← Book details Moon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 68

Sashe 28

Moon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

NOT EDITED� A hargitse Ohinoyi ya shiga jijjigasa tare da kiran sunansa,amma Deen ko mutsi ba yayi jikinsa gaba ɗaya ya saki ga wata zufa da take karyo masa ta ko ina,Nene kam tuni ta fara kuka sbd bata taɓa ganin yaron nata a cikin Iran wannan hali ba,da ƙyar Ohinoyi yana Deen ya ƙwantar da shi a saman duguwar sofa,ƙasa jurewa yay cikin sauri ya ƙarasa wajan telephone ɗin part ɗin, yana zuwa ya danna wasu lambobi kana ya danna kira,babu jimawa akai answering call ɗin, numfashi ya sauke kafin ya yaja bakinsa yay shiru kamar wanda bashi da abin cewa,jin shirun yay yawa Tiraki faɗin "Allah yaja da ƙwana ya ƙara maka lafiya,how can i help you?" Still Ohinoyi kasa magana yay sai ajjiyar zuciya da yake sauke,chan kuma yay gyaran murya yace "come with Dr yanzo" yana faɗin hakan yay rejecting call ɗin,wajan Deen ya dawo ya zauna kana ya sanya kan Deen saman cinyarsa ya shiga shafa sumar kansa,cikin ƙasa da murya wacce take nuna zallar damuwar da Deen yake ciki yace "what happened to you Besty?what is this? which gril are you talking about? Ko ƴar uban wacece zan baka ita idan harta kasance jinsin mu ce,idan har ta kasance ƙabilar mu ce,babu dalilin da zai sanya naƙi aura maka ita,ko taki ko tasu,ko iyayenta suna so ko basu so tabbas saika malleketa,tunda har zcyarka ta amince da ita,ban taɓa ganin kukan ka ba,ban taɓa ganin rauninka ya bai yana ba,ban taɓa ganin gazawar ka ba,amma yau dalilin soyayyar wata ka sume a jikina, please Besty wake up and tell me wacce kake so,na maka al'ƙawarin zan baka ita, nayi maka wannan al'ƙawarin kuma...,"maganarsa ce ta tsaya sbd jin Muryar Deen yana faɗin "da gaske?zaka aura min ita Besty?"ya faɗa yana lumshe idanunsa, zuciyarsa banda ta fasa babu abinda take,yana jin wani ɗaci a ransa,da sauri Ohinoyi yace "why not Besty?kai ne komai nawa, I'll do anything for you idan har zakai farin ciki,i promise you idan har akan aure kake kuka daga yau kukanka ya tsaya ka dai na yinsa har abada"Deen yana cije lips ɗinsa yay calmly tare da faɗin "sure?" Ohinoyi ya shafa kan Deen yace "i mean my words Besty,so take it easy,bari Dr yazo ya dubaka then we'll talk later" shiru Deen yay kana ya ɗura a saitin zcyarsa wacce take bugawa da ƙarfi, Nene da har lokacin ta kasa magana tana kallon ɗan nata ganin lokaci guda ya birkice kamar ba zakinta ba,lalle soyayya tai masa mugun kamu,wacce mai sa'ar ce ta samu nasarar samu handsome ɗin yaronta haka?ƴar wacece?waye iyayenta?ita harta matsu ta wannan CLASSES BABYN,10lefts Tiraki ya tsaya bakin plat ɗin yana son ai masa iso wajan Ohinoyi, bayan Jakadiya taiwa Ohinoyi bayani ya kalleta yana jinjina kansa, miƙewa tai tare da rusunawa tace "Allah ya ƙara maka yawan rai na Barka lafiya"bai ce mata komai ba,tana zuwa wajan Tiraki ta shaida masa Ohinoyi ya amsa, kai tsaye ya shiga cikin plat ɗin bayan wani matashin saurayi ne ke biye dashi hannunsa riƙe da first-aidbox,suna zuwa suka ƙwanta a ƙasa suna miƙawa Ohinoyi gaisuwa,kai kawai ya jijjiga, miƙewa sukai zaune kana Tiraki yace "Allah ya baka yawan rai da nisan ƙwana, ɗan Magaji jikan magaji,naji kira na amsa" kallonsu gaba ɗaya Ohinoyi yay kafin yay gyaran murya yace "wato Tiraki Ojohiyo (Yarima) ya dawo mana cikin wani yanayi"da sauri Tiraki yakai dubansa ga Deen wanda yake ƙwance idanunsa a lumshe yay lamo jikin Ohinoyi yana sauke numfashi,cikin yaransu yace "yasubuhanallah! Meke faruwa Magaji?meke damunka?"sai kuma ya juya ya kalli saurayin dake bayansa yana kallon Deen yace "zoka dubasa"kayan aikinsa ya fito dashi tare da ƙarasawa inda Deen yake ƙwance ya shiga dubawa,sosai ya tsorata ganin yadda ƙirjinsa ke ɗagawa da ƙarfi, ya shafe tsayin mintinuni kafin ya share zufar dake zubu masa, Tiraki ne ya katse masa shirun ta hanyar faɗin "bamu bayani, meke faruwa da Yarima?" Zama saurayin yay yace "abubuwan suna da yawa,abu na farko ya daɗe yana damunsa,na biyu kuma bai daɗe da kamasa ba,amma illar dake cikin hakan yasa dole a nema masa mafita"shiru sukai na wani lokaci kafin Tiraki yace "Dr Salman ma kake nufi ne?" Dr Salman yace "yana fama da matsanancin feelings mai ƙarfi wanda kuma dab yake dayi masa illah,spam yana danƙare masa a mara hakan yasa yake fama da ciwon ciki haɗi da mara,kuma a zahiri ana son spam ɗin mutum ya dinga tsinkewa yana zuba yayinda zai fitsari ko kuma sha'awarsa ta mutsa, we're all adults to babu abinda zan iya ɓoye maku,mafita ɗaya ce ga Yarima ya kasance da mata,domin dukkan wasu DRUGS baza siyi masa aiki ba,kai ko suna masa zuwa yanzu zasu daina,abu na gaba kuma yana cikin damuwa sosai wacce ta haddasa masa ciwon kai da zazzaɓi mai zafi"kafin wani yay magana Yayinda ta ƙarasu wajan cikin shigar ta ta alfarma,tana ɗan dugara sandan a ƙasa tace "uhm,bana faɗa ba,nace bana faɗa maku ba?ai wannan shiru shirun da Gadanga yake bana banza bane,nace maku aure ya keso kungi yanzu sai ku yarda ai,masifa tana tacin yaro a ciki amma gunƙi fahimta"babu wanda yace mata komai sai Tiraki da yace "ok yanzu mene zakai masa?" Dr Salman yace "aƙwai drugs da za'a bashi bayan yaci abinci sai ya sha,sai kuma injection da zan masa yanzu"da sauri Deen ya buɗe idanunsa jin an ambaci allura,shima Ohinoyi ya kalli Deen kafin yace "dole ka tsaya idan har kana sonta da gske,nasan ai itama baza taso ganinka cikin ciwo ba right? lumshe idanu yay kana ya buɗe, Ohinoyi ya shafa kansa yace "weldone" cikin nutsuwa Dr Salman yay masa allurar ƴar ƙara ya saki sai kuma ya saki Murmushi tare da shafa nipple ɗinsa inda Moon ta cijesa lokacin da Dr Sufyan yake mata allura,cikin zuciyarsa yace "u're right cutie" sallamar Dr Salman sukai,kana Tiraki yay masu sallama tare da nemawa Yarima Deen lafiya,yana fita Ohinoyi ya kalli Deen yace "wacece ita?" ɗan jim Deen yay kafin ya kalli Abban nasa idanunsa na lumshewa sbd allurar ta fara ɗibansa yace "she's is nothing to me Besty,i want to marry her sbd ina son kula da ita akan wani dalili,bata da kowa sai ni,ni ɗaya take kallo matsayin wani jigo nata,ni kaɗai take kallo a matsayin familynta,ko mene ya faru da ita nine SANADI"Nene da tun ɗazo ba tace komai ba ta gyara zamanta tare da faɗin "sorry!i did get you?" Kallonta yay yana haɗiye abinda ya keji kana yace "they're parents..,"sai kuma yay shiru kallon da suke masa yasa shi faɗin "duk sun mutu,na tsince ta ne nima,daga nan kuma na fahimci kashe iyayen akai kuma at anytime za'a iya FARAUTAR rayuwarta, Besty dan Allah ka amince min kada kace a'a"Murmushi Ohinoyi yay kafin yace "can i see her?"da sauri ya zaro tafkekiyar wayarsa iphone 12 max pro ya zare password ɗin kai,kai tsaye ya shiga gallery, ɓangaren camera ya shiga photonan ta suka bai yana masu yawa,na farko Ohinoyi ya fara gani, hannunta riƙe da ice cream zata tsallaka titi,sai kuma cikin girgi,wasu kuma tana ƙwance a gadon tana bacci,har yanzu na kwanciyar ta a asibiti,wani murmushin takaici Ohinoyi yay kafin ya bawa Deen wayar,itama Nene mamaki ne ƙwance a fuskarta,gaba ɗaya tunaninta ya gama bata wata zabgegiyar budurwa Deen ya gani yace yana so amma sai taga saɓanin haka,to mezaiyi da wannan yarinyar?yarinyar dako nono babu a ƙirjinta, kallonta zai tayi?ko kuma RAINONTA ZAIYI? cikin wani irin yanayi ta kalli Deen tace "Besty mene wannan?wannan ƙwailan zaka ɗauka as your wife wow? Are you at of your sense? Huuu kana ji dai abinda Dr ya gama cewa haka zaka dinga zama da wannan yarinyar babu uban da zatai maka?"Ohinoyi yace "wacce ƙabila ce?" Haɗe rai Deen yay yana rufe idanunsa yace "Hausa Fulani"gaba ɗaya suka zaro idanu hadda yayinda wacce take zaune tana jinsu amma ba tace komai ba,fesar da numfashi Ohinoyi yay yace "again?"kai tsaye Deen yace "yeah,wani abu ne dasu?"Murmushi yay yace "nothing jeka ƙwanta" babu tunanin komai Deen ya miƙe yana rangaji ganin zai faɗi yasa Ohinoyi saurin riƙesa tare da kamasa zuwa wani plat dake wannan babban side ɗin,wani haɗaɗɗan part ne wanda tun daga ƙofar part ɗin aka rubuta Yarima plat, faɗin haɗuwar part ɓata baki ne,wanda bai san kan gidan ba idan yaga part sai ya rantse shine part ɗin Sarki,manyan bedroom sukaiwa babban parlour'n ƙawanya, parlour'n yasha kujeru ƴan turkey,ga wata tangamemiyyar cenema,sai wani madaidai cin fridge mai ƙyau,gefe guda kuma ƙaton kitchen ne nagani na faɗa,ko mace albarka,komai na parlour'n white ne,sai ƙyalli parlour'n yake,cikin wani bedroom ya shigar dashi,nan ma ƙaramin parlour ne,shi kuma komai na cikinsa Green ne,an masa ado da kayan ado na sarakai, cikin bedroom ɗin suka shiga nan kuma yafi komai haɗuwa talkma wajansu daban,agoguna wajansu daban,p.cap wajanta da ban,haka parfumes everyday aƙwai wanda yake fesawa da lotion, daga can ɓangaren kuma babban Library ɗinsa ne,wanda aka zuba littafai kala² both sides arabic da boko,daga jikin Library wata farar ƙofa ce mai ƙyau sai sheƙi take,kana buɗewa zaka tadda lambun Deen wanda aka cikasa da flowers da kuma shukar fruit na nau'i daban²,ga wata ƙorama da take gudana, faɗin haɗuwar wajan dai ɓata baki ne, kwanciya yay a saman makeken royal bed ɗin yana sauke numfashi, suit ɗin jikinsa Ohinoyi ya zare tare da zare masa dugun wandon,ya cire masa talkmansa,duk ya ajjiye gefe guda,ƙura masa idanu yay yana jin wani abu a ransa,sauke numfashi yay kana ya durƙosa ya bashi wani peak a forehead ɗinsa,fita yay bayan ya ƙara masa gudun a.c., Ohinoyi na fita ya nufi plat ɗinsa zuciyarsa babu daɗi ransa kuma ya ɓaci sosai,bai dai nunawa ɗan nasa ba sbd bai son ya fahimci wani abu,shiga yay tare nema wata tattausan kujera ya zauna,babu jimawa Nene ta shigo,tana zama tace "yanzu nasa Jakadiya ta nema min iso wajanka,sai gashi ta dawo tace naje ka amsa,amma wanne kallo kaiwa labarin Yarima,then u'll support him or not?"fesar da numfashi Ohinoyi kafin ya ware manyan idanunsa irin na Deen ya sauke a kanta kamar bai kulata ba sai kuma yace "shi duk inda yaro yake dole sai ya nuna wawta wai?ina da tabbacin Yarima ya sa cewa bama haɗa zuri'a da Hausa Fulani, then yarinyar da yake magana akai is too
Chapter 28 · 0% Book details