← Book details Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 114

Sashe 72

Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*2.   Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3.  Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4.  Supplements na karawa fata kyau da sheki  glowing skin*

*5.   Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6.   Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7.   Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8.  Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9.  Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10.  Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11.  Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12.  Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13.  Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14.  Supplement na whitening/glowing skin*

*15.  Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

Cigaba da tunkaro su ruma suka yi, ruma kuma ta tattara hankalinta ta ga me za ayi.
Suna zuwa suka kewaye su rumaisa, ɗaya daga cikin su ya sanya hannu zai ɗaga Aisha, amma ruma ta saka hannu ta kare, ta ce 'Wai me zaka yi mata? Matar aure ce fa yaya zaka taɓa ta?".

"Ke, ni ki ke yi wa wannan maganar?" Ya kuma kai hannu zai janyo Aisha, amma ruma ta riƙe hannunsa. Jin hayaniya ya sanya Aisha motsawa a hankali ta buɗe idonta, ta kalli mutanen da ke tsaye a kanta, ta yinƙura da ƙyar ta tashi zaune ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un Lafiya?"

A karo na uku, mutumin ya kai hannu ya danƙi Aisha, ya fara janta, ruma kuma ta miƙe zata bi bayansa, ɗaya daga cikinsu ya danƙo ruma, yayi jifa da ita a gefe ya saita ta da bindiga.

Da sauri sha tara ya ce "A'a kar ka kuskura ka yi mata wani abu, akwai yarjejeniya tsakaninmu da ƙungiyar su barde, mun yi yarjejeniya a kanta, muddin wani abu ya sameta zamu yaƙi juna, babu ruwanku da ita, zan riƙe muku ita, dan ba zata yarda ta bari ku yi aikinku ba".

Yayi maganar tare da ƙarasawa ya danƙo ruma, aikuwa ta hau bori, tana kiran Anty Aisha, Aisha kuwa ta kasa magana, sai miƙawa ruma hannu take yi, mutumin nan kuwa babu imani sai janta yake yi.

Cikin gigita ruma ta ce "Dalla ka cikani, suwaye su me zasu yi mata?"

Sha tara ya ce "Ke a shegen shishshigin ki, zaki jawa kanki abun da ba shikenan ba" kan ruma ta kuma yin wata maganar, sha tara ya watsa wa ruma wani abu a fuska, ta silalale a wurin nan, tana gani sama-sama.

***
"Uwani ki buÉ—e kunnenki da kyau ki ji ni, bana son a wannan karon a samu wata matsala, ki yi mini aikin nan yadda yakamata"

Baba uwani ta risuna ta ce "In Allah ya yarda ba zan bari a samu wani kuskure ba uwar É—akina".

"Yauwwa, aikin da na saka ki ki ka kasa, Fauziyya ta yi mini rabin aikin, dan haka ƙarashe ne zaki yi yanzu, Fauziyya ta tabattar mini da ta gano in da maganin nan yake, yana ɗakin iman, a cikin drowern mudubinta, dan haka duk yadda zaki yi, ki samo mukulli ki buɗe wardrobe ɗin nan, ki ɗauko mini, akwai wani aiki da za ayi mini, wanda lallai sai da shi".

Baba uwani ta É—an yi shiru tana nazarin yadda za ta É—au wannan kasadar.

"Ya ki ka yi shiru ko ba zaki yi ba?"

"Wace ni? Ki ƙaddara an gama wannan aikin uwar ɗakina, zan yi da iznin Allah".

"Ai na zata ba zaki yi bane, sai kuma abu na biyu, wata jita-jita nake son ki yaɗa mini a gidan nan, na san daga nan har masarauta kowa zai ji, dan duk wani mufurci ku hadimai kun iya shi. Ina son ki je ki yayata cewar, Adam ya yi shaye-shaye ya bugu ya tashi yinƙurin yi wa iman fyaɗe!"

Ras! Gaban baba uwani ya faÉ—i, ta gyara zamanta ta ce "Uwar É—akina, fyaÉ—e kuma?"

"Eh, ko baki ji ba?"

"Allah ya baki yawan rai, na ji zan kuma aiwatar"

A wulaƙance "Mummy ta ce "Tashi ki je"

Jiki a sanyaye baba uwani ta tashi ta bar É—akin.

A hanyar komawa sashinsu ta haɗu da baba sabuwa, sabuwa ta ƙure uwani da ido, uwani ta ce "Lafiya ki ke yi mini wannan kallon haka?"

"Lafiya lau, kawai ina tunanin ranar da dubunki ta cika ya zaki yi? Baiwar Allah can ta yarda da ke ta baki amanar kanta da ta 'ya'yanta kina ci, duk wahalar da take yi miki"

A fusace baba uwani ta ce "To ina ruwanki, bana son saka ido fa, wallahi idan ba ki yi wasa ba, sai na gaya mata ta É—au mataki a kan ta".

"Wallahi ki ka gaya mata, kan ta É—au mataki a kaina zan É—auka a kanku, dan sai na ja abun da za'a É—auremu duka, dan nima na san sirrinta tana sakani aiki, ni idan nayi mata babu laifi, dama hadimarta ce ni, ke kuwa fa? Ki dai ji tsoron Allah wallahi" ba ta jira me baba uwani za ta ce ba, ta tafi ta bar wurin.

Hajiya Jamila ɗawisu sarkin ado, sukari ba ka yi farin banza ba, gugar ƙarfe sha kwaramniya. Haka hadimanta suka shiga jera mata kirari, sai dai babu wanda ta kula ta cigaba da takunta ɗai-ɗai ta nufi sashin Ammi.

Ammi kuwa na zaune ita da Adam a É—akinta, yana zaune a gabanta ya sunkuyar da kansa, sai dai duk ya rame, cikin nutsuwa da tawakalli Ammi ke yi masa nasiha.
"Har kullum Adam ba zan gaji jadadda maka batun yin addu'a ba, addu'a na da muhimmanci a rayuwarka, tun da na haifeka a cikin jarrabawa ka ke, ko in ce muke, ka ƙara haƙuri wannan ma zamu cinyeta da yardar Allah, ka yi haƙuri ka jure, na sani akwai ciwo amma ka sani, jarrabawa alamar soyayya Allah ce ga bawansa, kullum cikin Addu'a nake maka, har abada maƙiyanka fadawanka ne, waɗanda ka sani da wanda ba ka sani ba, Allah zai ije maka su in dai har kana Addu'a, ni dai fatana ka rage zafin zuciya adam, babu in da zuciya zata kai ka, ka din ga haƙuri da yanayin da duk zaka tsinci kan ka" wata hadimar Ammi ce ta nemi izini ta shiga, ta sanarwa da Ammi zuwan Mummy.

Sai da gaban Ammi ya faɗi, ba ta ƙaunar abin da zai haɗata da Mummy, dan ba ƙaramin fargaba take shiga ba, ƙarfin Addu'a ne yake sanya ta iya riƙe kanta.
Jiki a sanyaye ta tashi ta fita falo, ta tarar da Mummy a zaune a falon tana yi wa iman magana, sai dai ba ta kai ga jin abin da take cewa iman É—in ba ta yi shiru.

Ita kanta iman ba ƙaramin tsoron Mummy take ji ba, saboda haɗuwarsu babu daɗi sam, ta tsaneta sosai da sosai.

Fuskar iman Ammi ta kalla, ta san akwai wani abu da Mummy ta gaya mata, da ya sanya Iman shiga ruɗi, dan fuskar iman kullum idan ba murmushi ba, to tabbas shagwaɓa, amma sai ta ga iman a razane.

Mummy kuwa na ganin Ammi ta faÉ—aÉ—a murmushin ta, ta risuna ta ce "Allah ya taimaki giwa, barka da fitowa".

Ammi ta nemi wuri ta zauna, ta ce "Barkan ki dai, kuna lafiya?"

"Eh to, mun gode Allah sai dai ba na ce lau ba, yara babu wanda yake zuwa, duk sun ɗauke ƙafarsu".

"Kin san yanayin makaranta, ba sa samun zama shi ne kawai".

Mummy ta yi murmushi ta ce "Haka ne, dama yara ne suka zo mini da batun rashin lafiyar takawa, na ce bari na zo na yi masa sannu, Allah ya bashi lafiya, amma gaskiya yakamata ki tashi ki nema masa magani, shi da ake sanya ran ya gaji mahaifinsa, amma ya din ga abu kamar mahaukaci, gaba É—aya zance ya cika masarauta har kunnen manya".

Kalmar mahaukacin da ta kira Adam da shi, ba ƙaramin dukan Ammi ya yi ba.

Amma ta maze ta ce "Ai shi lamari irin wannan, duk maganin da zaka nema, lafiya ta Allah ce, idan ka miƙa masa lamarinka kuma, sai ya kawo maka mafita, tun da shi ya halicci kowa".

Mummy ta ɗan kaɗa ƙafa ta ce "Haka ne, akwai wasu ɗabi'unki da suke burgeni, wanda har nake koyi da su, ƙarfin hali da yarda da kai, bari mu gani idan yana da rabon warkewa, Allah ya bashi lafiya, na barki lafiya uwar masu jiran gado" ta miƙe tana wani irin shu'umin murmushi.

Kan iman Ammi ta mayar da idonta ta ce "Iman, me ta ce miki ne?"

Iman ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Bakomai Ammi, tambayata take ya jikin Takawa" Ammi tayi shiru, dan ta san iman ƙarya tayi mata, ba ta takura sai ta ji ba, saboda kar ta ji abin da zai ƙara bata haushi.
Chapter 72 · 0% Book details