← Book details Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 54

Sashe 15

Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Ido na bi shi da shi bayan ya shigo ɗakin, cikin tsoron ko ya ji wayar da nake yi, don babu abin da ya tsana a rayuwarsa sama da wani abu ya faru a tsakaninmu na faɗa wa wani, mutum ne shi mai son sirri sosai. Shi ya sa tun da muke da shi bai taɓa kai ƙara ta gida ba da sunan na yi masa wani laifin. Yana cire jallabiyar jikinsa na ƙarasa kusa da shi fuska a murtuke na ce. "Wai don Allah Anas me ya sa kake mun irin wannan abubuwan ne? Akan me za ka hana ni zuwa gyaran jikin nan?" Ba tare da ya kalle ni ba ya ce. "Saboda na isa." Kallon sama da ƙasa na yi masa na ce. "Yanzu kai ba abin jin daɗinka ba ne zan je a gyara ni?" Ya ce. "Ba shi ne damuwata ba, inda kika samo kuɗin zuwan nake son sani." A wulaƙance na ce. "Oh, saboda ga ƴar matsiyata dangin matalauta ko? Wadda wani nawa ba zai iya ba ni kuɗi ba." Kallon takaici kawai ya mun ya juya ya fita, na bi shi da harara. Kiran Maman Nasmah na ƙara yi na faɗa mata komai. Cikin faɗa ta ce. "Wai wannan mijin naki shi ne autan maza ne da kike ta lallaɓa shi haka? Maman Sultan kar dai ki ce mini ke ma mata kika rako duniya?" Na ce. "Ban gane ba?" Ta ce. "Ai ba za ki gane ba, ni kawai ki faɗa mini idan gyaran jikin ne ba kya so na saka ta dawo mini da kuɗina." Cikin rawar baki na ce. "Wallahi ina so, kawai ban san fita ba da izninsa ba ne." Ta ce. "To sannu doluwa, idan akan maganar kuɗi ne ki ce masa ƙawarki ce kuka haɗu a social media ta ba ki, ba shikenan ba ya ji abin da yake so?" Shiru na yi, don na san hakan ma wata sabuwar fitinar ce. Fahimtar hakan ya sa Maman Nasmah ta ce. "Ko me zai yi ki faɗa masa haka, don maza ba a yi musu lako-lako, ni ban ma taɓa ganin mace mai tsoron miji irinki ba ko a labari, ko a cikin group ɗinmu ai za ki ga kowacce tana faɗa watayawarta take yi son ranta a gidanta, ke kaɗai ce fa kike cikin wannan rayuwar ƙuncin, ki zage ki ƙwatarwa kanki ƴanci, idan ba haka ba taron ma hana ki zuwa zai yi. Don haka duk abin da zai ce ki yi ficewarki, kar ki raga masa, ba a raga wa maza yanzu ko kaɗan." Cikin rashin mafita na ce "Toh shikenan." Daga haka muka yi sallama. Zama na yi ina bitar maganganun Maman Nasmah, tabbas duk abin da ta faɗa gaskiya ne, su da mazajensu ma suke hamshaƙan masu kuɗi ba sa tsoron su sai ni matar talaka. Yanda matan group ɗinmu suke watayawarsu abin ba ƙaramin burge ni yake ba, sai na ji suna cewa duk inda suke so zuwa suke. Don haka ni ma daga yanzu na ɗaura ɗamarar yin duk abin da na ga dama, na daina shayin Anas, bari ya dawo daga kai su Sultan school, zan nuna masa wargi ce ni daidai ƙugunsa. Da wannan tunanin na tashi na fara shirin tafiya gidan mai gyaran jikin. Har na sha tea ɗin da ya tafasa da bread na yi wanka bai dawo ba. Ina cikin shiryawa ya shigo, sai da kammala komai na ɗauki jakata da mayafi na nufi ƙofa fuskata a murtuke, ba tare na ce masa ƙala ba.
"Babu inda za ki je fa wallahi Hafsah." Ya faɗa yana tare hanya. A haƙiƙance na ce. "Wai saboda me? Idan kuɗin ne dole sai ka ji wa ya ba ni to ƙawata ce da ta zo jiya." Yana ƙara babbake hanya ya ce. "A ina take? Mene ne alaƙarki da ita?" Kaina tsaye na ce. "A group na Whatsapp muka haɗu." Cikin matsanancin ɓacin rai ya ce. "Ban san ta ba, ban san irinta ba, ban san wace ce ita ba, ba zai yiwu haka kawai ta ɗauki kuɗi ta ba ki ni kuma na bar ki, ki yi amfani da shi ba, don haka ki mayar mata da abinta!" A zazafe na mayar masa da raddi da faɗin. "Wallahi ba zan mayar ba, kai ba ka ba ni ba, ita da yake mijinta mai zuciya ne da son faranta wa iyalinsa ya ba ta har ta sammun a ciki sannan kuma ka ce na mayar saboda mutunta? Su mazansu ga kuɗi ga ba matsi, sai kai talaka ne za ka hana ni rawar gaban hantsi? To wallahi bari ka ji Anas, ban ga abin da zai hana ni zuwa gyaran jikin nan ba, saboda taro za mu yi a group ɗinmu, kowacce mijinta ya ba ta kuɗi don ta fito fes sai ni ce zan tafi a duƙun-duƙun? To ba zai yiwu ba." Na ƙarashe maganar kamar zan kai masa duka, zugar Maman Nasmah na ƙara tunzura ni na ci gaba da faffaɗa masa maganganu ya gane ba na tsoron shi a yanzu, amma na danne na ƙyale shi haka ba don halin shi ba. Tsananin mamaki da al'ajabi su suka saka Anas sandarewa a tsaye, ya kasa ƙwaƙƙwaran motsi, hakan ya ba ni damar raɓawa ta gefen shi na fice. Na kai tsakiyar tsakar gida na ji muryarsa cikin matsanancin ɓacin ran da ban taɓa jin shi a cikinsa ba, don muryarsa har rawa take yana faɗin. "Wallahi! Wallahi! Wallahi idan kika ɗaga ƙafa kika fita daga gidan nan a bakin aurenki!".......✍️

*Zeey Kumurya*✍️
[3/8, 1:38 PM] Bahaushiya👍: *YI WA KAI*

*BRIGH PENS*
(FREE BATCH)

10.

Cak na tsaya kamar an kafe ni, don furucin a bakin aurenki da ya yi ba ƙaramin dukan zuciyata ya yi ba. Kamar na koma na fasa fitar, amma sai na ji ba zan iya ba, hakan ya sa kawai na ci gaba da tafiyata ba tare da na waiga ba, duk da na ji motsin fitowarsa tsakar gidan. Idan akwai abin da nake da tabbaci cikakke a kansa to shi ne son da Anas yake mini, na san ba zai taɓa iya rabuwa da ni ba, wannan maganar tasa ma ya yi ta ne kawai a matsayin hargagi, amma na san ba har cikin zuciyarsa take ba. Idan ma har cikin ran nasa ne matsalar shi ce ba tawa ba, don kamar yadda Maman Nasmah ta faɗa idan ina nuna ba na tsoron shi sai ya fi shayi na.
Na shafe kusan mintuna talatin kafin na ƙarasa gidan mai gyaran jikin saboda akwai nisa daga unguwarmu, ina zuwa babu ɓata lokaci ta fara gudanar da aikinta, ta na yi tana ba ni labarin kuɗin Maman Nasmah da na mijinta, don akan wannan gyaran jikin nawa ma sai da ta ninka mata kuɗin sau uku akan yadda take yi. Sai na ji ina ma ni ce ake labarin kuɗina da na mijina, na dinga addu'ar Allah ya nuna mini ranar ni ma zan zama irin haka, a dinga labarina da kwatance da ni. Sai yamma lis na baro gidan, matar tana ta yabon kyan fatata, ni kuwa gani nake murnar kuɗin da aka ba ta ne kawai ya sa take ta koɗa ni, babu wani kyan fata da nake da shi kamar yadda Maman Nasmah ta faɗa.
Chapter 15 · 0% Book details