Sashe 38
Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
turo mini. Amma sai na ga lambar Anas ce. Ban san me ya sa ba na ji zuciyata ta doka, jikina na mazari na buÉ—e amma sai na ga babu komai, ba abin da aka rubuta. Umarnin kiran shi zuciyata ta ba ni, bijire mata na yi cikin takaicin yadda na damu, cikin haushi na ja tsaki tare da taÉ“e baki ina faÉ—in. "Goge lambarsa ma zan yi, kar zamanta a cikin wayata ya shafa mini salalan tsiyar talauci." Bayan Azhar na karÉ“o wayata daga chaji na ga an kikkira ni da baÆ™uwar number har two missed call. Bin bayan kiran na yi, tana shiga na ji an katse an kira. Kafin na yi magana na ji wata irin murya mai sanyi da kamewa ta yi sallama. Amsawa na yi tare da faÉ—in. "Wa ke magana?" Bai amsa ba ya ce. "Da fatan ina magana da tauraruwa mai hasken da ya haskake zuciyata tun kafin na gan ta a zahiri?" Shiru na yi ina maimaita kalamansa a cikin raina, sai da ya Æ™ara magana sannan na ce. "Ai gabaÉ—aya ka sani a duhu ne, har na fara tunanin ko wrong number ka kira." Murmushi ya yi mai sauti wanda na ji shi har cikin kaina ya ce. "Ai zuciya ba ta taÉ“a mistake akan dukkanin abu mai muhimmanci a gare ta, ke ce wadda nake nema Hafsah." Ya yi shiru na wasu sakanni alamar ba ya iya dogon zance sannan ya ci gaba da magana. "Sunana Mansur Ibrahim Idonnera, Æ™awarki takwararki ce ta ba ni numbernki, tunda ta tura mini hotunki na gani na rasa sukunina gabaÉ—aya, tun lokacin har yanzu ina kwance ina ta tunaninki ne kawai, sai yanzu da kika É—aga na ji wannan zazzaÆ™ar muryar taki na ji na fara samun nutsuwa." Ƙaƙƙarfar ajiyar na sauke, da ma ina ta addu'a Allah ya sa shi ne wanda Maman Nasmah ta ce za ta haÉ—a mu, don muryarsa kaÉ—ai ta tabbatar da yanayinsa, yadda yake magana a kasalance yana jan numfashi ba Æ™aramin burge ni ya yi ba, daga ji babu tambaya jiÆ™aƙƙe a can Æ™asan tekun kuÉ—aÉ—e, ga sunansa kuma da ya Æ™ara tabbatar mini da haka. Murmushi na yi tare da kwanciya don wayar ta fi armashi na ce. "Duk wannan yabon ni kaÉ—ai?" Ya ce. "Kin fi gaban haka ma zinariyar mata, yanzu dai ki sanar mini na karÉ“u ko sai na Æ™ara zage damtse kar zuciyata ta buga." Siririyar dariya na saki tare da Æ™anÆ™ame wayar ban ce komai ba. "Dariya mai daÉ—i da saka nishaÉ—i." Ya faÉ—a Æ™asa-Æ™asa kamar mai raÉ—a. Hakan ya haifar mini da tashin tsigar jiki. Lumshe idona na yi na ce. "Idan akwai abin da ya fi karÉ“uwa ma ka yi shi a gurina." Ya ce. "Wow, thank you, dole na bayar da tukuicin amsar nan." Murmushi na yi na ce. "Ai kai ne tukuicin." Ya ce. "Bayan ni ma akwai buÆ™atar wani, ki tura mini account number É—inki na saka mini tukuicin, ko kuma ki faÉ—a mini wani abun da kike so na saka a kawo miki." Cikin jin daÉ—i na ce. "Na gode, amma account É—ina ba ya aiki yanzu." Don ba zan ce ban da shi gabaÉ—aya ba ya raina ni." Ya ce. "Zinariya guda ba account kuma nake zaune, bari na kira wani na haÉ—a ku, sai ki je bank É—insu ya buÉ—e miki duk lokacin da kike so, ni yanzu ba na Nigeria ne amma da ni zan zo na kai ki da kaina." Na ce. "Babu komai, hakan ma ni ce da godiya." Daga haka muka yi sallama bayan ya ce zai tura mini kati. Ina ta rawar murna na samu irin mijin da nake so message ya shigo wayata, ina dubawa na ga credit ne na 20k, murza idona na yi don Æ™ara tabbatarwa ko shi ne bai ganar mini daidai ba, amma still haka na gani. Waro ido na yi na yi tare da dafe Æ™irjina na ce. "Katin dubu ashirin? Katin waya na kira kawai!" GabaÉ—aya sai na ruÉ—e na susuce, na kira Maman Nasmah na sanar mata ba ta É—aga ba. Sai na hau online na shiga chat É—inmu, na ga ta tuttura mini hotunan Mansur, cikin azarÉ“aÉ“i na buÉ—e cike da matsuwar son ganin yadda kamanninsa da komai nasa za su kasance........âœï¸