Sashe 97
Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wai kai Jabir anya ka ci waec kuwa? Duk bayanin da nake baka ganewa, amma ni babban mamakina bai wuce yadda yarinyar nan take manne da ƙaddarata ba, ita ma an yi garkuwa da ita watannin baya, Bashir ne ya tsinceta a Katsina, a hanyar kai kuɗin fansar aisha, ta zo da ɗankwalin aisha wanda ya ƙara tabattar mini ba ƙarya take yi ba, sai dai duk yadda muka kaɗa muka raya taƙi faɗar komai a kak aisha, kamar tana amfani da hakan ta rama abun da na yi mata ne".
Zamewa jabir yayi ya tsuguna yana maimaita Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Adam kuma yana tsaye yana murza yatsunsa ya na jin yadda hawaye ke cika masa ido.
Sai da Jabir ya gama salallaminsa, sannan ya tashi tsaye, ya dubi Adam ya ce "Yanzu ba lokacin tattauna wata magana ba ce, babu isasshen lokaci, dole a nemo in da aisha take kan kowa ya ji wannan zancen, gashi ka ce sun daina kiranka a kan kuÉ—in fansarta".
Adam ya jinjina masa kai alamar eh.
"Ka ga, maza mu je mota, muje Asibitin".
Haka Adam ya É—auki Jabir suka tafi wurin rumaisa.
A can unguwa kuwa, mama na nan suna ta fama da jinyar rumaisa, amma maganar jaririn nan ta cika gari, kasancewar mama babu wanda suka yi wa bayanin in da rumaisa ta samo jariri, ko a 'yan uwa ba kowane ya sani ba.
Wasu suka din ga cewa ciki rumaisa ta yi, shi ne aka kaita wani wurin ta haihu, dama wannan shegiyar fitinarta ta da rawar kai ta yi yawa, tsaf zata aikata, ba su yi la'akari da irin raunukan da suke jikinta ba, wasu ma cewa suke yi, ba wani saceta da aka yi, rainon ciki ta yi. Ya yin da wani sashen suke cewa gaba É—aya rumaisa ba ta yi kama da wadda ta É—au ciki ta haihu ba, dan a yadda take É—in nan, idan ma cikin ne, abu ne mai wahalar gaske ace ta iya haihuwa da kanta, haka unguwa ta É—auka, wasu suna sukarta, wasu suna bata kariya, sai dai su mama sam basu sani ba, dan ko a gari babu wanda ya iya tarar zaratan samarin nan ya yi musu zancen.
Yanzu ma mama na ta shirin su kwanta, ruma ta sha magungunan ta, tana ta shafa dogon gashin jaririnta, tana kallon dogon hancinsa.
"Meyasa ka yi kama da babanka, dama babarka ka yi kama, da ka fi haka kyau boy na" ta yi maganar tana kissing É—in sa a goshinsa, tana murmushi da jin soyayyar Sabir na shiga zuciyarta.
Yaya Abubakar ya dubeta ya ce "Mama boy, zan tafi gida, gobe in Allah ya kaimu zan biyo mu yi sallama, zan koma school zamu fara exams".
Ruma ta ɓata fuska ta ce "Dan Allah kar ka tafi, bana son ka tafi".
"Ki hi haƙuri, exams ɗin nan ce zata saka na koma, ba dan haka ba a kusa da ke zan kasance in ta kallonki gudan jinina"
Ta yi murmushi ta ce "Allah ya bayar da sa'a"
Mama ta ce "Ka zo ka tafi kar ka yi dare"
"To mama, ban gaji da ganinku bane" kan mama ta yi magana Adam suka shigo.
Ruma ta kawar da kai tana faÉ—in "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" domin ta gaji da ganin takawa, da kullum sai ya zo sau biyu, kuma duk zuwa sai ya É—aga mata hankali a kan ta gaya masa in da Aisha take.
Ba ta ƙara haɗe rai ba sai da ta ga Jabir, sarai ta gane shi, da shi aka haɗa baki Adam ya ɗaukota yayi mata wulaƙanci.
Cikin girmamawa suka gaisa da ammi, yayin da jabir ya ƙurawa rumaisa ido, da ta haɗe rai.
Suka gaisa da Abubakar ma, da yake tsaye yana shirin tafiya.
Mama ta ce "Ana ta ɗawainiya da rumaisa fa, mun gode sosai Allah ya yi albarka, ya shiga lamarin ka ya kareka da ga sharrin maƙiya".
Adam ya ce "Bakomai mama, yi wa kai ne, ki daina godiya ma, addu'a muka fi buƙata"
Rumaisa a ranta ta ce "Ji shi, wai mama sai ka ce babarsu, dan tsabar kuturun iyayi, wallahi mamanmu ce kawai" ta yi maganar a zuciyarta.
Abubakar ya ce "Ruma baki iya gaisuwa bane?"
Ta ɗago ta ce 'Au wai baƙi mama ta yi, sannunku"
"Ya jiki kuwa?" Jabir yayi maganar yana kallon ruma.
"Da sauƙi".
"Ai da yake ban san meyafaru ba, sai yau, shiyasa bamu zo da shi na dubaki ba, mu ga jaririn"
Maimakon ta miƙo shi, sai saka hannu ta dafe shi, tana harare-harare.
Abubakar ya matsa ya ɗauko masa jaririn, ya bashi sannan ya fara yi wa ruma mita "Wai ke wace irin yarinya ce ne? Ke shikenan ba wanda zai taɓa yaron nan sai ke, ke da kece uwassa ban san yadda za'ayi ba".
"To ai nice mamansa, ai dai bar mini shi ta yi".
Ya ce "Ke tafi can, ke ma É—in ai Haryanzu rainonki ake yi, mama bari na wuce na je gida na haÉ—a kayana"
"Yaya Sadik, sai da safe ka gaishe da su"
"Ba yanzu duk suka tafi ba, duk kuna tare sai da safe, ban da yi wa mama rigima dan Allah, a bari sai mun zo mu ayi mana" murmushi ta yi Abubakar ya kama hanya ya fita.
Jabir ya zubawa yaron ido, Adam da ke zaune a gefensa ma, ya zuba masa ido yana saƙa abubuwa daban daban a ransa.
Mama ta juya tana amsa waya, ruma ta lallaɓa a hankali ta sauko daga kan gadonta, ta saka hannu ta ɗauke jaririn daga hannun jabir, a gabansa ta ce "A'uzubi kalaimatillahi tammat" ta ƙarasa gadonta ta kwantar da jaririnta, ta hau gadon tana ta haɗe fuska.
Adam ya É—an kalli jabir, kallon irin ka gani ko?.
Jabir ya girgiza kai ya ce "Rumaisa, na ji duk abun da ya faru, ina fatan Allah ya tsare gaba, amma yakamata ki bayar da haɗin kai wurin kuɓutar da maman yaron nan in dai kina ƙaunar ɗan ta da gaske, da haka zaki tabattar mana son gaskiya ki ke wa ɗan ta".
A wulaƙance rumaisa ta kalli Jabir ta ce "An gaya maka ina abu dan na burge mutane ne? To kar Allah ya sa ku yadda ɗin mana ina ruwana, wataƙila shi sai in gaya masa kai ban gaya maka ba, mugwaye kawai, kuma ni ba dan ta bar mini jaririn nan ba, ba abun da zan yi da ɗan ku, dan ni bana ko ɗaukar yara, idan aka bani riƙon ɗa ma, mintsini yake sha da cizo, wannan kuwa ɗana ne, ba wanda ya isa ya ƙwace mini shi ehe" ta yi maganar tana fari da murguɗa baki".
Jabir ya ce "Kan uba, haka ki ke?"
"Ai na fi haka ma, idan kun gama zaman kwa tafi, ko ku cigaba da zaman jirana in gaya muku in da take, tun da ni na saceta" tana gama maganar ta juya ta kwanta.
Jabir ya riƙe haɓa yana jinjina kai, Adam kuwa tuni ya fusata ya tashi fuuuu ya bar ɗakin, a waje ya tarar da mama yayi mata sallama suka wuce.
A mota Jabir yake cewa Adam "Ban taɓa zaton azabar taurin kan yarinyar nan ya kai haka ba, ji yarinya ƙarama da iya shege".
"Shawarar da bashir ya bayar, ita ce last option ɗina, idan taƙi ba da haɗin kai, zan yi abun da ba ta zato" a haka suka tafi gida suna tattaunawa.
Washegari da safe Ammi ta shirya, zata asibiti Nusaiba da Iman sun so bin ta, amma ta ce a'a su yi haƙuri ba yanzu ba, ta saka aka sheƙa girki, ta saka a mota, tana shirin shiga motar su tafi, ta ji yo muryar Mummy "Giwa, waye Babu lafiya ne na ganki da kulolin abinci da safiyar nan? Ko wani ne a cikin yaran amma ki ke ɓoye mini?"
Ammi mamaki ne ma yakamata, ya aka yi ta fito da sassafe haka, har ta ganta.
'Ba É—aya yara duk suna lafiya, wani abu ne mai muhimmanci" daga haka Ammi ta shige motar, ba tare da sake tanka Mummy ba.
Mummy ta riƙe ƙugu ta jinjina kai ta ce "Lallai ta tabbata akwai abun da ki ke ɓoyewa giwa, kuma da alama yana da muhimmanci a wurinki, bari mu ga idan na bankaɗo ko menene in da zaki saka kanki, zan saka a bi bayanki, domin ganin in da ki ke zuwa"
Rumaisa tana jin zuwan Ammi, suna ta hira ita da mama, amma ta yi bakam kamar bacci take yi, alhalin idonta biyu maganar ce kawai ba ta son yi.
Sai da likita ya shigo, sannan ta tashi suka gaisa da Ammi, likita ya duba X-ray ɗin ta ya ce babu wata matsala, haƙararin nata ma buguwa ce kawai, zai rubuta mata magani.
Mai sunan baba ma tuni sun zo, tare da Abubakar ya biyo yayi musu sallama zai koma makaranta.
Ammi take tambayar mama ko 'yan biyu ne saboda kamanin da suke yi, ba ta gane su, kawai dai ta lura da É—aya yana da fara'a É—aya baya yi.
Mama ta ce "Eh 'yan biyu ne, Abubakar da mai sunan babana, shi ne sa, ba ka dariya sai hamma".
Ammi ta yi murmushi ta ce "Tubarkallah Allah ya ray miki, familynki sun burgeni sosai da sosai, rumaisa a yayyen nan naki ki bani biyu mana, na je na ƙara da nawa yaran mana, ni nawa duk rasuwa suke yi, saura uku a raye"
Mama ta ce "Allah sarki, Allah ya raya wanda suka rage, ya jiƙan wanda suka rasu".
Ammi ta amsa da Amin.
Aka zubawa ruma abinci, Abubakar yana bata a baki, tana ta shagwaɓa.
Bashir yayi sallama, da shi da 'yan sanda huÉ—u cikin uniform.
Ruma ta tsaya cak tana bin su da ido, nan suka gaggaisa da kowa, Ammi ta bi bashir da kallon ko lafiya.
"Maman Boy, ya jiki? Yau zaki ganni da police, su ne case É—in binciken aisha yake hannunsu, dan haka za su yi miki tambayoyi ne" a take rumaisa ta haÉ—e rai, ta kawar da kanta gefe.
Ɗaya daga cikin 'yan sandan ya ce "Baby girl, ki amsa mana tambayoyinmu, zai taimaka mana ƙwarai wurin binciko wanda suka yi garkuwa da ku".
Zamewa jabir yayi ya tsuguna yana maimaita Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Adam kuma yana tsaye yana murza yatsunsa ya na jin yadda hawaye ke cika masa ido.
Sai da Jabir ya gama salallaminsa, sannan ya tashi tsaye, ya dubi Adam ya ce "Yanzu ba lokacin tattauna wata magana ba ce, babu isasshen lokaci, dole a nemo in da aisha take kan kowa ya ji wannan zancen, gashi ka ce sun daina kiranka a kan kuÉ—in fansarta".
Adam ya jinjina masa kai alamar eh.
"Ka ga, maza mu je mota, muje Asibitin".
Haka Adam ya É—auki Jabir suka tafi wurin rumaisa.
A can unguwa kuwa, mama na nan suna ta fama da jinyar rumaisa, amma maganar jaririn nan ta cika gari, kasancewar mama babu wanda suka yi wa bayanin in da rumaisa ta samo jariri, ko a 'yan uwa ba kowane ya sani ba.
Wasu suka din ga cewa ciki rumaisa ta yi, shi ne aka kaita wani wurin ta haihu, dama wannan shegiyar fitinarta ta da rawar kai ta yi yawa, tsaf zata aikata, ba su yi la'akari da irin raunukan da suke jikinta ba, wasu ma cewa suke yi, ba wani saceta da aka yi, rainon ciki ta yi. Ya yin da wani sashen suke cewa gaba É—aya rumaisa ba ta yi kama da wadda ta É—au ciki ta haihu ba, dan a yadda take É—in nan, idan ma cikin ne, abu ne mai wahalar gaske ace ta iya haihuwa da kanta, haka unguwa ta É—auka, wasu suna sukarta, wasu suna bata kariya, sai dai su mama sam basu sani ba, dan ko a gari babu wanda ya iya tarar zaratan samarin nan ya yi musu zancen.
Yanzu ma mama na ta shirin su kwanta, ruma ta sha magungunan ta, tana ta shafa dogon gashin jaririnta, tana kallon dogon hancinsa.
"Meyasa ka yi kama da babanka, dama babarka ka yi kama, da ka fi haka kyau boy na" ta yi maganar tana kissing É—in sa a goshinsa, tana murmushi da jin soyayyar Sabir na shiga zuciyarta.
Yaya Abubakar ya dubeta ya ce "Mama boy, zan tafi gida, gobe in Allah ya kaimu zan biyo mu yi sallama, zan koma school zamu fara exams".
Ruma ta ɓata fuska ta ce "Dan Allah kar ka tafi, bana son ka tafi".
"Ki hi haƙuri, exams ɗin nan ce zata saka na koma, ba dan haka ba a kusa da ke zan kasance in ta kallonki gudan jinina"
Ta yi murmushi ta ce "Allah ya bayar da sa'a"
Mama ta ce "Ka zo ka tafi kar ka yi dare"
"To mama, ban gaji da ganinku bane" kan mama ta yi magana Adam suka shigo.
Ruma ta kawar da kai tana faÉ—in "Innalillahi wa Innalillahi raji'un" domin ta gaji da ganin takawa, da kullum sai ya zo sau biyu, kuma duk zuwa sai ya É—aga mata hankali a kan ta gaya masa in da Aisha take.
Ba ta ƙara haɗe rai ba sai da ta ga Jabir, sarai ta gane shi, da shi aka haɗa baki Adam ya ɗaukota yayi mata wulaƙanci.
Cikin girmamawa suka gaisa da ammi, yayin da jabir ya ƙurawa rumaisa ido, da ta haɗe rai.
Suka gaisa da Abubakar ma, da yake tsaye yana shirin tafiya.
Mama ta ce "Ana ta ɗawainiya da rumaisa fa, mun gode sosai Allah ya yi albarka, ya shiga lamarin ka ya kareka da ga sharrin maƙiya".
Adam ya ce "Bakomai mama, yi wa kai ne, ki daina godiya ma, addu'a muka fi buƙata"
Rumaisa a ranta ta ce "Ji shi, wai mama sai ka ce babarsu, dan tsabar kuturun iyayi, wallahi mamanmu ce kawai" ta yi maganar a zuciyarta.
Abubakar ya ce "Ruma baki iya gaisuwa bane?"
Ta ɗago ta ce 'Au wai baƙi mama ta yi, sannunku"
"Ya jiki kuwa?" Jabir yayi maganar yana kallon ruma.
"Da sauƙi".
"Ai da yake ban san meyafaru ba, sai yau, shiyasa bamu zo da shi na dubaki ba, mu ga jaririn"
Maimakon ta miƙo shi, sai saka hannu ta dafe shi, tana harare-harare.
Abubakar ya matsa ya ɗauko masa jaririn, ya bashi sannan ya fara yi wa ruma mita "Wai ke wace irin yarinya ce ne? Ke shikenan ba wanda zai taɓa yaron nan sai ke, ke da kece uwassa ban san yadda za'ayi ba".
"To ai nice mamansa, ai dai bar mini shi ta yi".
Ya ce "Ke tafi can, ke ma É—in ai Haryanzu rainonki ake yi, mama bari na wuce na je gida na haÉ—a kayana"
"Yaya Sadik, sai da safe ka gaishe da su"
"Ba yanzu duk suka tafi ba, duk kuna tare sai da safe, ban da yi wa mama rigima dan Allah, a bari sai mun zo mu ayi mana" murmushi ta yi Abubakar ya kama hanya ya fita.
Jabir ya zubawa yaron ido, Adam da ke zaune a gefensa ma, ya zuba masa ido yana saƙa abubuwa daban daban a ransa.
Mama ta juya tana amsa waya, ruma ta lallaɓa a hankali ta sauko daga kan gadonta, ta saka hannu ta ɗauke jaririn daga hannun jabir, a gabansa ta ce "A'uzubi kalaimatillahi tammat" ta ƙarasa gadonta ta kwantar da jaririnta, ta hau gadon tana ta haɗe fuska.
Adam ya É—an kalli jabir, kallon irin ka gani ko?.
Jabir ya girgiza kai ya ce "Rumaisa, na ji duk abun da ya faru, ina fatan Allah ya tsare gaba, amma yakamata ki bayar da haɗin kai wurin kuɓutar da maman yaron nan in dai kina ƙaunar ɗan ta da gaske, da haka zaki tabattar mana son gaskiya ki ke wa ɗan ta".
A wulaƙance rumaisa ta kalli Jabir ta ce "An gaya maka ina abu dan na burge mutane ne? To kar Allah ya sa ku yadda ɗin mana ina ruwana, wataƙila shi sai in gaya masa kai ban gaya maka ba, mugwaye kawai, kuma ni ba dan ta bar mini jaririn nan ba, ba abun da zan yi da ɗan ku, dan ni bana ko ɗaukar yara, idan aka bani riƙon ɗa ma, mintsini yake sha da cizo, wannan kuwa ɗana ne, ba wanda ya isa ya ƙwace mini shi ehe" ta yi maganar tana fari da murguɗa baki".
Jabir ya ce "Kan uba, haka ki ke?"
"Ai na fi haka ma, idan kun gama zaman kwa tafi, ko ku cigaba da zaman jirana in gaya muku in da take, tun da ni na saceta" tana gama maganar ta juya ta kwanta.
Jabir ya riƙe haɓa yana jinjina kai, Adam kuwa tuni ya fusata ya tashi fuuuu ya bar ɗakin, a waje ya tarar da mama yayi mata sallama suka wuce.
A mota Jabir yake cewa Adam "Ban taɓa zaton azabar taurin kan yarinyar nan ya kai haka ba, ji yarinya ƙarama da iya shege".
"Shawarar da bashir ya bayar, ita ce last option ɗina, idan taƙi ba da haɗin kai, zan yi abun da ba ta zato" a haka suka tafi gida suna tattaunawa.
Washegari da safe Ammi ta shirya, zata asibiti Nusaiba da Iman sun so bin ta, amma ta ce a'a su yi haƙuri ba yanzu ba, ta saka aka sheƙa girki, ta saka a mota, tana shirin shiga motar su tafi, ta ji yo muryar Mummy "Giwa, waye Babu lafiya ne na ganki da kulolin abinci da safiyar nan? Ko wani ne a cikin yaran amma ki ke ɓoye mini?"
Ammi mamaki ne ma yakamata, ya aka yi ta fito da sassafe haka, har ta ganta.
'Ba É—aya yara duk suna lafiya, wani abu ne mai muhimmanci" daga haka Ammi ta shige motar, ba tare da sake tanka Mummy ba.
Mummy ta riƙe ƙugu ta jinjina kai ta ce "Lallai ta tabbata akwai abun da ki ke ɓoyewa giwa, kuma da alama yana da muhimmanci a wurinki, bari mu ga idan na bankaɗo ko menene in da zaki saka kanki, zan saka a bi bayanki, domin ganin in da ki ke zuwa"
Rumaisa tana jin zuwan Ammi, suna ta hira ita da mama, amma ta yi bakam kamar bacci take yi, alhalin idonta biyu maganar ce kawai ba ta son yi.
Sai da likita ya shigo, sannan ta tashi suka gaisa da Ammi, likita ya duba X-ray ɗin ta ya ce babu wata matsala, haƙararin nata ma buguwa ce kawai, zai rubuta mata magani.
Mai sunan baba ma tuni sun zo, tare da Abubakar ya biyo yayi musu sallama zai koma makaranta.
Ammi take tambayar mama ko 'yan biyu ne saboda kamanin da suke yi, ba ta gane su, kawai dai ta lura da É—aya yana da fara'a É—aya baya yi.
Mama ta ce "Eh 'yan biyu ne, Abubakar da mai sunan babana, shi ne sa, ba ka dariya sai hamma".
Ammi ta yi murmushi ta ce "Tubarkallah Allah ya ray miki, familynki sun burgeni sosai da sosai, rumaisa a yayyen nan naki ki bani biyu mana, na je na ƙara da nawa yaran mana, ni nawa duk rasuwa suke yi, saura uku a raye"
Mama ta ce "Allah sarki, Allah ya raya wanda suka rage, ya jiƙan wanda suka rasu".
Ammi ta amsa da Amin.
Aka zubawa ruma abinci, Abubakar yana bata a baki, tana ta shagwaɓa.
Bashir yayi sallama, da shi da 'yan sanda huÉ—u cikin uniform.
Ruma ta tsaya cak tana bin su da ido, nan suka gaggaisa da kowa, Ammi ta bi bashir da kallon ko lafiya.
"Maman Boy, ya jiki? Yau zaki ganni da police, su ne case É—in binciken aisha yake hannunsu, dan haka za su yi miki tambayoyi ne" a take rumaisa ta haÉ—e rai, ta kawar da kanta gefe.
Ɗaya daga cikin 'yan sandan ya ce "Baby girl, ki amsa mana tambayoyinmu, zai taimaka mana ƙwarai wurin binciko wanda suka yi garkuwa da ku".