Sashe 3
Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya É—ora da cewa "Wato ke duk wani abu da za'a gaya miki sai dai ya shiga ta kunnenki na dama, ya fita ta hagu ko?"
Ita dai tayi shiru tana rarraba ido.
"Kyaci ubanki, tashi ki kama kunnenki tun da ba zaki yi hankali ba".
Maraicewa tayi zata fara yi masa magiya, amma da yayi mata wani mugun kallo, ba shiri ta miƙe ta durƙusa ta hau kamun kunne.
Gaba ɗaya Huzaifa ji yayi bai ji daɗi ba, maimakon a hukuntata tun a lokacin amma sai da aka bari ta fara bacci, za a sakata kamun kunne, ya tsaya ta ƙofa yana leƙen tsakar gidan ya san yanzu zata galabaita, gashi babu wanda ya isa ya hana Yaya Umar abin da yayi niyya sai Hassan ɗin sa wato Abubakar Sadik, shi kuma baya nan.
Umar ya nutsu yana duba litattafansa, Rumaisa kuwa sai tangaÉ—i take tana neman ta faÉ—i, amma yayi banza da ita, dan ta san idan ta faÉ—i ko ta tashi ba zata iya É—aukar wani hukuncin ba.
Tun tana kuka ƙasa-ƙasa har ta fara yi da ƙarfi, saboda azabar gajiyar da ta yi.
"Tashi" ya faÉ—a ba tare da ya kalleta ba. Ta É—ago duk ta haÉ—a uban gumi, ga hawaye da majina duk a fuskarta.
"Kukan uban me kike yi?"
Cikin kuka ta ce 'Yaya na gaji ne, dan Allah kayi haƙuri ba zan sake ba, na tuba"
"Da alama haryanzu baki yi laushi ba, yi zaman babur tun da kin gaji da kamun kunne"
Babu kalar izayar da Yaya Umar bai yi mata ba a daren, har Sai da Mama ta ji babu daÉ—i a ranta, amma tuna cewar yarinyar ba 'yar goyo bace ba, ya sanya tayi banza ta cigaba da laziminta.
Aliyu ne ya fito daga ɗakinsu, cikin damuwa ya ce "Dan Allah Yaya kayi haƙuri ka ƙyaleta haka ta je ta kwanta dare yayi, wallahi ta horu, kuma ga gobe in Allah ya kaimu da makaranta".
A fusace Umar ya kalleshi ya ce "Ka ɓace mini daga gabana ko sai na haɗa da kai?" Ran Aliyu ba ƙaramin ɓaci yayi ba, kawai ya girgiza kai ya shiga banɗaki.
Sai da ya tabbatar da ta galabaita sannan ya ce ta zauna ta huta, shi kuma ya tashi ya fita.
Ta dinga kuka kamar ranta zai fita, saboda jin cinyoyinta take kamar babu nama a cikinsu sai rodi, saboda azabar sagewa da suka yi, ƙashin bayanta ma ban da azabar ciwo babu abin da yake yi mata.
Yaya Umar na fita, Huzaifa ya ƙaraso in da take yana mata sannu cikin tausayawa kamar ba shi ne ya gama bawa Mama shawarar ta haɗata da Yaya Umar ba.
Ya je ya ɗebo ruwa ya bata, ta karɓa ta kafa kai tana sha tana kuka. Ta gama sha, ya karɓi kofin ya ajiye yana goge mata hawayen fuskarta.
"Uban me kake a nan wurin?" Basu ji dawowar Yaya Umar ba, sai maganarsa kawai suka ji, suka yi tsuru-tsuru.
"Zaka tashi ko sai na haÉ—a da kai?" Jiki na rawa Huzaifa ya tashi, ya koma É—akinsu.
Ya kalli Ruma da ke ta ajiyar zuciya, ya tabbatar ta galabaita, ya san yanzu haka jikinta na ciwo, ya jefa mata leda a jikinta ya ce "Maza É—auki ki shanye"
Jiki na rawa ta ɗau ledar, doguwar jarka ce cike da youghurt mai sanyi a ciki, ta ɗaga kai ta sha rabi, yana tsaye yana kallonta, ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Na ƙoshi".
Jin bai ce komai ba ne ya sanya ta ɗago ta kalleshi, ganin yana mata wani irin kallo ne, ya sanya ta cigaba da sha tana yamutsa fuska, da ƙyar ta shanye, ta ajiye robar tana jiran umarni na gaba.
"wuce ki je ki kwanta"
Da ƙyar da yinƙura ta tashi, ƙafafuwanta na ta rawa saboda ciwo, ta shiga ɗaki.
Tana shiga ta tarar da Mama na salla, ta faÉ—a kan katifa tana kuka.
Mama har ta idar da sallar ba tace mata komai ba, ta cigaba da kukanta har bacci ya É—auke ta.
Cikin bacci ta ji Mama na É—ala mata duka a cinyarta "Tashi" duk da yadda ta ji zafin dukan, amma ta buÉ—e idonta a hankali ta kalli Mama, ba tare da ta ce komai ba.
"Saboda tsabar rashin hankali, ki kwanta ki yi fitsari a kwance, ke ba jaririya ba ba 'yar yaye ba" jin abin da Mama ta faɗa ne ya sanya ta miƙe zumbur, ta ganta luntsum a cikin fitsari.
Waro ido ta yi ta ce "Na shiga uku, wallahi na zata a mafarki ne, dan Allah kiyi haƙuri"
Mama cikin ɓacin rai ta girgiza kai ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, zaki tashi ki fita kije ki gyara jikinki ko kuwa?"
Sannu a hankali ta sauka daga kan katifar, saboda yadda jikinta ko ina yake yi mata ciwo, saboda punishment É—in da Yaya Umar ya sanya ta.
Da ta fita tsakar gida da rarrafe ta ƙarasa banɗaki, ta wanke jikinta ta dawo ta canza kaya, ta jingine katifar tayi kwanciyarta a ƙasa.
Har ga Allah, tana jin yadda fitsarin ya matseta, amma ta ji gandar tashi, saboda bacci take ji sosai, ga kuma ciwo da jikinta yake yi, dan haka ta cigaba da baccinta, da ta ganta a banÉ—aki ta zaci a gaskene ta saki fitsarinta.
Tana jin yadda Mama ke ta mita, amma ita ko a jikinta, wani nannauyan baccin ne ma yayi awon gaba da ita.
Da Asuba ma an kai ruwa rana kan Mama ta samu Rumaisa ta tashi ta yi salla, dan sai da ta yi iƙirarin haɗata da Yaya Umar sannan ta tashi ta yi sallar.
Ta idar da salla Mama tayi mata maganar shirin makaranta, amma ta tura baki ta ce "Ai kina gani jiya mai sunan Baba yana azabtar da ni baki hana shi, ni bani da lafiya, ba zani ba cinyata kamar an mini É—orin karaya haka nake ji na"
Mama ta yi mata shiru ta cigaba da laziminta, Huzaifa ne ya fara shigowa É—akin Mama ya gaisheta, suka gaisa ya tambayi Mama mai za'a É—ora na karin kumallo?.
Mama ta ce "Bari gari yayi haske, sai a sayo gasara, ka cewa Yasir ya feraye maka dankali, sai a soya"
Huzaifa ya jinjina kai ya miƙe, har zai fita idonsa ya sauka a kan katifar Rumaisa, ya ɗan yi turus ya dubi Mama ya ce "Mama ba dai fitsarin kwance yarinyar nan tayi ba?"
"Gashi kuwa kana gani, ai Yarinyar nan sai addu'a kawai".
"Innalillahi wa innalillahi raji'un, su Balama an yi asarar kunnuwa, ba sai ki saka ta fitar miki da ita daga ɗaki ba, sai ɗakin ya fara wari tukuna, abinka da fitsarin gardiya bana jariri ba, tashi shashasha" ya ƙarasa maganar yana zuba wa Rumaisa duka a ƙafa.
A gigice ta tashi zaune ta raba ido, tayi zaton Mama ce ta daketa, amma taga Huzaifa a kanta.
"Me nayi maka zaka dakeni?" Tayi maganar a ƙule.
"An dake ki ɗin, tashi ki fitar mata da wannan katifar daga ɗaki, mai abin kunya ƙatuwa da ke kina fitsarin kwance"
"Ba zan fita da ita É—in ba, uban shishshigi ko ina ruwanka, tun da ba a kan ka nayi ba, kuma ruwa ne ya zube ba fitsari nayi ba".
"Au Mama ƙarya take yi miki kenan, ba zaki tashi ba?"
Cikin tsiwa ta ce "Ba zan tashi ba"
miƙa hannu yayi, ya janyota ya ɗagata, ya ce "Wallahi sai kin fita da katifar nan kin wanke kayan da kika yi tsiyar a kan su". Idan da sabo Mama ta saba da wannan halin nasu na faɗace-faɗace, gashi Huzaifa ya bawa Rumaisa kusan shekaru shida, amma faɗa kamar suna ganin hanjin junansu.
Mama ta sharesu ta ƙi ko kallon in da suke, Rumaisa ta dinga turjewa tana kwarara ihu.
Basu yi aune ba suka ga Yaya Umar a tsakiyar É—akin, take suka yi cirko-cirko suna kallonsa.
Cikin kaushin murya ya ce "Meye haka karnuka ne ku?"
Suka girgiza kai a tare.
"Me kai mata take wannan ihun, da idon Mama bai sanya kun daina ba?".
"Fitsari ta yi a kwance, shi ne nace ta fita da kayan"
Cikin mamaki Umar ya kalleta ya ce "Fitsarin kwance kuma? Kina me kika yi fitsari?"
Cikin rauni ta ce "Wallahi Yaya tsautsayi ne, kasa tashi nayi"
"Tsautsayin uban wa? Kwashe kayan ki fita ki wanke ƙazamar banza kawai".
Haka ta ja katifar ta fita da ita tsakar gida, ta kwaso kayan da ta yi wa fitsari ta hau wanki.
Huzaifa ya faki idon Yaya Umar ya dinga yi mata dariya.
Duk wanda ya fito tsakar gida ya ga katifar Rumaisa sai ya ce me ya fito da katifar, Huzaifa sai yayi farat ya gaya musu ai fitsarin kwance ta yi.
Tausayinta ne ya kama Usman, ganin yadda take kuka, kuma ba ta saba yin fitsarin kwance ba, ya je ya karɓi kayan ya tayata.
Kowa da abin da yake faÉ—a a kan Ruma, wasu na mata Addu'a shiriya wasu kuma na yi mata faÉ—a har da zagi.
Tamkar gidan 'yan mata, haka zaratan samarin nan suka kama aikin gida, wasu na wanke-wanke, wasu shara da Abin karyawa, kan gari ya ƙarasa haske, hatta ruwan da Rumaisa zata yi wanka, an dafa ta haɗa ta yi wanka.
Haka suka jeru a tsakar gida, tare da Mama suna karyawa, Rumaisa kuwa sai shan kunun take da ƙyar tana yamutsa fuska.
Can ta kalli Mama ta ce "Mama Kununa bai ji suga ba, yayi tsami da yawa".
Haushi ya kama Mama ta ce "Amma a gabanki aka zazzage sugan kowa ya ɗiba ko? Kuma kin san ya ƙare"
Ta ture kofin kunun ta ce "Nifa dama kunun nan gudawa yake sani, gashi bai ji suga ba, ni cikina ma har ya fara ciwo"
Umar kawai ya girgiza kai, Rumaisa ba zata taɓa zaman mintuna goma lafiya ba, ba tare da tayi abin da za a yi mata magana ba.
Haidar ya kalleta, ya zura hannu a Aljihunsa ya É—auko É—ari biyu ya bata ya ce "Jeki wurin Mamuda ya baki buredi da suga, akwai ruwan zafi sai ki haÉ—a shayi ki sha"
Ita dai tayi shiru tana rarraba ido.
"Kyaci ubanki, tashi ki kama kunnenki tun da ba zaki yi hankali ba".
Maraicewa tayi zata fara yi masa magiya, amma da yayi mata wani mugun kallo, ba shiri ta miƙe ta durƙusa ta hau kamun kunne.
Gaba ɗaya Huzaifa ji yayi bai ji daɗi ba, maimakon a hukuntata tun a lokacin amma sai da aka bari ta fara bacci, za a sakata kamun kunne, ya tsaya ta ƙofa yana leƙen tsakar gidan ya san yanzu zata galabaita, gashi babu wanda ya isa ya hana Yaya Umar abin da yayi niyya sai Hassan ɗin sa wato Abubakar Sadik, shi kuma baya nan.
Umar ya nutsu yana duba litattafansa, Rumaisa kuwa sai tangaÉ—i take tana neman ta faÉ—i, amma yayi banza da ita, dan ta san idan ta faÉ—i ko ta tashi ba zata iya É—aukar wani hukuncin ba.
Tun tana kuka ƙasa-ƙasa har ta fara yi da ƙarfi, saboda azabar gajiyar da ta yi.
"Tashi" ya faÉ—a ba tare da ya kalleta ba. Ta É—ago duk ta haÉ—a uban gumi, ga hawaye da majina duk a fuskarta.
"Kukan uban me kike yi?"
Cikin kuka ta ce 'Yaya na gaji ne, dan Allah kayi haƙuri ba zan sake ba, na tuba"
"Da alama haryanzu baki yi laushi ba, yi zaman babur tun da kin gaji da kamun kunne"
Babu kalar izayar da Yaya Umar bai yi mata ba a daren, har Sai da Mama ta ji babu daÉ—i a ranta, amma tuna cewar yarinyar ba 'yar goyo bace ba, ya sanya tayi banza ta cigaba da laziminta.
Aliyu ne ya fito daga ɗakinsu, cikin damuwa ya ce "Dan Allah Yaya kayi haƙuri ka ƙyaleta haka ta je ta kwanta dare yayi, wallahi ta horu, kuma ga gobe in Allah ya kaimu da makaranta".
A fusace Umar ya kalleshi ya ce "Ka ɓace mini daga gabana ko sai na haɗa da kai?" Ran Aliyu ba ƙaramin ɓaci yayi ba, kawai ya girgiza kai ya shiga banɗaki.
Sai da ya tabbatar da ta galabaita sannan ya ce ta zauna ta huta, shi kuma ya tashi ya fita.
Ta dinga kuka kamar ranta zai fita, saboda jin cinyoyinta take kamar babu nama a cikinsu sai rodi, saboda azabar sagewa da suka yi, ƙashin bayanta ma ban da azabar ciwo babu abin da yake yi mata.
Yaya Umar na fita, Huzaifa ya ƙaraso in da take yana mata sannu cikin tausayawa kamar ba shi ne ya gama bawa Mama shawarar ta haɗata da Yaya Umar ba.
Ya je ya ɗebo ruwa ya bata, ta karɓa ta kafa kai tana sha tana kuka. Ta gama sha, ya karɓi kofin ya ajiye yana goge mata hawayen fuskarta.
"Uban me kake a nan wurin?" Basu ji dawowar Yaya Umar ba, sai maganarsa kawai suka ji, suka yi tsuru-tsuru.
"Zaka tashi ko sai na haÉ—a da kai?" Jiki na rawa Huzaifa ya tashi, ya koma É—akinsu.
Ya kalli Ruma da ke ta ajiyar zuciya, ya tabbatar ta galabaita, ya san yanzu haka jikinta na ciwo, ya jefa mata leda a jikinta ya ce "Maza É—auki ki shanye"
Jiki na rawa ta ɗau ledar, doguwar jarka ce cike da youghurt mai sanyi a ciki, ta ɗaga kai ta sha rabi, yana tsaye yana kallonta, ba tare da ta kalleshi ba ta ce "Na ƙoshi".
Jin bai ce komai ba ne ya sanya ta ɗago ta kalleshi, ganin yana mata wani irin kallo ne, ya sanya ta cigaba da sha tana yamutsa fuska, da ƙyar ta shanye, ta ajiye robar tana jiran umarni na gaba.
"wuce ki je ki kwanta"
Da ƙyar da yinƙura ta tashi, ƙafafuwanta na ta rawa saboda ciwo, ta shiga ɗaki.
Tana shiga ta tarar da Mama na salla, ta faÉ—a kan katifa tana kuka.
Mama har ta idar da sallar ba tace mata komai ba, ta cigaba da kukanta har bacci ya É—auke ta.
Cikin bacci ta ji Mama na É—ala mata duka a cinyarta "Tashi" duk da yadda ta ji zafin dukan, amma ta buÉ—e idonta a hankali ta kalli Mama, ba tare da ta ce komai ba.
"Saboda tsabar rashin hankali, ki kwanta ki yi fitsari a kwance, ke ba jaririya ba ba 'yar yaye ba" jin abin da Mama ta faɗa ne ya sanya ta miƙe zumbur, ta ganta luntsum a cikin fitsari.
Waro ido ta yi ta ce "Na shiga uku, wallahi na zata a mafarki ne, dan Allah kiyi haƙuri"
Mama cikin ɓacin rai ta girgiza kai ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, zaki tashi ki fita kije ki gyara jikinki ko kuwa?"
Sannu a hankali ta sauka daga kan katifar, saboda yadda jikinta ko ina yake yi mata ciwo, saboda punishment É—in da Yaya Umar ya sanya ta.
Da ta fita tsakar gida da rarrafe ta ƙarasa banɗaki, ta wanke jikinta ta dawo ta canza kaya, ta jingine katifar tayi kwanciyarta a ƙasa.
Har ga Allah, tana jin yadda fitsarin ya matseta, amma ta ji gandar tashi, saboda bacci take ji sosai, ga kuma ciwo da jikinta yake yi, dan haka ta cigaba da baccinta, da ta ganta a banÉ—aki ta zaci a gaskene ta saki fitsarinta.
Tana jin yadda Mama ke ta mita, amma ita ko a jikinta, wani nannauyan baccin ne ma yayi awon gaba da ita.
Da Asuba ma an kai ruwa rana kan Mama ta samu Rumaisa ta tashi ta yi salla, dan sai da ta yi iƙirarin haɗata da Yaya Umar sannan ta tashi ta yi sallar.
Ta idar da salla Mama tayi mata maganar shirin makaranta, amma ta tura baki ta ce "Ai kina gani jiya mai sunan Baba yana azabtar da ni baki hana shi, ni bani da lafiya, ba zani ba cinyata kamar an mini É—orin karaya haka nake ji na"
Mama ta yi mata shiru ta cigaba da laziminta, Huzaifa ne ya fara shigowa É—akin Mama ya gaisheta, suka gaisa ya tambayi Mama mai za'a É—ora na karin kumallo?.
Mama ta ce "Bari gari yayi haske, sai a sayo gasara, ka cewa Yasir ya feraye maka dankali, sai a soya"
Huzaifa ya jinjina kai ya miƙe, har zai fita idonsa ya sauka a kan katifar Rumaisa, ya ɗan yi turus ya dubi Mama ya ce "Mama ba dai fitsarin kwance yarinyar nan tayi ba?"
"Gashi kuwa kana gani, ai Yarinyar nan sai addu'a kawai".
"Innalillahi wa innalillahi raji'un, su Balama an yi asarar kunnuwa, ba sai ki saka ta fitar miki da ita daga ɗaki ba, sai ɗakin ya fara wari tukuna, abinka da fitsarin gardiya bana jariri ba, tashi shashasha" ya ƙarasa maganar yana zuba wa Rumaisa duka a ƙafa.
A gigice ta tashi zaune ta raba ido, tayi zaton Mama ce ta daketa, amma taga Huzaifa a kanta.
"Me nayi maka zaka dakeni?" Tayi maganar a ƙule.
"An dake ki ɗin, tashi ki fitar mata da wannan katifar daga ɗaki, mai abin kunya ƙatuwa da ke kina fitsarin kwance"
"Ba zan fita da ita É—in ba, uban shishshigi ko ina ruwanka, tun da ba a kan ka nayi ba, kuma ruwa ne ya zube ba fitsari nayi ba".
"Au Mama ƙarya take yi miki kenan, ba zaki tashi ba?"
Cikin tsiwa ta ce "Ba zan tashi ba"
miƙa hannu yayi, ya janyota ya ɗagata, ya ce "Wallahi sai kin fita da katifar nan kin wanke kayan da kika yi tsiyar a kan su". Idan da sabo Mama ta saba da wannan halin nasu na faɗace-faɗace, gashi Huzaifa ya bawa Rumaisa kusan shekaru shida, amma faɗa kamar suna ganin hanjin junansu.
Mama ta sharesu ta ƙi ko kallon in da suke, Rumaisa ta dinga turjewa tana kwarara ihu.
Basu yi aune ba suka ga Yaya Umar a tsakiyar É—akin, take suka yi cirko-cirko suna kallonsa.
Cikin kaushin murya ya ce "Meye haka karnuka ne ku?"
Suka girgiza kai a tare.
"Me kai mata take wannan ihun, da idon Mama bai sanya kun daina ba?".
"Fitsari ta yi a kwance, shi ne nace ta fita da kayan"
Cikin mamaki Umar ya kalleta ya ce "Fitsarin kwance kuma? Kina me kika yi fitsari?"
Cikin rauni ta ce "Wallahi Yaya tsautsayi ne, kasa tashi nayi"
"Tsautsayin uban wa? Kwashe kayan ki fita ki wanke ƙazamar banza kawai".
Haka ta ja katifar ta fita da ita tsakar gida, ta kwaso kayan da ta yi wa fitsari ta hau wanki.
Huzaifa ya faki idon Yaya Umar ya dinga yi mata dariya.
Duk wanda ya fito tsakar gida ya ga katifar Rumaisa sai ya ce me ya fito da katifar, Huzaifa sai yayi farat ya gaya musu ai fitsarin kwance ta yi.
Tausayinta ne ya kama Usman, ganin yadda take kuka, kuma ba ta saba yin fitsarin kwance ba, ya je ya karɓi kayan ya tayata.
Kowa da abin da yake faÉ—a a kan Ruma, wasu na mata Addu'a shiriya wasu kuma na yi mata faÉ—a har da zagi.
Tamkar gidan 'yan mata, haka zaratan samarin nan suka kama aikin gida, wasu na wanke-wanke, wasu shara da Abin karyawa, kan gari ya ƙarasa haske, hatta ruwan da Rumaisa zata yi wanka, an dafa ta haɗa ta yi wanka.
Haka suka jeru a tsakar gida, tare da Mama suna karyawa, Rumaisa kuwa sai shan kunun take da ƙyar tana yamutsa fuska.
Can ta kalli Mama ta ce "Mama Kununa bai ji suga ba, yayi tsami da yawa".
Haushi ya kama Mama ta ce "Amma a gabanki aka zazzage sugan kowa ya ɗiba ko? Kuma kin san ya ƙare"
Ta ture kofin kunun ta ce "Nifa dama kunun nan gudawa yake sani, gashi bai ji suga ba, ni cikina ma har ya fara ciwo"
Umar kawai ya girgiza kai, Rumaisa ba zata taɓa zaman mintuna goma lafiya ba, ba tare da tayi abin da za a yi mata magana ba.
Haidar ya kalleta, ya zura hannu a Aljihunsa ya É—auko É—ari biyu ya bata ya ce "Jeki wurin Mamuda ya baki buredi da suga, akwai ruwan zafi sai ki haÉ—a shayi ki sha"