Sashe 25
Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har mai sunan Baba ya dawo ruma tana nan tana aikin kamun kunne, tana yi tana faÉ—uwa tana tashi.
Sai da ya dawo sannan ya ce ta tashi, kuma ya ce mata washegari za su gauraya.
Tana miƙewa tsaye jiri ya kwasheta sai amai, Gwaggo ta fito da sauri ta kama ruma, kanta sai juyawa yake saboda azabar wahala.
A zaune ta yi alwala tayi sallar isha'i, ko abinci ba ta nema ba, ta kwanta saboda galabaita, cinyoyinta sai azabar ciwo suke yi mata, dama da fari suna ciwo saboda hawan keke, gwiwoyinta na raɗaɗi saboda duk ta ƙuje su saboda keke, yanzu kuma ga kamun kunne, jikinta kamar an mata duka haka take jin ta, a take wani irin wahalallen bacci ya kwasheta.
Sai dai kwana ta yi da wani irin zazzafan zazzaɓi, wanda ita kanta ba ta san ya hau ta ba, jin surutan ta ya yi yawa a baccin ne ya sanya mama zuwa ta taɓa jikinta, ta ji da zafi sosai.
Duk da mama a ƙule take da ruma, haka ta fita ta ɗebo ruwa ta sanya ɗan ƙaramin towel, ta din ga shafawa ruma ruwa a jikinta.
Tun asubar fari kuwa, ruma amai ne ya tasheta, saboda har a lokacin jiri take yi.
Yanzu ma a zaune ta yi sallar asuba, ta nemi wuri ta kwanta.
Tun mama na basar da ita, har kuma ta fara damuwa, Gwaggo kuwa ta samu wuri É—aya ta zauna sai mita take na masifa a kan mama tana gani aka bawa ruma gwale-gwale amma ba ta ce komai ba.
Bayan gari ya gama wayewa, Gwaggo ta karya ta yi haramar tafiya, sai dai a lokacin ruma ta samu bacci, dan a galabaice take. Gwaggo ta ce kar a tasheta, Abdallah ya tafi rakata tasha, suna ta murna zasu huta, dan dama Gwaggon ta ishe su, ruma ce kawai take son zamanta a gidan.
Mama ta tashi ruma, ta matsa mata a kan lallai ta ci Abinci, ta na ci tana kuka ta É—an sha tea kaÉ—an ta kuma kwanciya, sai dai ko mintuna goma ba ayi da cin Abincin na ta ba, ta tashi ta cigaba da amai.
Ba shiri mama ta ce Aliyu ya zo ya kai ruma chemist a dubata.
Da ƙyar take iya tafiya, suna tafe tana kuka, har sai da ran Aliyu ya fara ɓaci, amma ya shareta suka cigaba da tafiya a hankali. Cikin sa'a kuwa suka tarar ya fito, kasancewar asabar ce, ranar ba ya zuwa aiki.
Ya na ganinsu cikin kulawa ya ce "Subhanallah, 'yar gidan mama yau ke ce ba lafiya?" Ita dai ba ta iya magana ba ta nemi wuri ta zauna. Aliyu ya zauna ya rungumeta, saboda ƙoƙarin faɗuwa take yi.
"Meya sameta haka?"
Aliyu ya ce "Ina ga zazzaɓi ne dai, da amai ta fara jiya"
Bakinta bai mutu ba, ta ce "Kamun kunne aka sakani, kusan awa goma shine ya sani rashin lafiya"
"Subhanallah, waye ya saki kamun kunne kuma?"
"Mai sunan Baba ne"
"To ki yi haƙuri, yanzu dai zan ɗibi jininki na yi miki gwaji, in duba meye ya haddasa zazzaɓin"
Ɗiban jinin da za'a yiwa ruma, tamkar za a cire mata ido, ta dinga kurma ihu, tana fizge-fizge, ga ta da shegen ƙarfi, da ƙyar Aliyu ya riƙeta aka ɗebi jinin nan.
Kuka har da majina, Aliyu ya dinga dungure mata kai yana zaginta.
Ya gama gwaje-gwajen da zai yi mata, ya ce "Malaria ce ke damunta, dan haka akwai buƙatar ayi mata allurai, da kuma magunguna"
Ruma ta yi masa zuru da ido, tana jiran ta ga a ina za ayi allaurar.
Ya haɗa alluransa ya nufo ta, ta miƙe tsaye.
"Ke malama ki tsaya, dan ba zaki sake wahalar da ni ba"
"To a ina za ayi mini allurar?"
Mai chemist ya ce "Ai a baya ake yin ta"
"Wai bayana" tayi maganar tana nuna bayanta.
Nasiru mai chemist ta ce "A'a a mazaunai"
"Suwaye mazaunan?"
Aliyu ya haÉ—e rai ya ce "Ke juya ki tsaya ayi miki allurar nan mu tafi, kin san sarai a in da za ayi".
Ta riƙe skirt ɗin ta gam ta ce "Ni wallahi ba zai ganni ba"
Aliyu ya fizgota, ya riƙeta da ƙyar suka danneta suka yi mata, Aikuwa ta din ga zunduma ihu, kamar sun mata wani abu.
Haka aka gama yi mata treatment, suka taho gida, ban da uban kuka babu abin da take yi.
"To subhanallah, ko me aka yi mata kuma take wannan uban kukan haka oho" mama ta yi maganar tana fitowa tsakar gida.
Aikuwa suna shigowa, ta nufi mama tana kuka.
"Meye haka, kukan me ki ke haka,ki ke ɓare baki?"
"Mama yaya Aliyu ne da Nasiru mai chemist"
"Suka yi miki me?"
"Bayan ya É—ibar mini jini, kuma suka buÉ—e mini tsiraici na aka yi mini allura"
Mama ta ce "Subhanallah"
"Mama ba ke ki ka ce ɗuwawu tsiraici bane ba, amma har da Yaya Aliyu ya riƙe ni, Nasiru mai chemist ya ganni, wallahi ban yafe ba"
Mama ta girgiza kai, ta ƙiftawa Aliyu ido sannan ta ce "Haba Haidara, ya zaka yi mini haka, dan me za'a buɗe mata jiki ayi mata allura?"
Aliyu ya ce "To mama ai larura ce, ko a addinance ba haramun bane".
Cikin masifa ta ce "To shi yayana ne da zai ganni? Har da taɓani ya yi mini allura a wurin"
Aliyu ya ce "Sa'anki ne ni, uban me za a kalla a jikin naki?"
"Wallahi ba zan taɓa yafewa ba, Allah ya jijjigo bala'in duniya da lahira ya ɗora masa, tun da ya ganan mini tsiraici na"
Mama ta ce"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace irin Addu'a ce haka, kar in kuma ji, baki san larura ba?"
Aliyu ya ce "Sakarya, kamar ba tsairaicin ki ka je kina kaÉ—awa a gaban mutane ba jiya"
Umar ya shigo É—akin mama, suna magana, bai kula ruma ba amma dan ya duba jikinta ya shigo.
Tana kwance ga zafin ciwo, ga na takaicin allurar da aka yi mata, zafin allaurar bai dameta kamar ganinta da mai chemist ya yi.
Sai da yamma mama ta sakata ta yi wanka, ta canza kaya ta ɗan ji ƙwarin jikinta.
Sai da ta kwana uku tana fama, sannan ta ware gaba ɗaya, sai dai rashin lafiyar da tayi ya sanya aka mance da laifin da ta tafka, kowa sai lallaɓata yake, ban da Huzaifa.
Ta ware sarai har ta koma makaranta, kullum mama cikin nasiha take yi mata, tare da yi mata addu'a da fatan shiriya.
Tun daga ranar ruma ta daina bi ta hanyar chemist É—in Nasiru, idan kuwa ta ganshi ko kallonsa ba ta yi, balle ta gaishe shi, a cewarta É—an iska ne tsairaicin ta ya kalla.
"Mama wai yaushe zaki haihu ne, babannin 'yan ajinmu sai haihuwa suke yi, amma ke ban taɓa ganin kin haihu ba"
Mama ta ce "Ikon Allah, ba gaki na haife ki ba, ai ke ce auta ha zan kuma haihuwa ba, sai dai in kin girma kin haifa na É—auka"
"To ni yaushe zan haihun?"
"Sai kin girma kin yi aure"
Ruma ta ɗan yi jimm sannan ta ce "To ni so nake na haihu, ina son ƙani ko ƙanwa da zan din ga wasa da su"
"Ruma ki ka haihu yanzu ai a nemi tsari, sai an yi aure ake haihuwa"
"To gaskiya mama ni so nake na haihu yanzu"
Usman da yake jin hirar ta su ya ce "Ke, idan ki ka haihu ba aure tsanarki za ayi, a kore ki daga gidan nan da unguwar ma gaba ɗaya, shi ya sa ba a wasa da maza, ki ka bari namiji ya taɓa ki to ciki zaki ki haihu, kuma korar ki za mu yi"
Waro ido ruma tayi ta ce "Amma ku kuke taɓani?"
"Ai mu yayyenki ne, muharramanki ne mu"
Ruma ta dafe ƙirji ta ce "Allah ya rufa mini asiri, ai da ban sani ba, taɓ idan aka koreni ina zani?"
"Oho miki dai, wannan damben da ki ke da maza ma, idan ba ki daina ba, sai dai ki ga kin haihu, kuma sai kin bar mana gida"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce "In sha Allah hakan ma ba zata faru ba, ai ni ban san hakan abin yake ba, Allah ya sa na yi tsawo na auri kyakykyawa mai kuÉ—i".
Mama ta ce "Ke zan ci ubanki ke da kyakykyawa mai kuɗin nan, miji na gari ake roƙon Allah, fitsararriya"
"Ni dai gaskiya bana son mummuna, mai kyau nake so"
"Ke dalla ware, da wannan munin za ki auri kyakykyawa?"
"Ni dai yaya Ussy, ka yi mini Addu'a, ka san wa zan aura a cikin 'yan ball".
Miƙewa ya yi ya ce "Ba ni da lokacin jij wannan shirmen na ki".
Tun daga wannan lokacin, ruma take kaffa-kaffa, da gudun kar wani namiji ya taɓa ta, saboda kar ta haihu a koreta ta shiga uku, kuma ta san idan aka koreta ba kuɗin mota za a bata ba, balle ta tafi ko ƙauye ne wurin Gwaggo.
Yau gaba É—aya mama ta kasa gane kan ruma, tun da ta dawo daga makaranta yanayinta ya nuna kamar tana cikin damuwa.
Ba irin tambayar da mama ba ta yi mata ba, amma ta ƙi gayawa maman dalilin damuwarta ta, ta ce cikinta ne yake yi mata ciwo kawai
Mama ta aiki ruma sayen maganin sauro, ta je ta sayo, ta dawo ta tsaya a soro tana kuka.
Huzaifa ne ya sameta a soron tana kuka, dan sai da ya É—an tsorota.
"Ke me ki ke yi a nan?"
Cikin kuka ta kira sunansa "Huzaifa"
"Na'am" ya amsa.
"Ka san wani abu?"
"A'a sai kin faÉ—a"
"Yaya Usyy ne ya ce mini idan namiji ya taɓani, zan yi ciki in haihu, kuma korata za ayi daga gidan nan, sai malam ya aikeni karɓo masa chalk, da na kawo masa hannunsa ya taɓa nawa. Na tambayi 'yan babban aji na gaya musu abin da yaya ussy ya gaya mini, suka ce eh haka ne wai ciki ne da ni, ka ga cikina ma ya fara kumbura yanzu ya zan yi bana son a koreni dan Allah ya zan yi" ta yi maganar har cikin zuciyarta tana rushewa da kuka.
Sai da ya dawo sannan ya ce ta tashi, kuma ya ce mata washegari za su gauraya.
Tana miƙewa tsaye jiri ya kwasheta sai amai, Gwaggo ta fito da sauri ta kama ruma, kanta sai juyawa yake saboda azabar wahala.
A zaune ta yi alwala tayi sallar isha'i, ko abinci ba ta nema ba, ta kwanta saboda galabaita, cinyoyinta sai azabar ciwo suke yi mata, dama da fari suna ciwo saboda hawan keke, gwiwoyinta na raɗaɗi saboda duk ta ƙuje su saboda keke, yanzu kuma ga kamun kunne, jikinta kamar an mata duka haka take jin ta, a take wani irin wahalallen bacci ya kwasheta.
Sai dai kwana ta yi da wani irin zazzafan zazzaɓi, wanda ita kanta ba ta san ya hau ta ba, jin surutan ta ya yi yawa a baccin ne ya sanya mama zuwa ta taɓa jikinta, ta ji da zafi sosai.
Duk da mama a ƙule take da ruma, haka ta fita ta ɗebo ruwa ta sanya ɗan ƙaramin towel, ta din ga shafawa ruma ruwa a jikinta.
Tun asubar fari kuwa, ruma amai ne ya tasheta, saboda har a lokacin jiri take yi.
Yanzu ma a zaune ta yi sallar asuba, ta nemi wuri ta kwanta.
Tun mama na basar da ita, har kuma ta fara damuwa, Gwaggo kuwa ta samu wuri É—aya ta zauna sai mita take na masifa a kan mama tana gani aka bawa ruma gwale-gwale amma ba ta ce komai ba.
Bayan gari ya gama wayewa, Gwaggo ta karya ta yi haramar tafiya, sai dai a lokacin ruma ta samu bacci, dan a galabaice take. Gwaggo ta ce kar a tasheta, Abdallah ya tafi rakata tasha, suna ta murna zasu huta, dan dama Gwaggon ta ishe su, ruma ce kawai take son zamanta a gidan.
Mama ta tashi ruma, ta matsa mata a kan lallai ta ci Abinci, ta na ci tana kuka ta É—an sha tea kaÉ—an ta kuma kwanciya, sai dai ko mintuna goma ba ayi da cin Abincin na ta ba, ta tashi ta cigaba da amai.
Ba shiri mama ta ce Aliyu ya zo ya kai ruma chemist a dubata.
Da ƙyar take iya tafiya, suna tafe tana kuka, har sai da ran Aliyu ya fara ɓaci, amma ya shareta suka cigaba da tafiya a hankali. Cikin sa'a kuwa suka tarar ya fito, kasancewar asabar ce, ranar ba ya zuwa aiki.
Ya na ganinsu cikin kulawa ya ce "Subhanallah, 'yar gidan mama yau ke ce ba lafiya?" Ita dai ba ta iya magana ba ta nemi wuri ta zauna. Aliyu ya zauna ya rungumeta, saboda ƙoƙarin faɗuwa take yi.
"Meya sameta haka?"
Aliyu ya ce "Ina ga zazzaɓi ne dai, da amai ta fara jiya"
Bakinta bai mutu ba, ta ce "Kamun kunne aka sakani, kusan awa goma shine ya sani rashin lafiya"
"Subhanallah, waye ya saki kamun kunne kuma?"
"Mai sunan Baba ne"
"To ki yi haƙuri, yanzu dai zan ɗibi jininki na yi miki gwaji, in duba meye ya haddasa zazzaɓin"
Ɗiban jinin da za'a yiwa ruma, tamkar za a cire mata ido, ta dinga kurma ihu, tana fizge-fizge, ga ta da shegen ƙarfi, da ƙyar Aliyu ya riƙeta aka ɗebi jinin nan.
Kuka har da majina, Aliyu ya dinga dungure mata kai yana zaginta.
Ya gama gwaje-gwajen da zai yi mata, ya ce "Malaria ce ke damunta, dan haka akwai buƙatar ayi mata allurai, da kuma magunguna"
Ruma ta yi masa zuru da ido, tana jiran ta ga a ina za ayi allaurar.
Ya haɗa alluransa ya nufo ta, ta miƙe tsaye.
"Ke malama ki tsaya, dan ba zaki sake wahalar da ni ba"
"To a ina za ayi mini allurar?"
Mai chemist ya ce "Ai a baya ake yin ta"
"Wai bayana" tayi maganar tana nuna bayanta.
Nasiru mai chemist ta ce "A'a a mazaunai"
"Suwaye mazaunan?"
Aliyu ya haÉ—e rai ya ce "Ke juya ki tsaya ayi miki allurar nan mu tafi, kin san sarai a in da za ayi".
Ta riƙe skirt ɗin ta gam ta ce "Ni wallahi ba zai ganni ba"
Aliyu ya fizgota, ya riƙeta da ƙyar suka danneta suka yi mata, Aikuwa ta din ga zunduma ihu, kamar sun mata wani abu.
Haka aka gama yi mata treatment, suka taho gida, ban da uban kuka babu abin da take yi.
"To subhanallah, ko me aka yi mata kuma take wannan uban kukan haka oho" mama ta yi maganar tana fitowa tsakar gida.
Aikuwa suna shigowa, ta nufi mama tana kuka.
"Meye haka, kukan me ki ke haka,ki ke ɓare baki?"
"Mama yaya Aliyu ne da Nasiru mai chemist"
"Suka yi miki me?"
"Bayan ya É—ibar mini jini, kuma suka buÉ—e mini tsiraici na aka yi mini allura"
Mama ta ce "Subhanallah"
"Mama ba ke ki ka ce ɗuwawu tsiraici bane ba, amma har da Yaya Aliyu ya riƙe ni, Nasiru mai chemist ya ganni, wallahi ban yafe ba"
Mama ta girgiza kai, ta ƙiftawa Aliyu ido sannan ta ce "Haba Haidara, ya zaka yi mini haka, dan me za'a buɗe mata jiki ayi mata allura?"
Aliyu ya ce "To mama ai larura ce, ko a addinance ba haramun bane".
Cikin masifa ta ce "To shi yayana ne da zai ganni? Har da taɓani ya yi mini allura a wurin"
Aliyu ya ce "Sa'anki ne ni, uban me za a kalla a jikin naki?"
"Wallahi ba zan taɓa yafewa ba, Allah ya jijjigo bala'in duniya da lahira ya ɗora masa, tun da ya ganan mini tsiraici na"
Mama ta ce"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace irin Addu'a ce haka, kar in kuma ji, baki san larura ba?"
Aliyu ya ce "Sakarya, kamar ba tsairaicin ki ka je kina kaÉ—awa a gaban mutane ba jiya"
Umar ya shigo É—akin mama, suna magana, bai kula ruma ba amma dan ya duba jikinta ya shigo.
Tana kwance ga zafin ciwo, ga na takaicin allurar da aka yi mata, zafin allaurar bai dameta kamar ganinta da mai chemist ya yi.
Sai da yamma mama ta sakata ta yi wanka, ta canza kaya ta ɗan ji ƙwarin jikinta.
Sai da ta kwana uku tana fama, sannan ta ware gaba ɗaya, sai dai rashin lafiyar da tayi ya sanya aka mance da laifin da ta tafka, kowa sai lallaɓata yake, ban da Huzaifa.
Ta ware sarai har ta koma makaranta, kullum mama cikin nasiha take yi mata, tare da yi mata addu'a da fatan shiriya.
Tun daga ranar ruma ta daina bi ta hanyar chemist É—in Nasiru, idan kuwa ta ganshi ko kallonsa ba ta yi, balle ta gaishe shi, a cewarta É—an iska ne tsairaicin ta ya kalla.
"Mama wai yaushe zaki haihu ne, babannin 'yan ajinmu sai haihuwa suke yi, amma ke ban taɓa ganin kin haihu ba"
Mama ta ce "Ikon Allah, ba gaki na haife ki ba, ai ke ce auta ha zan kuma haihuwa ba, sai dai in kin girma kin haifa na É—auka"
"To ni yaushe zan haihun?"
"Sai kin girma kin yi aure"
Ruma ta ɗan yi jimm sannan ta ce "To ni so nake na haihu, ina son ƙani ko ƙanwa da zan din ga wasa da su"
"Ruma ki ka haihu yanzu ai a nemi tsari, sai an yi aure ake haihuwa"
"To gaskiya mama ni so nake na haihu yanzu"
Usman da yake jin hirar ta su ya ce "Ke, idan ki ka haihu ba aure tsanarki za ayi, a kore ki daga gidan nan da unguwar ma gaba ɗaya, shi ya sa ba a wasa da maza, ki ka bari namiji ya taɓa ki to ciki zaki ki haihu, kuma korar ki za mu yi"
Waro ido ruma tayi ta ce "Amma ku kuke taɓani?"
"Ai mu yayyenki ne, muharramanki ne mu"
Ruma ta dafe ƙirji ta ce "Allah ya rufa mini asiri, ai da ban sani ba, taɓ idan aka koreni ina zani?"
"Oho miki dai, wannan damben da ki ke da maza ma, idan ba ki daina ba, sai dai ki ga kin haihu, kuma sai kin bar mana gida"
Ta yi ajiyar zuciya ta ce "In sha Allah hakan ma ba zata faru ba, ai ni ban san hakan abin yake ba, Allah ya sa na yi tsawo na auri kyakykyawa mai kuÉ—i".
Mama ta ce "Ke zan ci ubanki ke da kyakykyawa mai kuɗin nan, miji na gari ake roƙon Allah, fitsararriya"
"Ni dai gaskiya bana son mummuna, mai kyau nake so"
"Ke dalla ware, da wannan munin za ki auri kyakykyawa?"
"Ni dai yaya Ussy, ka yi mini Addu'a, ka san wa zan aura a cikin 'yan ball".
Miƙewa ya yi ya ce "Ba ni da lokacin jij wannan shirmen na ki".
Tun daga wannan lokacin, ruma take kaffa-kaffa, da gudun kar wani namiji ya taɓa ta, saboda kar ta haihu a koreta ta shiga uku, kuma ta san idan aka koreta ba kuɗin mota za a bata ba, balle ta tafi ko ƙauye ne wurin Gwaggo.
Yau gaba É—aya mama ta kasa gane kan ruma, tun da ta dawo daga makaranta yanayinta ya nuna kamar tana cikin damuwa.
Ba irin tambayar da mama ba ta yi mata ba, amma ta ƙi gayawa maman dalilin damuwarta ta, ta ce cikinta ne yake yi mata ciwo kawai
Mama ta aiki ruma sayen maganin sauro, ta je ta sayo, ta dawo ta tsaya a soro tana kuka.
Huzaifa ne ya sameta a soron tana kuka, dan sai da ya É—an tsorota.
"Ke me ki ke yi a nan?"
Cikin kuka ta kira sunansa "Huzaifa"
"Na'am" ya amsa.
"Ka san wani abu?"
"A'a sai kin faÉ—a"
"Yaya Usyy ne ya ce mini idan namiji ya taɓani, zan yi ciki in haihu, kuma korata za ayi daga gidan nan, sai malam ya aikeni karɓo masa chalk, da na kawo masa hannunsa ya taɓa nawa. Na tambayi 'yan babban aji na gaya musu abin da yaya ussy ya gaya mini, suka ce eh haka ne wai ciki ne da ni, ka ga cikina ma ya fara kumbura yanzu ya zan yi bana son a koreni dan Allah ya zan yi" ta yi maganar har cikin zuciyarta tana rushewa da kuka.