← Book details Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 114

Sashe 65

Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baba uwani ta duƙa ta ce "Tuba nake, Allah ya huci zuciyarki, Allah ya sanyaya ruhinki".

"Tashi ki bani wuri, kar ki sake zuwa in da nake idan har baki kawo mini abun da na ce ba".

"In Allah ya yarda ba zan dawo ba sai da saƙonki, tuba nake".

Kwanki goma kenan da sace ruma, amma babu wani labari a kan ta, tun mai sunan Baba yana buga waya ko da wani labari, har mama ta ce yayi haƙuri ya daina kiran wayar.
Shi kansa dagaci ba yadda bai yi ba ayi sulhu, su faÉ—i abin da suke so a basu su sako wanda suka kama, amma suka ce ba zasu bayar ba, yayi musu maganar rumaisa amma suka ce su ba zasu iya gane wata yarinya da suka É—auka a gidansa ba.
Ruma kuwa sai gwada musu halin take na azabar taurin kai da rashin kunya, wataran ta yi borin amma sun ƙi su kasheta kamar yadda take fata, sannan suka fara yi mata horon yunwa, basu cigaba da takurata a kan sai ta bayar da lambar wanda za a kira a gidansu ba, suka ƙyaleta sai dai tana ganin azaba, idan ta ishesu da rashin mutunci, da kan bindiga suke dukanta.
Duk jikinta yayi tsami, ta fita hayyacinta kamar ba ita ba, ga rashin lafiya da take ta fama, wasu ko ba a kashe su ba wahala ce take kashe su a wurin, ruma ta fara sanya ran ita ma wahalar ce zata yi ajalinta.

Tun ruma na iya addu'a har ta fara sarewa, tayi kukan ta kira maman har ta haƙura ta zubawa sarautar Allah ido.

Tana nan kwance kamar matacciya, ta ji wani irin ƙamshin turare mai daɗin gaske ya gauraye wurin.

Wata mata ce take kuka, amma kamar iyayi matar take a cikin kukan, ruma ta ɗago da ƙyar ta kalli matar.
Tsohon ciki ne a jikin matar, duk da ruma ba ta san kan ciki ba, amma yadda cikin matar yayi girma kana gani ka san ta kusa haihuwa, matar na sanye da wani irin farin leshi mai ɗaukar ido da hankali, mai ɗauke da golden a jiki, hannunta zuwa kunnenta duk gold ne. Kai da gani ka san ba a wahala take ba, gata fara sol kamar ba ta shiga rana, sai kuka take ƙafarta na ta zubar da jini tana haki.

"Rufe mana baki, ko mu harbeki a ciki" suka yi mata tsawa toshe bakinta ta yi da hannunta ta zauna tana kuka, tana ƙarewa wurin da taken kallo.

Tausayinta ne ya kama rumaisa, ita wannan ƙaton cikin na matar ne yafi ba ta tausayi. Ita kuma ko a ina suka ɗaukota oho?.

Fatar matar duk tayi burɗun-burɗun, tayi jaa, alamar ƙwari duk sun cijeta a hanya kan su ƙaraso.

Ayshercool.

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*.

Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

https://youtube.com/@CoolhausaNovels?si=Uv_ZJT91QMMuaNxG
Ku yi subscribing YouTube channel É—in mu domin samun daÉ—aÉ—an litattafan hausa na sauraro.

Cikin ƙarfin hali da kuka, matar ta ce "Dan Allah ku yi haƙuri, ku tausaya mini halin da nake ciki, ku sallameni, ko dan halin da nake ciki, cikina saura kwanaki kaɗan na shiga wata tara, dan girman Allah ko nawa ku ke so ku kira gidanmu, za su baku ku sake ni".

"Ke ki rufe mana baki, ke zaki gaya mana abin da zamu yi?"

"Ba abin da zaku yi nake gaya muku ba, taimaka mini zaku yi, dan Allah ku duba halin da nake ciki"

Banza suka yi da ita suka cigaba da abin da ya dame su.

Ruma tana fama da kanta, amma sai bin matar take da kallo, ƙarshen tausayi matar ta bata. Galibin waɗanda aka ɗauko ruma da su, da waɗanda ta tarar an sallami wasu, wasu kuma an kashe su, sannan kuma kusan kullum akwai wanda mutanen za su kawo.

"Ki yi haƙuri ki daina kuka, ki yi addu'a" ruma tayi maganar cikin sanyin jiki.

Matar ta kalli ruma ta share hawayenta, ta ce "To, Allah ya kuɓutar da mu, sun kashe mini direbana ma, ya iyalinsa za su ji?" Tayi maganar cikin kuka.

Ruma a ranta ta ce "Lallai wannan 'yar gata ce, har direba ne da ke"

A haka dare yayi, matar nan na ta kuka, abinka da farar fata ta koma jawur saboda kuka.
Suna nan a  zube a wurin kamar shara, ga wata irin iska da ake yi mai sanyin gaske, ga yunwa na damun ruma ga ciwo, dare ya tsala ruma ta kwanta ta takure, saboda yadda sanyi ya takura mata. Matar nan kuwa tana zaune tana cigaba da aikin kuka, gaba ɗaya a tsorace take da wurin sai waige-waige take, ita ma tana sake dunƙule jikinta saboda sanyin da take ji.

Idon ruma biyu tana kallon matar, a hankali ta matsa kusa da ruma zata kwanta a ƙasa, saboda ta gaji da zaman ga ɗan cikinta ya dunƙule mata wuri guda, cikinta yayi mata babu daɗi, hannunta ne ya taɓa na ruma, ta ji yadda jikin ruma ya ɗau zafi sosai, ta sake kai hannunta goshin rumaisa ta ji kamar an kunna wuta. Ta ɗan jijjiga ruma amma ba ta motsa ba.
Ta cire ɗankwalin kanta ta rufawa ruma a jikinta, ta kwanta ta miƙe ƙafafuwanta, sai dai ba aje ko ina ba, matar ta fara tari da atishawa wanda hakan ba ya rasa nasaba da sanyin da yayi mata yawa.

***
Katafaren falo ne mai girman gaske, kai kace wata fadar ce, saboda girma da tsaruwar falon, Hajiya Jamila ce zaune a kan wani lallausan carfet a ƙasa, yayin da wani babban mutum ke zaune a kan kujera.

"Ina jinki Jamila, ina fatan dai ba wata matsalar ba ce?"

Ta sake duƙawa ta ce "Allah ya ja kwanan mai girman wambai, matsala kam ba za a rasata ba".

"To Ubangiji Allah ya warware mana, meke faruwa?"

"Allah ya taimake ka, tatsuniyar gizo dai ba ta wuce ƙoƙi, ƙarar giwa na kawo maka" sai kuma ta yi shiru.

Ya ce "Ina jinki".

"Allah ya baka yawan rai, na rasa gane in da ta dosa, ban san menene a ranta game da ni da yarana ba, 'ya'yanta ne manya, nawa ƙanana ko da kishi a tsakanin mu, ai bai kamata zumuncin yaranmu ya taɓu ba, shikenan ina son ganin su Nusaiba amma ba sa zuwa in da nake, shi kansa mai babban suna sai ya shafe wata bai taka in da nake ba, wataran tamkar zai dakeni, na rasa irin wannan abu. yaranmu ai abu ɗaya ne a ganina, amma sam yaran nan ban san kallon me suke yi mini ba, gaisuwa sai sun ga dama suke yi mini, mussaman wannan buzuwar yarinyar ni na gaji da irin wannan zaman da muke yi" ta ƙarasa maganar cikin damuwa.
Chapter 65 · 0% Book details