Sashe 34
Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
gata a duniyar nan bayan Ubangijin da ya halicce ki sama da Anas ba." Cikin Æ™osasa da surutunta na ce. "Shi gatan ne da shi? Yanda ba ni da kowa shi ma hakan yake." Tana gyara zaman jakarta a kafaÉ—arta ta ce. "Shi namiji ne, ba shi da matsalar neman matallafi a rayuwa kamar ke, zai iya yin rayuwarsa shi kaÉ—ai ma a cikin gidansa, amma ke kuwa a matsayinki na mace dole sai kina Æ™arÆ™ashin wani!" Tsaki na kuma ja ban tanka mata ba. Ta ce. "Hmm, Hafsah kenan, yau ni kike wa haka akan wasu can haÉ—uwar jiya-jiya?" Na ce. "Na yi É—in, hurumin da ba naki ba da kika shiga shi ya janyo miki." Ta ce. "Haka ne, kowa rai ya yi wa daÉ—i babu kamar mai shi, in sha Allah daga yau ba zan Æ™ara yi miki magana akan wannan rayuwar da kika É—aukar wa kanki ba." Cikin kora da hali na ce. "Ya fi miki alkhairi, ki sakar mini mara ki bar ni na yi rayuwata yadda na ga dama." Sallama ta mun ta tafi bayan ta Æ™ara yi mini bitar maganganunta da kwata-kwata ba su da mazauni a gurina, don tamkar amahin shata haka na É—auke su. Ban da Æ™ona mini rai ma babu abin da suke yi. Na fara yarda da maganar Maman Nasmah da ta ce hassada da baÆ™incikin mu'amalata da Æ´an gayu take yi. Wunin yau cikin tufka da warwara na yi shi, don ko girkin rana ban yi ba, na jiÆ™a wa su Sufyan garin kwaki suka sha suka wuce islamiyya. Da suka dawo kuma na ba su ragowar abincin da suka ci da safe, na ce musu idan uban nasu ya dawo ya nemo musu abin da za su ci da daddare ko ya dafa musu. Ni kuma na ci biscuit É—in da na siya da yawa na ajiye saboda da irin haka, na kora da ruwa. Daf da Magriba na É—auko bola na wargatsa a tsakar gida da soro, na É—ebi ruwa na kwara a kai. Da kaina na fita Æ™ofar gida na É—ebo Æ™asa na tila akai. Na yi hakan ne saboda Anas, don na san ba Æ™aramin É“aci ransa zai yi ba idan ya zo ya tarar da gidan a haka, saboda ba ya son Æ™azanta ko kaÉ—an a rayuwarsa, ga shi da Æ™yanÆ™yami, kuma kafin ya fita sai da ya share gidan tas. Toilet kuwa da Sufyan ya yi bayangida hana shi flushing na yi, na Æ™ara damalmala bakin masan na bar shi a haka, duk saboda ya gani ransa ya É“aci. Da Æ™yar Sultan ya iya yin alwala, sai kakkame jikinsa yake ya na É“ata fuska cikin Æ™yanÆ™yami. Sufyan kuma ya na fitowa daga É—aki ya kama bakinsa ya ce. "Mami wa ya yi mana wannan Æ™azantar a gida?" Na ce. "Ban sani ba don ubanka." Jijjiga kai ya yi yana keÉ“e baki ya ce. "TaÉ“, idan Abba ya dawo zai yi faÉ—a, ki yi sauri ki gyara kar ya zo ya gani." Ban kuma tanka masa har ya Æ™araci surutunsa ya yi shiru, Sultan kuwa da ya san ni na yi bai ce komai ba. Bayan ya idar da alwalar ya É—auko tsintsiya zai fara shara na Æ™wace na kora shi waje. Tare da suka dawo da Baban nasu, ina daga É—akin su Sultan na ji yana cewa. "Mene wannan kuma a gidan kamar kwata ?" Daga nan ban san ya aka yi ba sai ji na yi ya faÉ—i tim a cikin cakwalin. Da sauri na fito na haske shi, ganin shi na yi kwance male-male, Æ™oÆ™arin tashi ya yi cikin hanzari, ban san lokacin da wata irin dariya ta Æ™wace mini ba, saboda tozalin da na yi da fuskarsa ta yi dagaje-dagaje da ruwa da Æ™asa da bolar da na zubar.........âœï¸