← Book details Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 79 OF 114

Sashe 79

Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Lokaci guda mutuwar aisha da ta barde ta faÉ—o mata, aikuwa ta fashe da kuka, tana kuka tana faÉ—in "Anty Aisha ina ma tare muke tafiyar nan, ko ina suka kai gawarki oho, Allah ya yi miki rahama, kai kuma Barde ban sani ba ko Allah zai yafe maka, amma Allah ya baka ladan tausaya mini da ciyar da ni da ka din ga yi, ni dai na yafe maka duniya da lahira.

Ruma ba ta san jikinta babu ƙwari ba, sai da ta fara tafiyar nan, sannan ta gane ashe a galabaice take, jikinta babu ƙwari da ƙarfi kamar yadda take jin ta a da, gaba ɗaya ta gaji, ƙishirwa take ji, ga duhun magariba ya fara yi, kuma babu alamar samun hanya, ƙafafuwanta tuni suka yi tsami, gashi sai taka abubuwa take yi, kama daga ƙaya zuwa ƙananan duwatsu, amma zuciyarta ta cigaba da bata ƙwarin gwiwar ta tafi, tana jin zata iya fita hanya a kowane lokaci.

***
Takawa ne yake ta safa da marwa a É—akinsa, yana daddana wayar hannunsa, kallo É—aya zaka yi masa ka san ya rame, duk yayi wani iri kamar mara lafiya.
Can ya kara wayar a kunnensa, cikin zaƙuwa ya ce "Ya ake ciki, me ka gano? Akwai wani labari ne?".

"Easy mana Adam, wacce zan amsa maka cikin tambayoyin naka tukuna? Ka yi haƙuri wannan bayanin duk ba na waya bane ba, kana da time ka shigo abuja gobe in Allah ya kaimu?".

Adam ya ce "Ni bani da wani time, am so much busy here, abubuwa sun yi mini yawa, koma menene kawai ka gaya mini ta waya, ina jin ka".

"A'a ni babu abun za zan gaya maka ta waya, ka bari ni zan shigo kanon in sha Allah"

Adam ya yakice gumin da yake tsatstsafo masa, ya ce "Bashir, bani da wani isasshen lokaci da zan baka, kawai ka yi abun da na ce, koma menene ka gaya mini, kar aikin da nake yi ya koma baya".

"Na fuskanci a rikice ka ke, idan ka sauko ma yi maganar, gaggawar ba ta da wani amfani " kan adam ya kuma magana, ya kashe wayarsa. Ya yi jifa da wayar a kan gado, ya san tun da bashir ya ce masa ba zai gaya masa a yau ba ba zai faÉ—a ba.

"Bashir why, kana ƙoƙarin mayar mini da aiki baya fa, dole na zo na sameka, ba zan iya jiranka ba".

Ya miƙe hannu ya ɗau waya ɗaya, ya sanya a aljihunsa, ya fita ya ɗau mota ya nufi family house ɗin su.

A sashen Ammi ya tarar da duk iyalan gidan ahalin marigayi Galadiman kano sun hallara, kama daga kan Mummy zuwa Fauziyya da ruƙayya, duk da ita ruƙayya ba ta fiye zama a gidan ba, tana can gidan yayar Mummy, ga kuma Ammi a zaune da iman da kuma Nusaiba, na gidan auren ne kawai ba sa nan. Takawa yayi turus yana kallonsu, wambai ya ƙure shi da ido, ya ƙaraso cikin falon yana sake tsuke fuska ya ɗam risuna ya ce "Barka da zuwa"

Wambai ya ƙi kulashi, shi kuma Adam bai tashi ba.

"Wato wuyanka har yayi kaurin da zan aika maka ka zo, ka yi burus da kirana ko?"

Yayi shiru bai ko motsa ba, sai ma alamun ɓacin rai da suka baiyyana a fuskar shi.

Da sauri Ammi ta ce "Allah ya taimake ka tuba yake yi, ayyuka ne suka sha masa kai, ga rashin lafiya da.....

"Ya isa binta, dama ke ki ke goya masa baya yake abun da ya ga dama, bai san darajar mutane ba sai zuciya ta banza da ta wofi, tabbas na fara gazgata jita-jitar da ake yi a kansa, na cewar yana shaye-shaye, duba da yanayin abubuwan da yake aikatawa, kalli yadda yake muzurai kamar zai kai mini duka, kalli yadda yake yawo a gari, kamar ba jinin sarauta ba, kalli ƙananan kayan da ke jikinsa, duk wani abu da ya shafi al'adar gidan nan nema yake ya watsr da ita, saboda kawai ya raina mutane.

Cikin dakiya Ammi ta sake cewa "Tuba yake, ayi masa afuwa".
Adam a zuciyarsa kuwa ji yake yi tamkar ya tashi yayi tafiyarsa, don cigaba da sauraren wambai, na iya sanya wa ya É—uÉ—É—ura masa ashar ya huta, saboda takaici.

Wambai ya mayar da idonsa kan Ammi ya ce 'Na san kina sane da maganar da take yawo a cikin masarautar nan, na yayi shaye-shaye yayi yimƙurin yi wa waccan yarinya fyaɗe, yayin da daga wata majiyar muka samu labarin ba fyaɗe bane ba, wani abu ne a tsakaninsu daban, to dukkaninku ku sani, ko da ɗan uwana baya raye, ba zan lamuncin mutunci da martabar gidan nan ta lalace ba, a hakan ka ke saka ran sarauta ta shiga hannunka, kana shaye-shaye ga kuma wannan mummunar maganar, ba zan lamunta ba, tun kan maganar nan ta je wurin mai martaba, zan yi wa tufkar hanci, ni na san abun yi. Ke binta ina mai baki umarni a kan lallai wannan yarinya 'yar tsintuwa, ko dai ki nemi ahalinta ki mayar musu da ita, ko kuma ki nema mata miji ta tattara ta bar cikin gidan nan, na baki nan da abun da bai wuce watanni biyu ba, ta daina amfani da kyawunta tana barazana ga mutuncin gidan nan ba. Labarai suna zuwar mana, yadda ake ta samun akasin auren 'ya'yan jamila saboda ita, to ki san abun yi tun kan ku kai ni bango ". Iman ta yi shiru ta sunkuyar da kai, ta riƙe yatsun Ammi tana wasa da su, tana ɗan murzawa da ƙarfi, saboda azabar ɓacin rai da damuwa.
Haka wambai ya ƙarewa Ammi cin mutunci ita da yaranta, a gaban Mummy, daga bisani ya sallame su.

Tun kan su gama watsewa daga falon, iman ta fashe da kuka, mussaman da ake ce wai ita ce ke barazana ga mutuncin gidan. Adam rasa abin da zai ce ya yi, bayan fitar wambai Mummy ta ce "Sai haƙuri fa binta, yaran yau me ka haifesu ba ka haifi halinsu, a zage a bawa yara tarbiyya, kan a samar mana da abun kunyar da zamu gagara kallon duniya, ko mu rasa sarautarmu gaba ɗaya". Babu wanda ya tanka mata a cikin su, har Adam da yake zaune yana jin ta.

Bayan fitar Mummy Adam ya ce "Ammi, Allah fa bai ce in bi wan ubana ba, ke da marigayi kune yake wajibina na biku, dan haka babu ni babu wannan tsohon da zuriyarsa har gaban abada, ba zan ƙara zuwan kiran da zai yi mini ba, kuma ba zan sake zama a gabansa na yi masa kallon uba ba, ita kuma Mummy haryanzu kin hanani dama a kanta, shikenan idan har zamu cigaba da zuba mata ido, to fa zata cigaba da ƙoƙarin ganinmu a rana ne. Ni ban damu ba dama can ni ɗan iska ne mara mutunci a cikin masarautar nan, amma ba zan cigaba da lamuntar wulaƙanta iman ba, ko dan saboda ita yakamata ko sau ɗaya ki kareta" ya ƙarasa maganar a matuƙar zafafe, ya tashi ya bar falon.

Daga Nusaiba har iman saka Ammi suka yi a gaba suna yi mata kuka, ta rasa abun da zata yi, ta rungumesu duka a jikinta tana ajiyar zuciya.

Tabbas takawa yayi gaskiya, haƙuri da kawaicin da take nunawa a kan abubuwan da ake yi wa iman da ma iya kanta da yaranta, yayi yawa, sai dai ba tana yin hakan da wulaƙanta iman ko 'ya'yanta ba, sai dan gudun kar ayi ƙoƙarin rabata da ita.

***
Ko arzikin ganin tafin hannunta rumaisa ba ta iya yi, saboda duhun da ya mamaye ilahirin dajin, sai kukan abubuwa daban daban da take ji, lokaci zuwa lokaci, wasu lokutan kuma ta ji shiru kamar babu wata halitta da ta wanzu a cikin dajin.
Sai yanzu ta gane a wurin 'yan ta'addam nan a rahama take, ko ba komai tana jin motsin mutane, idan ta gaji kuma tana yi musu kuka ko da zasu hantareta,  wani irin sauro da kuma wasu irin ƙwari ne suke gasa mata cizo ko ta ko ina.

Ta yi iya ƙoƙarin ta ta nannaɗe jaririn, dan kar ƙwari su cije shi, sai numfashi yake sama-sama, jikinsa ya ɗau zafi, ita kanta rumaisan zazzaɓi ne a jikinta, ga wata irin azababbiyar ƙishirwa da kuma yunwa da take ji. A haka ta jingina a jikin bishiya tana addu'a tana kuka ƙasa-ƙasa, ba dan tana tausayin jaririn nan ba, da kuma tsoron wanda ya kashe kansa makomarsa wuta ba, to da babu abun da zai hanata ta kashe kanta.
A hankali take sauke numfashi tana soshe-soshe, babu alamar tana jin bacci a idonta.

Kamar wadda aka tsikara, ta tashi tana laluba hanya, tana tafiya a hankali, hannunta É—auke da jariri. Hayaniya ta fara jiyowa sama-sama ana maganganu.
Dan haka ta din ga nufar in da sautin yake fitowa, tana nufar sautin tana hango hasken wuta yana ci, da alama dai mutane ne a wajen. A haka har ta cin musu, ta laɓe tana leƙawa, kusan zata iya cewa wata ƙaramar masan'anta ce ta sarrafa makamai iri iri, manya da ƙanana dan wasu ma ba ta san su ba, wasu suna shaye-shaye wasu suna ta shirya makamai, yayin da wasu ke ƙidaya kuɗi.

"Kai har labari ya cika gari artabun da aka yi a dajin nan, mutuwar su sha tara duk ta cika jaridu, kuma haryanzu babu wata ƙungiya da ta ɗau alhakin kai wa su sha tara hari" cewar wani da yake ta murza sigari.

"Kuma ba jami'an tsaro bane ba, a cikin mu ne dai, kuma an kwashe mutanen suka yi garkuwa da su ba" wani ya bashi amsa.

"Haka na ji, daga sama an bada umarnin abi sahunsu, akwai wani jariri da wata mata ta haifa, ana son a tabattar da baya raye, gobe akwai operation, dole a gano suwaye suka kai harin".

"Haka ne, amma yanzu a gama ware kayan nan, su je su rarraba, da safe a bar gari da su, kai yellow, ku zo ku ɗinke kuɗin nan a cikin buhunhuna a kai su a daren nan, mutanen cikin bukkar nan kuwa duk wanda ba a kawo kuɗin fansar sa ba, ku ƙaddamar masa kawai".
Chapter 79 · 0% Book details