Sashe 93
Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai duk rawar kan rumaisa taƙi sakin jiki ta basu labarin abun da ya faru a zamanta a hannun 'yan ta'adda, ko zancen aka ɗauko sai ta haɗe rai ta hau kuka, gashi haryanzu lokaci zuwa lokaci tana razana, haka kurum tana zaune sai ta hau ihu, tana kiran sunayen 'yan bindigar ta ce zasu yi mata wani abu, har sai da mai sunan Baba ya hana yi mata zancen gaba ɗaya.
Tun da aka rubutawa rumaisa hoto, mama ta aika Abubakar ya tambayo kuÉ—in hoton, aka ce masa dubu arba'in da uku, mama ta É—an shiga damuwa, domin kuÉ—in da yawa, ba ta son yawan É—orawa yaran É—awainiya, dan ma kuÉ—in asibiti da na magani ba biya suke yi ba, an riga an É—au nauyin lafiyar rumaisa a aljihun takawa, dan tun da bashir ya ji yaron nan na Adam ne, ya sanya aka canza musu asibiti zuwa babban asibitin kuÉ—i, domin samun kulawa ta musamman tun da ya san adam yana da kuÉ—in biya, ko magani likita ya rubutawa ruma, sai dai kawai a É—auko a kawo musu, sai dai wanda babu su je waje su saya.
***
Tana zaune a kan katafaren gadonta, sai shirya mata kayanta mai aiki take a cikin akwati, dan ta ƙallafa ranta a kan tafiyarta Abuja nan, sai ba wa mai aikin umarni take cikin isa da kuma gadara gami da wulaƙanci.
Samha kenan akwai gayu da ƙwalisa, sai dai babu hali mai kyau, ɗaya daga cikin wayoyinta ta duba ba ta gani ba, ta js ɗan gajeren tsaki, ta fita ta tafi ɗakin mama.
Mama ta tarar tana ta ƙananan surutai tana mita. "Mama na bar Samsung ɗina a ɗakin nan ne?".
"Ke ni rabu da ni da wata wayarki, turaki ya ɓata mini rai".
Samha ta ce "Too ikon Allah, mai Baban kuma yayi miki?"
"Manta kawai, jirgin ƙarfe nawa zaki bi?"
Samha ta ɗan yi ajiyar zuciya ta ce "Ƙarfe biyar na yamma, amma ki din ga haƙuri mama, kin san tsufa yana taka muhimmiyar rawa a kansa yanzu, idan ki ka matsa zaki yi ta damuwa ne ranki yana ɓaci".
ÆŠan shiru mama tayi sannan ta ce "Abun nasa dai ba tsufa bane, ba wani tsufa kawai halinsa ne, ina yi masa maganar wani abun daban, amma yana nuna mini maganata ba ta da muhimmanci yana kawo mini nasa zancen da bai shafeni ba".
Samha ta yi murmushi ta ɗau wayarta ta ce "Na san tatsuniyar gizo ba ta wuce ƙoƙi, yakamata ace zuwa yanzu kin saba mama, ki yi haƙuri, bari na je na cigaba da shirina" daga haka ta fice ta koma ɗakinta.
***
Abubuwa suka cakuɗewa Adam gaba ɗaya, kallo ɗaya zaka yi masa ka san a cikin tashin hankali yake da matsananciyar damuwa, Ammi ta ce sam ba ta yarda ya je gidansa ya zauna shikaɗai ba, don tun da ya shiga damuwar nan take cikin fargaba, kar ciwonsa ya tashi abu ya ƙara haɗe musu.
Yau da safe Ammi da kanta ta je ta saka Adam a gaba a kan ya ci abinci amma ya kasa ci, sai da ya ga ta matsa sosai da sosai sannan ya É—an cakali kaÉ—an ya bar shi.
Ammi ta dube shi a tsanake sannan ta ce "Takawa" ya É—aga kai ya dubeta.
"Yanzu meye abun yi ne? Me ka yanke a kan lamarin nan, kuma ya ake ciki game da binciken?"
Ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Dama Bashir ne incharge ɗin da case ɗin yake a hannunsa, sannan police ɗin da case ɗin yake hannunsu suna ta ƙoƙari, ina ga in anjima za su je asibitin da kansu, su yi mata tambayoyi".
Ammi ta É—an sauke numfashi sannan ta ce "Bana son a cigaba da yawan matsawa yarinyar ne a kan maganar, na ga haryanzu tana cikin razani, dole a bita a hankali".
Adam a ransa ya ce "Babu wani razani, tsagwaron iskanci ne, kuma da ni take zancenta, ba zan lamunci iskancinta a kan rayuwar matata ba'
Amma a zahiri ya ce "Amma Ammi dole ta yi magana domin gaggauta ceto Aisha".
"Eh haka ne, amma ita ma 'ya ce, kuma yakamta a bita a sannu, saboda lafiyar ƙwaƙwalwarta, kana kallona gabanka jiya take ihu wai an harbe wani" Ammi ta dafe goshi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu, dole yarinyar nan ta shiga ruɗu, ayi kisan kai a gaban yarinya ƙarama kamar wannan"
Shiru Adam yayi, yana ta addu'a Allah ya sa Aisha tana lafiya.
Ya kalli ammi ya miƙe tsaye ya ce "Ammi, bari na je asibitin nan da kaina".
"A'a kar fa ka je ka nuna musu zafin zuciya da zafin kai, ka bi komai a hankali".
Ya girgiza kai ya ce "Ba wani abun zan yi ba, kin san yau za'a kai ta x-ray, so nake na je na ga yaron, in kuma jarrabawa ko zata yi magana".
"To shikenan, ka gaishe su, ni sai zuwa dare in Allah ya kaimu na je" ya jinjina wa ammi kai ya fice.
Likita ne a tsaye a kan rumaisa da take ta bacci, tun bayan da mama ta yi mata wanka, ta yi wa jaririn, ta kwantar da shi a kusa da rumaisa suke ta bacci, haka nan mama ma yaron ya shiga ranta, ga yaron da matuƙar haƙuri, idan yayi kuka ko dai ya gaji da kwanciya ko kuma yana jin yunwa, daga bacci sai cin hannu kawai yake yi, mama ba ta taɓa jin ta gaji da ɗawainiyar da take da ɗan da bata da alaƙa da shi ba, ji take yi hakkinta ne na uwa ta kula da shi, gefe guda kuma tana matsanancin jin tausayinsa tare da fatan Allah ya kuɓutar da mahaifiyar sa, ita kanta da ta ɗaukowa rumaisa zancen uwar yaron, sai ta hau zabure-zabure.
Likita yana duba file É—in ruma yana kallonta, mama ta ce "Likita babu dai matsala ko?".
Ya ce "Eh babu, duk wasu gwaje-gwaje da yakamata ayi mata mun yi mata, babu wani mummunan ciwo a tare da ita, sai dai zan rubuta wata allaura a sayo ayi mata, saboda ciwon haƙarƙarin da take kuka da shi, kan ku yo hoton".
"Eh, in anjima za aje yin hoton in Allah ya yarda, dan sai daf da asuba ta samu bacci, da gari ya waye na tasheta, tana ta kuka da wurin".
Ya ce "In sha Allah idan aka yi allurar, za ta samu releif, kan muga sakamakon".
Mama ta ɗan nisa sannan ta ce "Amma likita ba su yi mata wani abu ba dai ko? Basu taɓa ta ba kun duba?".
Ya jinjinawa mama kai ya ce "Ki kwantar da hankalinki, akwai report da police suka bamu, tun daga asibitin farko da aka kaita, da na biyu zuwa nan, muma da namu binciken, komai lafiya ƙalau".
Mama so take ya bata amsa ƙarara, amma kamar bai fahimci me take nufi ba, ba ta son ya ga kamar ta matsa masa, dan haka ta ƙyale shi".
Ganin yadda rumaisa ke kuka da ciwon haƙarƙarin nan ya sanya ta ce bari ta yi sauri ta je ta sayo allurar, gashi da wuri Abdallah ya tafi, yau yana da jarrabawa a makaranta, gwaggo kuma daga ita har iya suna fama da jikin girma, suma mama cewa tayi su tafi gida su huta, dan haka ganin ruman na barci ya sanya ya fito nursing station ta ce musu dan Allah ga rumaisa nan, za ta je sayo allura.
Mama na fita takawa ya iso asibitin, dan direba ya saka ya kawo shi, shi ba zai iya tuƙin ba.
Yana daf da shiga É—akin da rumaisa take, likita ya fito daga É—akin kusa da nata, suka tsaya suna gaisawa.
Takawa ya tambayi likitan ya jikin jaririnsa?.
Likita ya ce "Baby yana nan lafiya Alhamdilillah, shi ya samu sauƙi sosai Alhamdilillah, mamansa ce dai iya rigima haryanzu muna fama ba ta warware ba, muna jiran sakamakon hoton da zamu turata mu san abun yi na gaba".
Adam ya ce "Haryanzu ta ƙi magana a kan in da mahaifiyar yaron nan take, da an yi maganar sai ta hau ihu, dan Allah hakan yana da nasaba da razani ko kuma iskanci ne kawai"
Sai da doctor yayi dariya ya ce "To kowanne ma zai iya kasancewa, amma razani kam tabbas tana cikinsa haryanzu, wasu lokutan tunanin ya kan ƙwace mata ta zaci tana hannunsu haryanzu, amma abi komai a hankali, sannan dan Allah idan ku ka tashi karɓar yaron nan, ku bita a hankali ta shaƙu da shi sosai, kar ku rabata da shi lokaci ɗaya".
Bayanin likitan na yanzu ya shiga ta kunnen Adam na dama, ya fita na hangu, dan bai ji zai iya saurarawa ko ɗaga ƙafa wurin karɓar ɗansa ba, yanzu ma don yana cikin tashin hankali ne, da damuwa da son sanin in da matarsa take, ba dan haka ba, da tuni ya ɗauk ɗan sa.
"Thank you very much" ya faɗa a taƙaice ya shiga ɗakin rumaisa.
Sai dai yayi mamakin ganin babu kowa, baccinta take hankali a kwance, gefenta ga jaririn shi ma yana barci, kai ka ce uwarsa ce.
Ya ƙarasa gaban gadon ya tsaya ya ƙare mata kallo, a haka tana bacci looking so innocent, amma a zahiri halinta idan ba ka kai ziciyarka nesa ba, sai ta sa zuciyar mutum ta buga.
Ya kalli ƙafarta da aka rage bandejin da ake saka mata, saboda raunukan da suke ƙafar, ga wani yanka a ƙwaurinta, kai da gani ka san faɗuwa ta yi, ga tabo a gefen goshinta, kai ba sai an gaya maka iya wannan ya isa ya tabbatar wa mutum da ruma ta azabtu kan ta kuɓuta.
Hannunsa biyu ya saka a kan gadon, ya ƙurawa yaronsa ido da yake daga lungu, ya tuna irin yadda suka shirya rayuwa da shi da Aisha idan Allah ya sauketa lafiya, da irin budurin da suka shirya yi, da yadda take nanata masa sai dai su bawa mutane mamaki, ba wanda ya san da cikin sai dai su ce wa mutane ga babynsu, yau ga baby amma ita ba ta nan.
Tun da aka rubutawa rumaisa hoto, mama ta aika Abubakar ya tambayo kuÉ—in hoton, aka ce masa dubu arba'in da uku, mama ta É—an shiga damuwa, domin kuÉ—in da yawa, ba ta son yawan É—orawa yaran É—awainiya, dan ma kuÉ—in asibiti da na magani ba biya suke yi ba, an riga an É—au nauyin lafiyar rumaisa a aljihun takawa, dan tun da bashir ya ji yaron nan na Adam ne, ya sanya aka canza musu asibiti zuwa babban asibitin kuÉ—i, domin samun kulawa ta musamman tun da ya san adam yana da kuÉ—in biya, ko magani likita ya rubutawa ruma, sai dai kawai a É—auko a kawo musu, sai dai wanda babu su je waje su saya.
***
Tana zaune a kan katafaren gadonta, sai shirya mata kayanta mai aiki take a cikin akwati, dan ta ƙallafa ranta a kan tafiyarta Abuja nan, sai ba wa mai aikin umarni take cikin isa da kuma gadara gami da wulaƙanci.
Samha kenan akwai gayu da ƙwalisa, sai dai babu hali mai kyau, ɗaya daga cikin wayoyinta ta duba ba ta gani ba, ta js ɗan gajeren tsaki, ta fita ta tafi ɗakin mama.
Mama ta tarar tana ta ƙananan surutai tana mita. "Mama na bar Samsung ɗina a ɗakin nan ne?".
"Ke ni rabu da ni da wata wayarki, turaki ya ɓata mini rai".
Samha ta ce "Too ikon Allah, mai Baban kuma yayi miki?"
"Manta kawai, jirgin ƙarfe nawa zaki bi?"
Samha ta ɗan yi ajiyar zuciya ta ce "Ƙarfe biyar na yamma, amma ki din ga haƙuri mama, kin san tsufa yana taka muhimmiyar rawa a kansa yanzu, idan ki ka matsa zaki yi ta damuwa ne ranki yana ɓaci".
ÆŠan shiru mama tayi sannan ta ce "Abun nasa dai ba tsufa bane, ba wani tsufa kawai halinsa ne, ina yi masa maganar wani abun daban, amma yana nuna mini maganata ba ta da muhimmanci yana kawo mini nasa zancen da bai shafeni ba".
Samha ta yi murmushi ta ɗau wayarta ta ce "Na san tatsuniyar gizo ba ta wuce ƙoƙi, yakamata ace zuwa yanzu kin saba mama, ki yi haƙuri, bari na je na cigaba da shirina" daga haka ta fice ta koma ɗakinta.
***
Abubuwa suka cakuɗewa Adam gaba ɗaya, kallo ɗaya zaka yi masa ka san a cikin tashin hankali yake da matsananciyar damuwa, Ammi ta ce sam ba ta yarda ya je gidansa ya zauna shikaɗai ba, don tun da ya shiga damuwar nan take cikin fargaba, kar ciwonsa ya tashi abu ya ƙara haɗe musu.
Yau da safe Ammi da kanta ta je ta saka Adam a gaba a kan ya ci abinci amma ya kasa ci, sai da ya ga ta matsa sosai da sosai sannan ya É—an cakali kaÉ—an ya bar shi.
Ammi ta dube shi a tsanake sannan ta ce "Takawa" ya É—aga kai ya dubeta.
"Yanzu meye abun yi ne? Me ka yanke a kan lamarin nan, kuma ya ake ciki game da binciken?"
Ya ɗan yi jimm sannan ya ce "Dama Bashir ne incharge ɗin da case ɗin yake a hannunsa, sannan police ɗin da case ɗin yake hannunsu suna ta ƙoƙari, ina ga in anjima za su je asibitin da kansu, su yi mata tambayoyi".
Ammi ta É—an sauke numfashi sannan ta ce "Bana son a cigaba da yawan matsawa yarinyar ne a kan maganar, na ga haryanzu tana cikin razani, dole a bita a hankali".
Adam a ransa ya ce "Babu wani razani, tsagwaron iskanci ne, kuma da ni take zancenta, ba zan lamunci iskancinta a kan rayuwar matata ba'
Amma a zahiri ya ce "Amma Ammi dole ta yi magana domin gaggauta ceto Aisha".
"Eh haka ne, amma ita ma 'ya ce, kuma yakamta a bita a sannu, saboda lafiyar ƙwaƙwalwarta, kana kallona gabanka jiya take ihu wai an harbe wani" Ammi ta dafe goshi ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu, dole yarinyar nan ta shiga ruɗu, ayi kisan kai a gaban yarinya ƙarama kamar wannan"
Shiru Adam yayi, yana ta addu'a Allah ya sa Aisha tana lafiya.
Ya kalli ammi ya miƙe tsaye ya ce "Ammi, bari na je asibitin nan da kaina".
"A'a kar fa ka je ka nuna musu zafin zuciya da zafin kai, ka bi komai a hankali".
Ya girgiza kai ya ce "Ba wani abun zan yi ba, kin san yau za'a kai ta x-ray, so nake na je na ga yaron, in kuma jarrabawa ko zata yi magana".
"To shikenan, ka gaishe su, ni sai zuwa dare in Allah ya kaimu na je" ya jinjina wa ammi kai ya fice.
Likita ne a tsaye a kan rumaisa da take ta bacci, tun bayan da mama ta yi mata wanka, ta yi wa jaririn, ta kwantar da shi a kusa da rumaisa suke ta bacci, haka nan mama ma yaron ya shiga ranta, ga yaron da matuƙar haƙuri, idan yayi kuka ko dai ya gaji da kwanciya ko kuma yana jin yunwa, daga bacci sai cin hannu kawai yake yi, mama ba ta taɓa jin ta gaji da ɗawainiyar da take da ɗan da bata da alaƙa da shi ba, ji take yi hakkinta ne na uwa ta kula da shi, gefe guda kuma tana matsanancin jin tausayinsa tare da fatan Allah ya kuɓutar da mahaifiyar sa, ita kanta da ta ɗaukowa rumaisa zancen uwar yaron, sai ta hau zabure-zabure.
Likita yana duba file É—in ruma yana kallonta, mama ta ce "Likita babu dai matsala ko?".
Ya ce "Eh babu, duk wasu gwaje-gwaje da yakamata ayi mata mun yi mata, babu wani mummunan ciwo a tare da ita, sai dai zan rubuta wata allaura a sayo ayi mata, saboda ciwon haƙarƙarin da take kuka da shi, kan ku yo hoton".
"Eh, in anjima za aje yin hoton in Allah ya yarda, dan sai daf da asuba ta samu bacci, da gari ya waye na tasheta, tana ta kuka da wurin".
Ya ce "In sha Allah idan aka yi allurar, za ta samu releif, kan muga sakamakon".
Mama ta ɗan nisa sannan ta ce "Amma likita ba su yi mata wani abu ba dai ko? Basu taɓa ta ba kun duba?".
Ya jinjinawa mama kai ya ce "Ki kwantar da hankalinki, akwai report da police suka bamu, tun daga asibitin farko da aka kaita, da na biyu zuwa nan, muma da namu binciken, komai lafiya ƙalau".
Mama so take ya bata amsa ƙarara, amma kamar bai fahimci me take nufi ba, ba ta son ya ga kamar ta matsa masa, dan haka ta ƙyale shi".
Ganin yadda rumaisa ke kuka da ciwon haƙarƙarin nan ya sanya ta ce bari ta yi sauri ta je ta sayo allurar, gashi da wuri Abdallah ya tafi, yau yana da jarrabawa a makaranta, gwaggo kuma daga ita har iya suna fama da jikin girma, suma mama cewa tayi su tafi gida su huta, dan haka ganin ruman na barci ya sanya ya fito nursing station ta ce musu dan Allah ga rumaisa nan, za ta je sayo allura.
Mama na fita takawa ya iso asibitin, dan direba ya saka ya kawo shi, shi ba zai iya tuƙin ba.
Yana daf da shiga É—akin da rumaisa take, likita ya fito daga É—akin kusa da nata, suka tsaya suna gaisawa.
Takawa ya tambayi likitan ya jikin jaririnsa?.
Likita ya ce "Baby yana nan lafiya Alhamdilillah, shi ya samu sauƙi sosai Alhamdilillah, mamansa ce dai iya rigima haryanzu muna fama ba ta warware ba, muna jiran sakamakon hoton da zamu turata mu san abun yi na gaba".
Adam ya ce "Haryanzu ta ƙi magana a kan in da mahaifiyar yaron nan take, da an yi maganar sai ta hau ihu, dan Allah hakan yana da nasaba da razani ko kuma iskanci ne kawai"
Sai da doctor yayi dariya ya ce "To kowanne ma zai iya kasancewa, amma razani kam tabbas tana cikinsa haryanzu, wasu lokutan tunanin ya kan ƙwace mata ta zaci tana hannunsu haryanzu, amma abi komai a hankali, sannan dan Allah idan ku ka tashi karɓar yaron nan, ku bita a hankali ta shaƙu da shi sosai, kar ku rabata da shi lokaci ɗaya".
Bayanin likitan na yanzu ya shiga ta kunnen Adam na dama, ya fita na hangu, dan bai ji zai iya saurarawa ko ɗaga ƙafa wurin karɓar ɗansa ba, yanzu ma don yana cikin tashin hankali ne, da damuwa da son sanin in da matarsa take, ba dan haka ba, da tuni ya ɗauk ɗan sa.
"Thank you very much" ya faɗa a taƙaice ya shiga ɗakin rumaisa.
Sai dai yayi mamakin ganin babu kowa, baccinta take hankali a kwance, gefenta ga jaririn shi ma yana barci, kai ka ce uwarsa ce.
Ya ƙarasa gaban gadon ya tsaya ya ƙare mata kallo, a haka tana bacci looking so innocent, amma a zahiri halinta idan ba ka kai ziciyarka nesa ba, sai ta sa zuciyar mutum ta buga.
Ya kalli ƙafarta da aka rage bandejin da ake saka mata, saboda raunukan da suke ƙafar, ga wani yanka a ƙwaurinta, kai da gani ka san faɗuwa ta yi, ga tabo a gefen goshinta, kai ba sai an gaya maka iya wannan ya isa ya tabbatar wa mutum da ruma ta azabtu kan ta kuɓuta.
Hannunsa biyu ya saka a kan gadon, ya ƙurawa yaronsa ido da yake daga lungu, ya tuna irin yadda suka shirya rayuwa da shi da Aisha idan Allah ya sauketa lafiya, da irin budurin da suka shirya yi, da yadda take nanata masa sai dai su bawa mutane mamaki, ba wanda ya san da cikin sai dai su ce wa mutane ga babynsu, yau ga baby amma ita ba ta nan.