← Book details Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 54

Sashe 14

Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Washegari na tashi cikin tsananin farinciki mara misaltuwa, ni kaɗai na dinga sakin murmushi ina imagining rawa da murnar da zan yi idan saƙon da Maman Nasmah ta ce za ta kawo mini ya ƙaraso. Ga ni nake kamar a mafarki, idan na tuna wai har da sarƙar gold za ta haɗo mun, sarƙa fa? Ba ma ɗan'kunne ko zobe ba. Gaskiya watan arziƙina ne ya tsaya. Na dinga kallon kaina ina hasaso ni sanye da ɗanƙareriyar sarƙa tana zuba walwali.
Ƙarfe bakwai na safe na ga ta mun text na address ɗin gidan mai gyaran jikin, ta ce na je ƙarfe tara tana jira na. Cikin zumuɗi na koma parlour inda Anas yake shirya su Sultan na zauna a kan kujera, fuskata ba yabo ba fallasa na ce. "Abban Sultan zan fara zuwa gyaran jiki yau, na ga fatata duk ta yanƙwane." Kallo na ya yi cikin mamaki sannan ya ce wa Sultan. "Ɗauki abincin naku ku je ɗakinku ku ci." Suka amsa tare ɗauka suka fice suna satar kallo na. Anas ya maido da hankalinsa gare ni tare da faɗin. "Ina jin ki, ban gane me kike nufi ba?" Kaina tsaye na ce. "Cewa na yi zan je gyaran jiki anjima, za a yi mini na sati ɗaya." Cikin rashin fahimta ya ce. "Wai wanne irin gyaran jiki? Da ma kina zuwa ne ban sani ba? Har yanzu ban fahimce ki ba Hafsah?" Cikin hasala na ce. "Da Hausa fa nake yi maka maganar nan, gyaran jiki dai wanda ake yi wa mata su yi kyau fatarsu tai ta sheƙi da fitar da ƙamshi, da kake tambaya kuma da ina yi, ba na yi, yanzu zan fara." Wani kallo da ban taɓa ganin ya yi mini irinsa ba ya wurga mini tare da faɗin. "Shi ne kuma sai a yau ɗin za ki je za ki faɗa mun? To ban shirya ba gaskiya." Tsaki na ja a cikin raina na ce. 'Sarkin tsiya aminin talauci, to ba cewa zan yi ka ba ni kuɗin ba.'
"Ba kai za ka biya ba ai, ni zan biya da kaina." Na faÉ—i haka ina huhhura hanci.
"A ina kika samu kuÉ—in?"
"Allah ne ya ba ni."
"To ba za ki je ba." Ya faɗa a fusace tare miƙewa ya bar mini parlour'n.
Da wani matsiyacin kallo na raka shi, ƙwafa na ja na miƙe kamar zan kifa na ɗauko wayata na kira Maman Nasmah, ringing biyu ta ɗaga, muryarta da alamun bacci ta ce. "Kin ga saƙona kenan?" Na ce. "Eh, ki yi haƙuri na tashe ki a bacci." Ta ce. "Ba komai, Kin tambayi mijin naki?" Na ce. "Hmm." Tare da faɗa mata duk yadda muka yi da shi. Cikin kwakwazo ta ce. "Wannan miji naki ba dai baƙar zuciya ba wallahi, ni fa tunda na gan shi yana yi miki wani murmushin gefen baki na san mugu ne, ban da haka mene na hana ki wani fita?" Kamar zan yi kuka na ce. "Kulle ne da shi da ma, ko bayani ban gama yi masa ba ya tashi ya bar ni, in dai ba tare za mu fita ba bai fiya bari na fita ba, wai shi kishi."
"Kin gani ba, muguntar kenan ai, shi yana fita yana watayawa kullum amma ke yana barin ki a gida a dunkume, saboda kar ki fita ki....." Jin motsin shi na yi saurin katse da faÉ—in. "Ina zuwa, ga shi nan." Ban jira amsar ta ba na datse kiran.
Murmushin mugunta Maman Nasmah ta yi ta ce. "Jaka, haka zan ta zura ki na kai ki na baro, miji irin naki ai abin so ne, mai kishin iyalinsa da tsare mutuncinsu, ban da mahaukaciya ce ke da ma wanne mijin arziƙi ne za ka ce masa za ka fara fita wani gyaran jiki rana tsaka ya bar ka? In sha Allahu kafin taron nan sai na yi sanadin da zai miki ko saki ɗaya ne, daga nan na fara plan B ɗina." Ta lumshe idonta tare da rungume pillown da yake ƙirjinta, wani irin son Anas sabo na fizgar ta, mutumin da ko sunansa ba ta sani ba, amma soyayyar shi ta mata mugun gamu, saboda yadda tunaninsa ya addabe ta ko lokacin yin wasu abubuwan ba ta samu yi ba a daren jiya, raba dare ta yi tana ta juyi a gado tare da hasaso irin soyayyar da take fatan su yi. Tana ganin ɗaya daga cikin mazan da take hulɗa su yana ta kiran ta amma ta ƙi ɗagawa, domin daga lokacin da ta yi tozali da Anas duk mazan duniya suka koma mata tamkar mata ƴan'uwanta, shi kaɗai take gani a Namiji. Fatanta kawai Allah ya sa mijinta ya dawo a cikin satin nan, ta rura masa wuta ya ba ta takardarta, ta yi ta yi ta gama iddarta a ɗaura mata aure da masoyinta. Komai take yi fuskarsa kawai take gani a cikin idanuwanta da murmushin da yake yi wa Hafsah. Numfashi ta sauke tare da mirginawa tana murmushi ta ce. "Ina son ka sosai mijin Hafsah Maman Sultan a yanzu, nan gaba kaɗan kuma mijin Hafsat Maman kyawawan ƴaƴan da za ta haifa maka masu kama da kai."
Chapter 14 · 0% Book details