← Book details Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 54

Sashe 3

Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Saukar da idona na yi a kan wardrobe ɗinmu, wadda na san a irin gidansu Maman Fa'iz ko a ɗakin mai gadi ba za a saka irinta ba. Komawa na yi na kwanta, saboda tsabar tunani kaina har wani juya mini yake yi. A lokacin Anas ya shigo ɗakin bakinsa ɗauke da sallama, na amsa masa ciki-ciki. Bai damu ba ya dube ni cikin kulawa tare da faɗin. "Ya kika kwanta kuma ba ki saki net ba? Duk da akwai Nepa ai sauro yana yawo." Na ce. "Zan saki ne." Yana sakin net ɗin ya ce. "Kin je kin tofa wa su Sultan addu'a ne?" Cikin ƙosawa da maganar tasa na ce. "Eh." Ya ce. "To bari na kakkashe ƙwaiƙwaye na zo mu yi magana, don wannan yanayin da kike ciki na san ba ƙalau ba my love." Baki kawai na taɓe ban ce komai ba, ya gama abin da zai yi ya hawo kan gadon ya ja ni jikinsa ya ce. "Don girman Allah ki faɗa mini abin da yake damun ki, wallahi ganin ki a haka gabaɗaya ya hautsina zuciyata." Na ce. "Ba komai fa, ka yi baccinka kawai." Ƙasa ya yi da murya kamar kodayaushe idan yana rarrashi na ya ce. "Ba ma haka da ke, kar mu fara a yau, kin san babu yadda za a yi na iya yin bacci kina cikin ɓacin rai, ko kun samu saɓani da wani ne ta waya? Na ga da tana hannunki kina ta tsaki." Hararar shi na yi na ce. "Ko ɗaya, tunda na ce maka babu komai ka ƙyale ni mana!" Shiru ya yi kawai, duk da duhu ne amma na san kallo na ya tsaya yana yi. Barin jikinsa na yi na koma can ƙarshen gado ina jan tsaki a cikin zuciyata. Don ni gabaɗaya gani nake shi ne matsalata, da ya zo a mai kuɗi ai da yanzu ba na cikin fargabar fita kunya a cikin group ɗinmu. Ina jin shi yana sassauke numfashi na yi banza da shi. Na san abu biyu ne ya haɗar masa, baƙon halin da na tsiro da shi da kuma tabbacin rashin samun haɗin kaina da zai yi idan ya buƙace ni, don ba ƙaramin tanadi ya yi wa wannan daren ba, saboda yau da safe na yi wankan tsarkin hailar da na yi kwanaki biyar ina yi, tun kafin ya fita yake ɗoki, da rana ma da ya muka yi wayar da muka saba yi kullum idan ya fita sai da ya yi mini zancen. Na ɗauka ya haƙura amma sai na tsinkayi muryarsa a raunane yana faɗin. "Shikenan Hafsah tunda haka kika zaɓa, ba zan takura ki dole sai kin faɗa mini abin da yake faruwa ba tunda kin ɓoye, amma don Allah ki daina bayyana ɓacin ranki, kin fi kowa sanin yadda hakan yake taɓa ni sosai ya kuma sanya ni a cikin damuwa, ba ki ji yadda nake ji a cikin raina ba, gabaɗaya na rasa nutsuwata, don Allah ki yi mini wannan alfarmar." Ture tausayinsa dake ƙoƙarin mamaye ni na yi na ce. "Shikenan, in sha Allah zan yi hakan." Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi tare da faɗin. "Na gode tawan, Allah ya yi miki albarka ya ji ƙan Umma, ya raya mana su Sultan, ya kawo ƙannensu dozen masu albarka." Ya ƙarashe maganar cikin sigar tsokana. A daƙike na ce. "Amin." Ban yi niyyar tanka masa ba, amma don ya ƙyale ni na samu na yi tunanin sama wa kaina mafita na biye masa muka yi magana. Sai dai abin da nake so ɗin bai samu ba, don jin shi kawai na yi a jikina a maimakon na ga yana shirin yin bacci. 'Mutum sai jarabar tsiya amma ba ko sisi.' Na faɗi haka a cikin raina cikin takaici da haushin shi da yake ƙara cika mini zuciya.......✍️
Chapter 3 · 0% Book details