Sashe 17
Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ko sama da Æ™asa za su haÉ—e ba zan auri talaka ba. Ga shi ana ta tagged É—ina ana cewa ni ina nawa abubuwan? Rashin abin cewa ya sa ba na yi musu reply. Duk wata tijara da rashin mutunci babu wadda ban yi wa Abban Sultan ba akan Æ™in siyo mini wayar da ya yi, na daina aikin komai a gidan, tsakani na da su Sufyan sai hantara da zagi, musamman idan yana gidan, amma duk da haka ko É—aga kai bai taÉ“a yi ya kalle ni ba bare ya tanka, duk da ina ganin tsantsar É“acin rai a kan fuskarsa. Yau ya kama saura kwana biyu taronmu, da daddare bayan na dawo daga gidan gyaran jiki ina zaune a gefen gado ina kallon fatata yadda ta yi wani irin kyau da sheÆ™i abun gwanin burgewa. Kallon yadda jikina ya koma kaÉ—ai ya na saka ni a cikin matuÆ™ar nishaÉ—i. Kiran Maman Nasmah ne ya shigo wayata, da murmushi na É—aga tare da yin sallama, bayan ta amsa na ce. "Ya shirye-shirye?" Ta ce. "Shirye-shirye Alhamdulillah, ai mu mun gama komai, rana kawai muke jira." Na ce. "Masha Allah, Allah ya nuna mana wannan rana dai da rai da lafiya, mu sha shagali mu mori bidirin tanadin da aka yi mata." Ta ce. "Amin, amma dai ya kawo miki wayar?" Na ce. "Hmm, ina fa! Ai da Æ™yar ya siya mini, ko tanka ni ba ya yi fa." Ta ce. "TaÉ“, kowa kuwa da sabuwar waya zai je gurin nan, daga mai ta million sai mai ta sama da haka, ke kaÉ—ai ce za ki tashi da jagwal." Cikin yaÆ™e na ce. "In sha Allah ni ma da sabuwa zan zo, bari ya dawo gidan." Ta ce. "Allah ya sa, ki san dai duk yadda za ki yi ya siya miki atou." Na ce. "In sha Allah." Daga haka muka yi sallama ta kashe wayar. MiÆ™ewa na yi na fara zarya a É—akin, ina tunanin hanyar da zan bi na samu waya mai tsada irinta Æ´an group É—inmu, na Æ™ulla na Æ™unce amma ban da wata hanya sai Anas É—in dai. Citson yatsa na yi na ce. "Oh Allah, ni Hafsah wacce Æ™addara ce ta kai ni auren mara zuciyar da ba zai iya nemo kuÉ—in da zai wadata ni da shi ba? Ya mayar da ni zarra a cikin mata ni ma kamar su Maman Nasmah." Tsaki na ja na koma na zauna tare da rafka tagumi. A haka ya dawo ya same ni, na tarÉ“e shi da kallon banza tare da jan dogon tsaki. Bayan ya rage kayan jikinsa ya na Æ™oÆ™arin barin É—akin na yi tsalle na sha gabansa, ina bin shi da wulaÆ™antaccen kallo na ce. "Anas don Allah wai kai wanne irin mutum ne? Ko babu zuciya a Æ™irjinka ne da za ka yi amfani da ita ka nemo kuÉ—i a duk inda suke ka yi mini abin da nake da muraÉ—i?" Numfashi ya sauke tare da Æ™oÆ™arin raÉ“awa ta gefena ya fita amma na Æ™ara tare hanyar, ina hawaye na ce. "Wai mahaukaciya ka mayar da ni a gidan nan ne da sai nai ta maka magana ka Æ™i Kula Ni?" "To ai ba ki da maraba da ita." Ya faÉ—a fuskarsa ba yabo ba fallasa. Bai jira amsata ba ya ci gaba da magana da faÉ—in. "Duk abin da za ki yi da cin mutuncin da za ki mun na yi wa kaina alÆ™awarin ba zan kula ki ba, bare na biye miki, har ki yi ki gama." Ƙugu na riÆ™e a harzuÆ™e na ce. "Ai ban da ranar ganawa idan har ba za ka yi mini abin da nake so ba, na gaji da zama sai dai na ga a yi wa wasu abubuwa ni ba a min, alhalin su ma mazajen nasu mutane ne kamar kai, ba fin ka suka yi da komai ba, abin da suke yi suke samun kuÉ—i kai ma za ka iya." Girgiza kai ya yi cikin tsantsar takaici ya ce."Allah ya ganar da ke Hafsah, amma ba zan gajiya da yi miki wannan addu'ar ba." Ina Æ™oÆ™arin Æ™ara yin wata maganar ya hankaÉ—e ni ya fice, Æ™wafa na yi na koma na zauna ina jijjiga jiki. Sabbin wayoyi da motocin da Æ´an group É—inmu suka tutturo mazajensu sun siya musu sai gizo suke mun a cikin kaina, babban abin da ya fi É—aga mini hankali yadda duk wadda ta turo abu wani sashi na gidanta ya fito sai na gan shi haÉ—aÉ—É—e ginin zamani, wani parking space ma kaÉ—ai sai a saka gidana a ciki ya zauna har da ragowa. GabaÉ—aya Anas da duk wata kyautatawa, kulawa da soyayyar da yake min sun fice mini a rai, rayuwar gidan kuÉ—i da jin daÉ—i kawai nake hange. Na tabbata yadda nake kwana da wuni da tunanin ranar da mafarkina zai zama gaske idan aka auna jinina ba Æ™aramin hawa za a ga ya yi ba. Duk yadda na so mu yi fitina da Anas a daren nan amma ya Æ™i biye mini, Æ™arshe ma ficewa ya yi ya bar mini É—akin ya koma nasu Sultan. Da Asuba ina tashi na É—ora daga inda na tsaya, na dinga watsi da kayan É—akina ina jifan shi da shi, tare da gasa masa duk maganar da ta fito daga bakina. Don hankalina a matuÆ™ar tashe yake na ganin har ana i gobe taronmu amma ban mallaki sabuwar waya ba, kuma kamar yadda Maman Nasmah ta faÉ—a duk kyawun da zan yi a gurin, da tsadar kayan da zan saka a banza za su tashi idan ban da rantsatstsiyar waya, saboda akwai video da za a yi mana wanda kowa zai É—aga wayarsa a ciki, so ake mu tashi kan media a taron nan namu, ai ta yawo da videos da pictures É—inmu, mu zama topic of discussion a ranar, shi ya sa aka ce kowacce ta sako gold. Don haka duk rintsi duk wahala ba zan bari na zamo takashin baya ba, dole duk abin da za a yi ya zamto ina gaba-gaba. Yau idan na je gidan gyaran jiki shi ne za a mun lalle, amma saboda zullumin rashin waya ya sa har 8 ta wuce ban fara shirin tafiya ba. Ina kwance ina aikin kallon hotunan wayoyin da fiye da rabin Æ´an group É—in suka turo a tsakanin shekaran jiya da jiya Abban Sultan ya shigo É—akin. Kamar an tsikare ni na tashi zaune na dirga daga kan gadon a haukace na je gabansa na haska masa rakwaÉ“aɓɓen screen É—in wayata na ce. "Kalli yadda ake abin arziÆ™i, kalli irin wayoyin da mazajen wasu suka sissiya musu, ni kam Anas anya ka na so na kuwa? Gobe ne abin nan amma ka fitar da ni kunya abu ya gagara." TankwaÉ“ar da wayar ya yi ya ce. "Ban taÉ“a sanin ba ki da hankali ba Hafsah sai yanzu, kin taÉ“a ganin mutum ba shi da gashin wance ya ce sai ya yi irin kitsonta? Kin san kuÉ—in da mazajen nasu suke da shi ne?" Ina huci na ce. "Ai ba da kuÉ—in suka zo duniya ba, nema suka yi, kai ma sai ka fita ka nemo a duk inda suke." Murmushin takaici ya yi ya ce. "Kin yi nisa my love, ba za ki taÉ“a jin kira ba, abu É—aya nake fata shi ne Allah ya sa ki je ki ga mazajen nasu ba su da wani abu da suke nema ido rufe, wanda ni kuma ina da shi, na san daga nan za ki dawo cikin hayyacinki." WulaÆ™antaccen kallo na bi shi da shi, ina keÉ“e fuska kamar na ga kashi na ce. "Har akwai wani abu da talaka yake da shi da mai arziÆ™i zai rasa? Ai kuÉ—i babu abin da ba sa samar wa mutum a duniya." Girgiza kai ya yi ya ce. "Kamar yadda Ubangiji yake raba arziÆ™i ga wanda ya so haka yake raba lafiya da sauran baiwa ga bayinsa, don ka na da kuÉ—i bai zama lallai ka na da lafiya ko kuma wani abu mai muhimmanci a rayuwarka ba, na san ba za ki taÉ“a gane duk wani abu da zan faÉ—a miki ba a yanzu, balle ki yarda da ni, saboda nausawar da kika yi a cikin wani tunani na banza da wofi. Shi ya sa na tattara ki na watsar na zuba miki ido ki yi duk abin da za ki yi ki gama, zan dai ci gaba da yi miki addu'ar Ubangiji ya ganar da ke cikin gaggawa." Wawan tsaki na ja tare da galla masa harara, ina jin kamar na kikkifa masa mari. Bai ko kalle ni ba ya É—auki abin da zai É—auka ya fice. Rashin sanin abin yi ya sa na tafi inda na ajiye kayan da Maman Nasmah ta ba ni don na É—auka na tasa su a gaba na kalla kamar yadda nake yi kullum ko zan ji sanyi a raina. Sai dai me? Neman duniya babu wanda ban yi ba amma babu su babu alamar su, gabaÉ—aya na Æ™ara hargitsa É—akin, na yi wa komai filla-filla, amma ko alamar abu mai kama da su ban gani ba. A haukace na fita parlour ina sharce zufa na duba amma nan ma babu, kitchen, toilet, É—akin su Sultan, soro babu inda ban duba ba amma ban gan su ba, har bokitin da nake zuba shara sai da na zazzage a Æ™asa na duba. Amma kaya suka ce É—auke mu inda kika ajiye....âœï¸