-zirgar da na yi ce ta saka." Na ce. "Sannu Allah ya ƙara sauƙi." Ya ce. "Amin ya rabb, ashe Camera rage miki kyau take yi, a fili kin fi kyau sosai." Fari na yi masa da ido na ce. "Kai ma haka ai, Ina yini? Ko gaisawa ba ka bari mun yi ba." Ya ce. "Ana ta kai wa yake ta kaya? Gabaɗaya ni kin ruɗa ni ne ai, gaskiya dole na samu wata gwaggwaɓar kyauta na yi wa Maman Nasmah, saboda haɗa ni da tauraruwar matan da ta yi." Na yi dariya kawai ina ƙare masa kallo, ƙamshinsa mai daɗi da sanyin AC na ratsa ni.
Mun daɗe muna hira, da zai tafi ya raka ni har bakin soro, ya ce na kira Inna ya gaishe ta, bayan sun gaisa ya ba ta kuɗi, ni ma da zai wuce ya ba ni bandir ɗin ƴan ɗari biyar. Da murna Inna ta rungume ni bayan na koma, tana dariya ta ce. "Yanzu kika yi miji, ai irin waɗannan kullum su muke addu'a da fatan ku samu, rabon arziƙi ne ya sa kika baro gidan wancan matsolon." Na ce. "Haka ni ma na ce, amma ni Inna Kawu kawai nake ji, don shi Alhajin ya ce ba ya so bikinmu ya kai azumi." Dafa kafaɗata ta yi ta ce. "Kwantar da hankalinki, saboda yanzun nan ma na kira shi na ce masa a nan za ki kwana, gobe da kaina zan je na yi masa bayani, na gama shirya duk abin da zan ce masa, ke ma anjima zan faɗa miki, yadda bakinmu ba zai zama biyu ba, yanzu bari na siyo mana tsire mu ci, wancan tuwon a ba wa almajirai shi kawai." Ina murmushi na ce. "To Gwaggo sai kin dawo."
Kusan raba dare muka yi muna tsara yadda abubuwa za su kasance, ni kuwa zuciyata fes na yi amanna da duk ƙaryar da Inna za ta faɗa wa Kawu, don ko ban yi bincike akan Mansur ba na san ba zaɓan tumin dare ba ne, saboda na yi amanna Maman Nasmah ba za ta taɓa haɗa ni da wanda ba ta aminta da shi ba.
Washegari wajen ƙarfe goma muka koma gida tare da Inna, bayan mun gaisa da Kawu na shige ciki na bar su tare, cikin raina ina addu'ar Allah ya sa kar ya ba mu matsala a cikin auren nan, don na san halinsa tsaf zai ce a'a idan ya ji irin kuɗin da Alhaji Mansur yake da shi. A tsanake Inna ta dubi Kawu ta ce. "Ɗan'lami magana nake tafe da ita mai muhimmanci fa." Kawu ya ce. "To ina sauraren ki Yaya Habi." Ta ce. "Yawwa, yarinyar nan Hafsah jiya da ta je wani ƙanin mijin maƙociyarmu ya gan ta ya ce yana so, babban mutum ne mai hankali da kowa yake yabon shi, matarsa ce ta rasu shekara ɗaya da suka wuce, bai sake aure ba har yanzu kuma bai taɓa haihuwa ba." Gyara zama sosai Kawu ya yi ya ce. "A ina yake? Mene ne kuma sana'arsa?" Inna Habi ta ce. "Ɗan kasuwa ne, sauran bayani kuma idan ya zo duk zai yi maka da bakinsa, don shi a yadda muka yi magana jiya a ƙage yake, kafin azumi yake son a yi komai idan mai duka ya nufa." Jinjina kai ya yi ya ce. "Amma Yaya kamar ya yi kusa yarinyar nan ta sake aure kafin azumi, don har yanzu tana cikin damuwar mutuwar wancan auren nata, da bari muka yi ta huta sosai, radadi da zafin abun ya bar cikin ranta." Da sauri Inna ta ce. "Wanne hutu kuma? Ai ba ta buƙatar wani hutu, idan ta yi auren ai shi ne abin zai fi saurin barin cikin ranta ta manta da wani Anas, kai dai kawai ka yi mata addu'a, ƙila rabon wasu ƴaƴan da ba na wancan ba ne ya fito da ita. Kuma ita ma fa ta amince da na yi mata magana." Kawu ya ce. "Hafsan da kanta?" Ta ce. "Ita fa." Numfashi ya sauke ya ce. "To Allah ya tabbatar mana da alkhairi, ki ce ya zo mu zanta, idan har ta amince da shi kuma ba shi da wani aibu da za a hana shi aure shikenan, sai a yi." Cikin farinciki ta ce. "Yawwa, ko kai fa, ai ita bazawa ba a buƙatar yin jinkiri a lamarin aurenta."
Da Inna ta sanar mini yadda suka yi ba ƙaramin murna na yi ba, a lokacin Kawu ya kira ki ya tambaye ni zan iya yin aure yanzu? Kuma ina son wanda Inna ta zo masa da batunsa? Tun kafin ya gan shi gara ya ji ra'ayina. Kaina a ƙasa na amsa da na amince. Ya yi mana addu'a tare da fatan alkhairi.
A ɗokance na kira Alhaji Mansur bayan na koma cikin gida na ce. "Kawu ya ce duk lokacin da ka shirya ka zo yana son ganin ka." Muryarsa ɗauke da farinciki ya ce. "Kai amma na ji daɗi, Alhamdulillah! Ai ni a shirye nake, anjima da daddare in sha Allahu zan zo." Ina murmushi na ce. "Sai ka zo, zan sanar masa, amma don Allah zan roƙe ka wata alfarma." Ya ce. "Faɗi kanki tsaye darling." Na ce. "Yawwa, idan ka zo gurin Kawu don Allah kar ka ba shi ko taro har ku tafi, hakan zai fi sakawa ya fi amincewa da kai." Murmushi ya yi mai sauti ya ce. "Shikenan, duk da abin yana da matuƙar wahala a gurina, don ni ban san me ya sa ba hannu har ƙaiƙayi yake wajen yin kyauta, bare kuma Babana guda na je har gabansa na kasa ba shi kuɗi, anya zan iya kuwa?" A shagwaɓe na ce. "Please my Man." Cikin marairacewa ya ce. "Ya zan yi, yadda kika ce ai haka za a yi." Na ce. "Yawwa thank you."
Inna Habi ce ta sanar wa Kawu zuwan Alhaji Mansur Idonnera, har dare kuma ba ta tafi ba, ta ce sai sun zo ta ji yadda aka yi. Gwaggo dai da ido kawai take bin mu.
Kamar yadda ya alƙawarta bayan isha'i suka zo, na ce masa su shiga soron kawai, don kunya nake ji na tsallake Kawu da sunan na fita zance. Hakan ya sa har suka tafi ba mu haɗu ba, sai waya muka yi ya mun sallama, yana ta yabon yadda Kawu ya tarɓe su. Shi ma Kawun yabon nasu ya yi ta yi, ina jin shi yana cewa Inna. "Ma sha Allah, yaron akwai tarin ilimin addini sosai, magana da komai nasa cikin nutsuwa da ilimi yake yi." Washe baki ta yi ta ce. "Ka gani ba, ka ga abin da nake faɗa maka ai." Ya ce. "Na gani kam, yanzu mun gama magana na ce ya turo manyansa neman izini kafin ta fara fita gurin shi, sai su fahimci juna." Inna ta ce. "Hakan ya yi, Allah ya tabbatar mana da alkhairi." Ya ce. "Amin ya hayyu ya ƙayyum."
Mun daɗe muna hira, da zai tafi ya raka ni har bakin soro, ya ce na kira Inna ya gaishe ta, bayan sun gaisa ya ba ta kuɗi, ni ma da zai wuce ya ba ni bandir ɗin ƴan ɗari biyar. Da murna Inna ta rungume ni bayan na koma, tana dariya ta ce. "Yanzu kika yi miji, ai irin waɗannan kullum su muke addu'a da fatan ku samu, rabon arziƙi ne ya sa kika baro gidan wancan matsolon." Na ce. "Haka ni ma na ce, amma ni Inna Kawu kawai nake ji, don shi Alhajin ya ce ba ya so bikinmu ya kai azumi." Dafa kafaɗata ta yi ta ce. "Kwantar da hankalinki, saboda yanzun nan ma na kira shi na ce masa a nan za ki kwana, gobe da kaina zan je na yi masa bayani, na gama shirya duk abin da zan ce masa, ke ma anjima zan faɗa miki, yadda bakinmu ba zai zama biyu ba, yanzu bari na siyo mana tsire mu ci, wancan tuwon a ba wa almajirai shi kawai." Ina murmushi na ce. "To Gwaggo sai kin dawo."
Kusan raba dare muka yi muna tsara yadda abubuwa za su kasance, ni kuwa zuciyata fes na yi amanna da duk ƙaryar da Inna za ta faɗa wa Kawu, don ko ban yi bincike akan Mansur ba na san ba zaɓan tumin dare ba ne, saboda na yi amanna Maman Nasmah ba za ta taɓa haɗa ni da wanda ba ta aminta da shi ba.
Washegari wajen ƙarfe goma muka koma gida tare da Inna, bayan mun gaisa da Kawu na shige ciki na bar su tare, cikin raina ina addu'ar Allah ya sa kar ya ba mu matsala a cikin auren nan, don na san halinsa tsaf zai ce a'a idan ya ji irin kuɗin da Alhaji Mansur yake da shi. A tsanake Inna ta dubi Kawu ta ce. "Ɗan'lami magana nake tafe da ita mai muhimmanci fa." Kawu ya ce. "To ina sauraren ki Yaya Habi." Ta ce. "Yawwa, yarinyar nan Hafsah jiya da ta je wani ƙanin mijin maƙociyarmu ya gan ta ya ce yana so, babban mutum ne mai hankali da kowa yake yabon shi, matarsa ce ta rasu shekara ɗaya da suka wuce, bai sake aure ba har yanzu kuma bai taɓa haihuwa ba." Gyara zama sosai Kawu ya yi ya ce. "A ina yake? Mene ne kuma sana'arsa?" Inna Habi ta ce. "Ɗan kasuwa ne, sauran bayani kuma idan ya zo duk zai yi maka da bakinsa, don shi a yadda muka yi magana jiya a ƙage yake, kafin azumi yake son a yi komai idan mai duka ya nufa." Jinjina kai ya yi ya ce. "Amma Yaya kamar ya yi kusa yarinyar nan ta sake aure kafin azumi, don har yanzu tana cikin damuwar mutuwar wancan auren nata, da bari muka yi ta huta sosai, radadi da zafin abun ya bar cikin ranta." Da sauri Inna ta ce. "Wanne hutu kuma? Ai ba ta buƙatar wani hutu, idan ta yi auren ai shi ne abin zai fi saurin barin cikin ranta ta manta da wani Anas, kai dai kawai ka yi mata addu'a, ƙila rabon wasu ƴaƴan da ba na wancan ba ne ya fito da ita. Kuma ita ma fa ta amince da na yi mata magana." Kawu ya ce. "Hafsan da kanta?" Ta ce. "Ita fa." Numfashi ya sauke ya ce. "To Allah ya tabbatar mana da alkhairi, ki ce ya zo mu zanta, idan har ta amince da shi kuma ba shi da wani aibu da za a hana shi aure shikenan, sai a yi." Cikin farinciki ta ce. "Yawwa, ko kai fa, ai ita bazawa ba a buƙatar yin jinkiri a lamarin aurenta."
Da Inna ta sanar mini yadda suka yi ba ƙaramin murna na yi ba, a lokacin Kawu ya kira ki ya tambaye ni zan iya yin aure yanzu? Kuma ina son wanda Inna ta zo masa da batunsa? Tun kafin ya gan shi gara ya ji ra'ayina. Kaina a ƙasa na amsa da na amince. Ya yi mana addu'a tare da fatan alkhairi.
A ɗokance na kira Alhaji Mansur bayan na koma cikin gida na ce. "Kawu ya ce duk lokacin da ka shirya ka zo yana son ganin ka." Muryarsa ɗauke da farinciki ya ce. "Kai amma na ji daɗi, Alhamdulillah! Ai ni a shirye nake, anjima da daddare in sha Allahu zan zo." Ina murmushi na ce. "Sai ka zo, zan sanar masa, amma don Allah zan roƙe ka wata alfarma." Ya ce. "Faɗi kanki tsaye darling." Na ce. "Yawwa, idan ka zo gurin Kawu don Allah kar ka ba shi ko taro har ku tafi, hakan zai fi sakawa ya fi amincewa da kai." Murmushi ya yi mai sauti ya ce. "Shikenan, duk da abin yana da matuƙar wahala a gurina, don ni ban san me ya sa ba hannu har ƙaiƙayi yake wajen yin kyauta, bare kuma Babana guda na je har gabansa na kasa ba shi kuɗi, anya zan iya kuwa?" A shagwaɓe na ce. "Please my Man." Cikin marairacewa ya ce. "Ya zan yi, yadda kika ce ai haka za a yi." Na ce. "Yawwa thank you."
Inna Habi ce ta sanar wa Kawu zuwan Alhaji Mansur Idonnera, har dare kuma ba ta tafi ba, ta ce sai sun zo ta ji yadda aka yi. Gwaggo dai da ido kawai take bin mu.
Kamar yadda ya alƙawarta bayan isha'i suka zo, na ce masa su shiga soron kawai, don kunya nake ji na tsallake Kawu da sunan na fita zance. Hakan ya sa har suka tafi ba mu haɗu ba, sai waya muka yi ya mun sallama, yana ta yabon yadda Kawu ya tarɓe su. Shi ma Kawun yabon nasu ya yi ta yi, ina jin shi yana cewa Inna. "Ma sha Allah, yaron akwai tarin ilimin addini sosai, magana da komai nasa cikin nutsuwa da ilimi yake yi." Washe baki ta yi ta ce. "Ka gani ba, ka ga abin da nake faɗa maka ai." Ya ce. "Na gani kam, yanzu mun gama magana na ce ya turo manyansa neman izini kafin ta fara fita gurin shi, sai su fahimci juna." Inna ta ce. "Hakan ya yi, Allah ya tabbatar mana da alkhairi." Ya ce. "Amin ya hayyu ya ƙayyum."