Sashe 20
Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
ce. "Haba, mene na godiya, ai na faÉ—a miki tamkar Æ´ar'uwata ta jini haka na É—auke ki, don haka babu godiya a tsakaninmu, abin da nake so da ke kawai duk wani abu da ya shige miki duhu ki faÉ—a mini zan ba ki shawara in sha Allah." Na ce. "Na gode, zan kira ki anjima na faÉ—a miki duk yadda muka yi da shi." Ta ce. "Allah ya kai mu, ina Æ™ara jaddada miki dai kar ki raga masa fa, ki buÉ—e masa wuta ya fito miki da kayanki." Na ce. "In sha Allahu." Tare da kashe wayar na yi cilli da ita cikin Æ™unar zuci kamar ita ce Anas É—in. Wani irin tafarfasa da turirin bala'i ne kawai yake kai kawo a cikinta. Maganganun Maman Nasmah sun yi zaman kafaffen rodi a cikin zuciyata, na yi amanna da yarda da su É—ari bisa É—ari, don a yanzu ko tantama ba na yi Abban Sultan ne ya sace mini kayana. Rasa inda zan saka kaina na ji daÉ—i na yi, na dinga safa da marwa daga tsakar gida zuwa É—aki kamar zautacciya, filin zuciyata cike da tanadin tulin buhunhunan tijara da rashin mutuncin da zan zazzage a kan Anas. Ina bakin Æ™ofar soro na haÉ—a kaina da bango na ji an buÉ—e Æ™ofar gidan an shigo, kamar wadda ta ga abin tsoro haka na É—ago kaina da sauri na bi shi da mugun kallo, ban amsa sallamar da ya yi ba na fara magana cikin É—aga murya. "Ina kayana? Kar ka ce mini komai kawai ka fito mun da kayana." Sororo ya yi yana kallo na cikin rashin fahimta, fuskarsa É—auke da maÉ—aukakin mamaki ya ce. "Rashin kayan ne ya zautar da ke haka kike sunbatu marasa kan gado?" A fusace na ce. "Idan akwai abin da ya fi mahaukaciya ka kira ni da shi ma Anas bai dame ni ba, abin da na sani kawai wallahi sai ka dawo mun da abuna, ka je duk inda ka kai ma ko ka siyar da ka sata ka karÉ“o k...." "Sata kuma? Ni kike alaÆ™antawa da sata yau? Me zan yi miki da kayanki? Me za su Æ™are ni da shi?" Ya yi maganar yana nuna kansa cikin É“acin rai. ÆŠage kafaÉ—a na yi na ce. "Oho maka, ka na tsammanin ba zan gane kai ba ne ka sata? Daga ni sai kai a gidan idan ba kai ba wa zai É—auka?" Girgiza kai ya yi cikin takaici ya ce. "Wallahi Hafsah inda kika ajiye kayanki ma ban sani ba bare na É—auka, rantsuwa ba É—abi'ata ba ce kin sani, amma na rantse miki da zatin Allah ba ni na É—aukar miki kayanki ba, ki dai tuna ko kin cilla su wani gurin kin manta, ban da haka wa zai É—aukar miki? Wa ma ya shigo gidan?" "Kai mana!" Na faÉ—a ina zabga masa harara. Numfashi ya sauke ya ce. "Da farko na É—auka da wasa kike da kika nuna kike zargi, amma yanzu ban ga alamar hakan a tattare da ke ba, ban taÉ“a tunanin akwai ranar da za ta zo a rayuwarmu ki alaÆ™anta ni da sata ba, kin fi kowa sani na da abin da zan aikata da wanda ba zan yi ba, ban san me na yi miki ba Hafsah kika zaÉ“i ki ta É“ata mini rai, kar ki kai ni bango na yanke hukuncin da duk ba zai mana daÉ—i ba." Baki na taÉ“e na ce. "An yi walÆ™iya na ga duk wasu mugayen halinka da a da son ka ya rufe mini ido ba na gani, don haka ko me za ka yi ka daÉ—e ba ka yi ba, Æ™arÆ™ari ka ce za ka sake ni ko? To idan ba ka sani ba ma ka sani shi na fi buÆ™ata a yanzu, don in na rabu da kai wanda ya fi ka komai da komai zan aura." Taune leÉ“ensa ya yi yana hucin É“acin rai ya ce. "HuÉ—ubar da suke yi miki kenan?" Na ce. "Oho maka, ni dai yanzu ba dogon surutu na nema ba, kawai ka fito mini da kayana, don ba ka siya mini ba, ba ka isa ka É—auke wanda aka ba ni ba wallahi." Ya ce. "Sai ki yi ta yi, Allah ne shaidata kuma shi zai bayyana gaskiya." Cikin zaÆ™alÆ™ala na riÆ™e Æ™ugu na ce. "Aikin banza, gayyar tsiya kawai da rashin zuciyata, ban da mugun hali babu abin da mutum ya iya, ko da yake an ce gado ba karambani ba ai, tunda ba ka tashi ka ga ana yi a gidanku ba ai kai ma ba ka yi a gidanka ba." Cak ya tsaya daga Æ™oÆ™arin shiga É—akin da yake, ya juyo ya zuba mini idanunsa da suka yi jajir É—in bacin rai, muryarsa na rawa ya ce. "Hafsah! Me kike nufi?" Ba tare da tsoro ko dogon nazarin sakamakon da maganata za ta janyo ba na ce. "Abin da yake akwai shi nake nufi, wanda ya kasa riÆ™e É—ansa ya turo shi almajiranci ta yaya zai iya kula da matarsa har ya yi mata duk abin da take so? Ka ga kenan ba a Æ™asa ka É—auka ba." Jikinsa har tsuma yake saboda tsananin fushi da É“acin rai, don da farko na É—auka duka ne zai yi idan ya Æ™araso inda nake, amma sai na ga ya kama hannayena ya damÆ™e a cikin nasa, muryarsa kamar mai shirin fashewa da kuka ya ce. "Cin mutuncin har da iyayena da suke Æ™asa Hafsah? Kar ki fara don Allah! Kar ki fara abin da zuciyata ba za ta É—auka ba wato sako iyayena a cikin sabgar mu, don ba zan jure ba, zuciyata za ta iya tunzura ni na aikata abin da ban yi niyya ba, kar ki bari mu yi asarar juna saboda wasu can da ba ki san su ba, ba ki san da alkhairi suke nufin ki ko da sharri ba. Please na roÆ™e ki ko dan su Sultan, ina son ki, ban shirya rabuwa da ke. Kuma kar ki manta yanzu igiyar aurenmu saura biyu, furucin da na yi a baya na idan kika fita a bakin aurenki ya riga ya tabbata saboda kin fitan, na shiga tashin hankali a sanadin hakan, amma ke na ga ko a jikinki, to don girman Allah kar ki bari saura biyun ma su tsinke mana." Dogon tsaki na ja tare da fizge hannuna, ko kaÉ—an ban ji tausayinsa ko kuma na ji kalamansa sun ratsa ni ba, sai ma wani irin haushin shi da ya Æ™ara rufe ni, musamman da na tuno gobe ne taronmu, kuma shi nake zargi da sace abubuwan da za su saka na zama tauraruwa a taron, da kuma baÆ™incikin Æ™in siyo mini wayar da ya yi, alhalin matan group É—inmu komai suke so mazajensu suna yi musu cikin gaggawa. Ga uwa uba huÉ—ubar Maman Nasmah, da ta dinga jaddada mini na tabbatar na matuÆ™ar É“ata masa rai, ya ji babu daÉ—i shi ma kamar yadda na ji. Cikin son Æ™ara Æ™ona masa rai na ce. "Ai da ma wanzami ba ya son jarfa, to tunda ba ka so in dinga taÉ“a maka Iyaye, ka sake ni na je na auri wanda zai so ni, ya gatanta ni, ya yi mini duk abin da nake so a duniya, mai kuÉ—i ba faÆ™iri irinka ba." Bai ce komai ba ya juya kamar zai tashi sama alamun ba ya son ci gaba da jin maganganun da nake yi. Jikinsa sai kyarmar tsantsar É“acin rai yake. Da sauri na bi bayansa na riÆ™o rigarsa, cikin fitsara na ce. "Na gaji! Na gaji da wannan takaicin naka! Ka sawwaÆ™e mini idan ka cika É—an halak a cikin Binta da Musa!" Ban san lokacin da ya juyo ba sai ji kawai na yi ya É—auke ni da wani wawan mari da ya saka ni kifawa. Da sauri na dafe kuncina tare da É—aga kaina na kalle shi ina hawaye. Sai na ga shi ma nasa idanun da suka kaÉ—a suka yi jajir cike suke da Æ™walla, muryarsa a dashe saboda tsananin tashin hankali da É“acin rai ya ce. "Ki je na sake ki Hafsah!".......âœï¸