Sashe 112
Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Adam ya amsa da Amin, ya miƙe ya ce "Bari zan shiga gari na ga Bashir, gobe in Allah ya kaimu zai bar gari, ina da muhimman abubuwan da zamu tattauna".
Jamil ma tashi yayi ya ce "bari nima na gangara gida, na gaida Alhaji, sannan na wuce gida sai sa safenku".
Jabir ya ce "To Allah ya bamu alkhairi"
Kamar yadda Jamil ya faÉ—a, gida ya wuce ya je ha gaida mama da turaki, sannan yayi aniyar tafiya gidansa, Samha ce ta bi yo shi, tana kiran sunansa.
Ya tsaya yana jiran isowarta, ko sa ta ƙaraso, hannunsa ta ja ta ce "Mu je motarka mu yi magana" bai musa mata ba suka wuce motarsa, suka shiga.
Shiru ne ya É—an ratsa, daga bisani ya É—an numfasa ya ce "Ina jinki"
Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "A duniya bayan mama bani da wani kamarka yaya jamil, mama ta kasa fahimta ta, ban sani ba ko kai zaka fahimceni, domin kuwa kaine dai-dai da zamanin da muke ciki"
Jamil ya ce "Haka ne, ina saurarenki".
"Yaya jamil game da takawa ne"
Ya dubeta ya ce "Takawa again, me kuma ya faru?".
"Maganar nan ce dai ta shekarun baya, tun da Aisha ta mutu ina son maye gurbinta, na so na je wurin baba da kaina, amma sai na ga rashin dacewar hakan, ka taimaka yaya kai kaÉ—ai zaka fahimci halin da nake ciki"
"Wai ke samha ba zaki ƙyal adam ba kamar baki da zuciya? Duk cikin tarin samarinki babu wanda zaki fitar ki aura sai shi dai?"
Kamar ta fashe da kuka ta ce "Da zan iya cire shi daga zuciyata da tuni na yi, dan Allah ka taimakeni yaya jamil"
Jamil ya É—an yi shiru sannan ya ce "Zan fara yi wa adam É—in maganar na ji mai zace"
Da sauri ta ce 'A'a dan Allah kar ka gaya masa yanzu, turaki zaka fara yi wa zancen"
"To amma kin san magana yanzu ba zata yiwu ba, tun da haryanzu ana cikin alhinin mutuwar nan"
"Ohhj God, to sai zuwa yaushe kenan?"
'dole ki yi haƙuri, lokaci ya ɗan tura kaɗan"
"To shikenan na gode, ina saurarenka ka gaida gida " ya jinjina mata kai, ita kuma ta buÉ—e motar ta fita, tana jin a jikinta kamar a wannan karon za ayi nasara.
Kamar wutar daji, haka Zancen mutuwar aisha, ya cigaba da zaga gidan jaridu, da kuma kafafen watsa labarai, yayin da ta ɓangarensa yaƙi cewa kowa komai, kuma yaƙi magana da kowane ɗan jarida.
A yau babu tsammani, mai girma turaki ya karɓi baƙuncin wambai da misalin ƙarfe tara na dare.
Turaki yayi mamakin ganin ɗan uwan nasa a wannan lokacin, amma ya ɓoye mamakinsa, ya karɓe shi.
Wambai ya ce "Na san zaka yi mamakin ganina a wannan lokaci, sai da ba komai ne ya kawoni ba, illa zuwa in sake tabattar da abun da kunnuwana suke jiye mini, kuma ka yi burus, ba ka ce da ni komai ba"
Cikin rashin fahimta, turaki ya ce "Meke nan kake nufi?"
"Maganar rasuwar Æ´ar wurinka aisha mana, ko kai ba ka jin jita-jitar da ke ta yawo a kan mutuwarta?"
Turaki yayi murmushi ya ce "Alhamdilillah, da kai da kanka ka ce jita-jita ne, nima haka nan na tsinci zancen"
"Turaki na zuwa na yi domin mu yi wasan barkwanci ba, gaskiyar lamari zaka sanar mini, gaba É—aya mutuncin masarauta na nema ya zube, martaba da kimar gidanmu adam na ta cigaba da rusata sa shi da uwarsa, wannan wane irin abu ne?"
Turaki ya girgiza kai ya ce "Na san mai ɗakina ce ta je ta gaya maka wasu abubuwan, maganar da ke yawo a gari, tabbas aisha ta mutu a hannun 'yan bindiga, amma ba adam ne sila ba, ko ya kasheta ya sha jininta ba kamar yadda maƙiya ke ta kwarmato, kuma yarinyar da aka tsaresu tare ta zo da yaron wurin aisha".
"Turaki kana nufin goya masa baya wurin ɓoye laifinsa, dan me za a ce a ƙasar waje ta mutu a ɓoye gaskiya, wannan banzan aikin da yake yi na shishshigi ga manyan ƙasar nan da kawo ƙarshensu, ai gashi shi zasu kawo ƙarshensa, ko iya wannan labarin an yi mana mummunan tambari, a ce an samu babbar zuriya kamar ta mu da ƙarya. Dan haka dole a hukunta adam, sai ya yi wa duniya bayanin yadda matarsa ta mutu domin wanke ahalinmu daga mummunan zargin tsafi da kisan kai, ga uwa uba ayar tambaya a kan yaron da ake ce nasa ne, na baku awanni arba'in da takwas, idan har bai yi abun da na ce ba, matakin da zan ɗauka a kan sa ba zai yi muku daɗi ba.
Kai banda tsabar rashin sanin ciwon kai, kamar ba Æ´arka ba wane irin abu ne haka?"
Turaki ya ce "Da Adam da A'isha, duk tsatso É—aya ne, kuma Æ´aÆ´anmu ne, dukkansu.....
Bai ƙarasa ba, wambai ya ɗaga masa hannu tare da faɗin. "Ba nasiha nake buƙata ko tunatarwa ba, martabar ahalinmu da sarautarmu nake ƙoƙarin karewa, dan haka ayi abun da muka umarta, ko a ga ba dai-dai ba"
Turaki yayi ajiyar zuciya, ya bi wambai da kallo, da ya tashi fuuuu ya fice.
Yayi ajiyar zuciya yana jin wani irin matsanancin tausayin Adam.
Duk wannan kumfar bakin da wambai yayi, ya biyo bayan ziga da kuma famfon da Mummy ta je har gida ta yi masa tare da taimakon hajiya sauda, shi kuma kamar kullum ya hau kai ya zauna ba tare da bincike ba.
Rumaisa har islamiyya ta koma, in da malamai da ɗalibai suka din ga yi mata barka da arziki na kuɓutowa daga hannun ƴan bindiga, sai dai a wannan karon ma, duk yadda ƴan bugun ciki, suka so ta basu labarin abun da ya faru da ita ƙi ta yi, wasu har suna cewa rumaisa ta koma saliha.
Bayan tashi daga islamiyya, ta wuce gidansu habiba, dan tun da ta dawo ba ta je gidan su habiba, suka rungume juna suna tsalle a tsakar gida.
Daga bisani suka zauna suka hau hira, mamansu habiba ta zubo musu É—an wake, suka kewaye suna ci suna hira.
"Ruma ina yaya Aliyu ne?"
Ruma ta kalleta ta ce "Meyasa ki ke nemansa?".
"A'a, tun a asibitin nan ban kuma ganinsa ba"
"To meye haÉ—inki da shi, to idan son sa ki ke yi, zaki dinga sai mini kayan daÉ—i kina bani"
Waro ido habiba ta yi ta ce "Astagfirullah, dan Allah ruma ki daina yi mini haka, baki san kirkin da ya yi mini ba lokacin da nake zuwa gidanku da ki ka ɓata, mai sunan baba yayi ta hararata, shi yake rarrshina ya dawo da ni gida".
Ruma ta kwashe da dariya, ta ce "Allah sarki habibata, kamar ba nan muke kwasar dambe da ke ba, ke ni shawara zaki bani ma"
"Shawarar me" habiba ta yi maganar tana suÉ—e hannunta.
"Mutumin nan da ya ƙwace mini jaririna, wai ya zan yi da shi ne in karɓo ɗana?"
"Wai ƙwace jaririn suka yi gaba ɗaya to saboda me?"
"Saboda wulaƙanci mana, kullum da tunanin yaron nan nake kwana nake tashi, babarsa fa cewa ta yi ta bar mini shi, amma ya ƙwace mini shi. Habiba kin san in da kotu take? Ƙararsa zan je na kai, ba dama an ce zulai ta kai ƙara kotu alƙali ya bata ɗan ta ba, to nima kotu zan kai shi".
Habiba ta É—an yi shiru ta ce "Tsoro nake ji ruma, kin san ba a wasa a kotu"
"Na sani, ai ba wasa zamu je ba, ƙara zamu kai".
Habiba ta ce "To, a unguwar su babanmu akwai kotu, dama za ayi sauka a gidan, sai ki zo mu je".
Ruma ta yi murmushi ta ce"Amma na ji daɗi habiba, Allah ya kaimu in sha Allah sai an bani ɗa na, bari na tafi gida" ta miƙe suka fita tsakar gida suka wanke hannu, ta yi wa maman Habiba sallama sannan ta tafi gida.
Idan har da wanda za'a zarga a kan mutuwar aisha, to ba kowa bane ba face ni mahaifinta, domin ni na ɓoye ainihin abun da ya faru, adam ba matsafi ba ne, bai kashe aisha ba, kuma bai yi tsafi da gangar jikinta ba, a madadinsa, ina mai baiwa al'umma haƙuri na ɓoye haƙiƙanin gaskiyar abun da ya faru.
Mummy ta yi jifa da wayar hannun ta, bayan kammala karanta abun da turaki ya sanar da Æ´an jarida, ya wanke adam.
Ayshercool.
*Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*
Masifa mummy take kamar ta ari baki, duk ƙoƙarin da ta yi, amma turaki lokaci ɗaya ya watsa komai.
Takawa ma mamaki ne ya kama shi, da ganin abun da turaki ya ce, ya wanke shi ya É—au laifin, bai jira komai ba ya tafi gidan turaki.
Bayan an yi masa iso ya shiga sun gaisa da turaki, ya dubi turaki ya ce "Allah ya baka yawan rai, na ga abun da ka gayawa manema labarai, amma ni yakamata na ɗau wannan laifin na magantu ba kai ba".
Turaki ya murmusa ya ce "A'a mu ɗin ne dai yakamata, wambai ya zo nan ya nemi mu sanya ka fito duniya ka bayar da haƙuri, a kan abun da ya faru, wai sunan masarauta na neman ɓaci saboda kai, hakan ya sanya ni na bayar da haƙurin, kar ka ji komai"
"Amma Allah ya taimake ka..."
Turaki ya girgiza wa adam kai ya ce "An rufe wannan babin, ina Æ´a ta?"
Adam ya ce "Wace Æ´ar ta ka?"
Turaki yayi murmushi ya ce "Ƴa ta yarinyar da ta kawo jikana, rumaisa"
Adam ya É—an tsuke fuska ya ce "Tana gidansu"
"Allah sarki, duk lokacin da aka ganta, ace muna gaisuwa, Allah ya ƙara mata lafiya" turaki yayi maganar yana murmushi, yana tuna lokacin da rumaisa ta zauna a gabansa tana ta zuba shirme son ranta.
Jamil ma tashi yayi ya ce "bari nima na gangara gida, na gaida Alhaji, sannan na wuce gida sai sa safenku".
Jabir ya ce "To Allah ya bamu alkhairi"
Kamar yadda Jamil ya faÉ—a, gida ya wuce ya je ha gaida mama da turaki, sannan yayi aniyar tafiya gidansa, Samha ce ta bi yo shi, tana kiran sunansa.
Ya tsaya yana jiran isowarta, ko sa ta ƙaraso, hannunsa ta ja ta ce "Mu je motarka mu yi magana" bai musa mata ba suka wuce motarsa, suka shiga.
Shiru ne ya É—an ratsa, daga bisani ya É—an numfasa ya ce "Ina jinki"
Ba tare da ta kalleshi ba ta ce "A duniya bayan mama bani da wani kamarka yaya jamil, mama ta kasa fahimta ta, ban sani ba ko kai zaka fahimceni, domin kuwa kaine dai-dai da zamanin da muke ciki"
Jamil ya ce "Haka ne, ina saurarenki".
"Yaya jamil game da takawa ne"
Ya dubeta ya ce "Takawa again, me kuma ya faru?".
"Maganar nan ce dai ta shekarun baya, tun da Aisha ta mutu ina son maye gurbinta, na so na je wurin baba da kaina, amma sai na ga rashin dacewar hakan, ka taimaka yaya kai kaÉ—ai zaka fahimci halin da nake ciki"
"Wai ke samha ba zaki ƙyal adam ba kamar baki da zuciya? Duk cikin tarin samarinki babu wanda zaki fitar ki aura sai shi dai?"
Kamar ta fashe da kuka ta ce "Da zan iya cire shi daga zuciyata da tuni na yi, dan Allah ka taimakeni yaya jamil"
Jamil ya É—an yi shiru sannan ya ce "Zan fara yi wa adam É—in maganar na ji mai zace"
Da sauri ta ce 'A'a dan Allah kar ka gaya masa yanzu, turaki zaka fara yi wa zancen"
"To amma kin san magana yanzu ba zata yiwu ba, tun da haryanzu ana cikin alhinin mutuwar nan"
"Ohhj God, to sai zuwa yaushe kenan?"
'dole ki yi haƙuri, lokaci ya ɗan tura kaɗan"
"To shikenan na gode, ina saurarenka ka gaida gida " ya jinjina mata kai, ita kuma ta buÉ—e motar ta fita, tana jin a jikinta kamar a wannan karon za ayi nasara.
Kamar wutar daji, haka Zancen mutuwar aisha, ya cigaba da zaga gidan jaridu, da kuma kafafen watsa labarai, yayin da ta ɓangarensa yaƙi cewa kowa komai, kuma yaƙi magana da kowane ɗan jarida.
A yau babu tsammani, mai girma turaki ya karɓi baƙuncin wambai da misalin ƙarfe tara na dare.
Turaki yayi mamakin ganin ɗan uwan nasa a wannan lokacin, amma ya ɓoye mamakinsa, ya karɓe shi.
Wambai ya ce "Na san zaka yi mamakin ganina a wannan lokaci, sai da ba komai ne ya kawoni ba, illa zuwa in sake tabattar da abun da kunnuwana suke jiye mini, kuma ka yi burus, ba ka ce da ni komai ba"
Cikin rashin fahimta, turaki ya ce "Meke nan kake nufi?"
"Maganar rasuwar Æ´ar wurinka aisha mana, ko kai ba ka jin jita-jitar da ke ta yawo a kan mutuwarta?"
Turaki yayi murmushi ya ce "Alhamdilillah, da kai da kanka ka ce jita-jita ne, nima haka nan na tsinci zancen"
"Turaki na zuwa na yi domin mu yi wasan barkwanci ba, gaskiyar lamari zaka sanar mini, gaba É—aya mutuncin masarauta na nema ya zube, martaba da kimar gidanmu adam na ta cigaba da rusata sa shi da uwarsa, wannan wane irin abu ne?"
Turaki ya girgiza kai ya ce "Na san mai ɗakina ce ta je ta gaya maka wasu abubuwan, maganar da ke yawo a gari, tabbas aisha ta mutu a hannun 'yan bindiga, amma ba adam ne sila ba, ko ya kasheta ya sha jininta ba kamar yadda maƙiya ke ta kwarmato, kuma yarinyar da aka tsaresu tare ta zo da yaron wurin aisha".
"Turaki kana nufin goya masa baya wurin ɓoye laifinsa, dan me za a ce a ƙasar waje ta mutu a ɓoye gaskiya, wannan banzan aikin da yake yi na shishshigi ga manyan ƙasar nan da kawo ƙarshensu, ai gashi shi zasu kawo ƙarshensa, ko iya wannan labarin an yi mana mummunan tambari, a ce an samu babbar zuriya kamar ta mu da ƙarya. Dan haka dole a hukunta adam, sai ya yi wa duniya bayanin yadda matarsa ta mutu domin wanke ahalinmu daga mummunan zargin tsafi da kisan kai, ga uwa uba ayar tambaya a kan yaron da ake ce nasa ne, na baku awanni arba'in da takwas, idan har bai yi abun da na ce ba, matakin da zan ɗauka a kan sa ba zai yi muku daɗi ba.
Kai banda tsabar rashin sanin ciwon kai, kamar ba Æ´arka ba wane irin abu ne haka?"
Turaki ya ce "Da Adam da A'isha, duk tsatso É—aya ne, kuma Æ´aÆ´anmu ne, dukkansu.....
Bai ƙarasa ba, wambai ya ɗaga masa hannu tare da faɗin. "Ba nasiha nake buƙata ko tunatarwa ba, martabar ahalinmu da sarautarmu nake ƙoƙarin karewa, dan haka ayi abun da muka umarta, ko a ga ba dai-dai ba"
Turaki yayi ajiyar zuciya, ya bi wambai da kallo, da ya tashi fuuuu ya fice.
Yayi ajiyar zuciya yana jin wani irin matsanancin tausayin Adam.
Duk wannan kumfar bakin da wambai yayi, ya biyo bayan ziga da kuma famfon da Mummy ta je har gida ta yi masa tare da taimakon hajiya sauda, shi kuma kamar kullum ya hau kai ya zauna ba tare da bincike ba.
Rumaisa har islamiyya ta koma, in da malamai da ɗalibai suka din ga yi mata barka da arziki na kuɓutowa daga hannun ƴan bindiga, sai dai a wannan karon ma, duk yadda ƴan bugun ciki, suka so ta basu labarin abun da ya faru da ita ƙi ta yi, wasu har suna cewa rumaisa ta koma saliha.
Bayan tashi daga islamiyya, ta wuce gidansu habiba, dan tun da ta dawo ba ta je gidan su habiba, suka rungume juna suna tsalle a tsakar gida.
Daga bisani suka zauna suka hau hira, mamansu habiba ta zubo musu É—an wake, suka kewaye suna ci suna hira.
"Ruma ina yaya Aliyu ne?"
Ruma ta kalleta ta ce "Meyasa ki ke nemansa?".
"A'a, tun a asibitin nan ban kuma ganinsa ba"
"To meye haÉ—inki da shi, to idan son sa ki ke yi, zaki dinga sai mini kayan daÉ—i kina bani"
Waro ido habiba ta yi ta ce "Astagfirullah, dan Allah ruma ki daina yi mini haka, baki san kirkin da ya yi mini ba lokacin da nake zuwa gidanku da ki ka ɓata, mai sunan baba yayi ta hararata, shi yake rarrshina ya dawo da ni gida".
Ruma ta kwashe da dariya, ta ce "Allah sarki habibata, kamar ba nan muke kwasar dambe da ke ba, ke ni shawara zaki bani ma"
"Shawarar me" habiba ta yi maganar tana suÉ—e hannunta.
"Mutumin nan da ya ƙwace mini jaririna, wai ya zan yi da shi ne in karɓo ɗana?"
"Wai ƙwace jaririn suka yi gaba ɗaya to saboda me?"
"Saboda wulaƙanci mana, kullum da tunanin yaron nan nake kwana nake tashi, babarsa fa cewa ta yi ta bar mini shi, amma ya ƙwace mini shi. Habiba kin san in da kotu take? Ƙararsa zan je na kai, ba dama an ce zulai ta kai ƙara kotu alƙali ya bata ɗan ta ba, to nima kotu zan kai shi".
Habiba ta É—an yi shiru ta ce "Tsoro nake ji ruma, kin san ba a wasa a kotu"
"Na sani, ai ba wasa zamu je ba, ƙara zamu kai".
Habiba ta ce "To, a unguwar su babanmu akwai kotu, dama za ayi sauka a gidan, sai ki zo mu je".
Ruma ta yi murmushi ta ce"Amma na ji daɗi habiba, Allah ya kaimu in sha Allah sai an bani ɗa na, bari na tafi gida" ta miƙe suka fita tsakar gida suka wanke hannu, ta yi wa maman Habiba sallama sannan ta tafi gida.
Idan har da wanda za'a zarga a kan mutuwar aisha, to ba kowa bane ba face ni mahaifinta, domin ni na ɓoye ainihin abun da ya faru, adam ba matsafi ba ne, bai kashe aisha ba, kuma bai yi tsafi da gangar jikinta ba, a madadinsa, ina mai baiwa al'umma haƙuri na ɓoye haƙiƙanin gaskiyar abun da ya faru.
Mummy ta yi jifa da wayar hannun ta, bayan kammala karanta abun da turaki ya sanar da Æ´an jarida, ya wanke adam.
Ayshercool.
*Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*
Masifa mummy take kamar ta ari baki, duk ƙoƙarin da ta yi, amma turaki lokaci ɗaya ya watsa komai.
Takawa ma mamaki ne ya kama shi, da ganin abun da turaki ya ce, ya wanke shi ya É—au laifin, bai jira komai ba ya tafi gidan turaki.
Bayan an yi masa iso ya shiga sun gaisa da turaki, ya dubi turaki ya ce "Allah ya baka yawan rai, na ga abun da ka gayawa manema labarai, amma ni yakamata na ɗau wannan laifin na magantu ba kai ba".
Turaki ya murmusa ya ce "A'a mu ɗin ne dai yakamata, wambai ya zo nan ya nemi mu sanya ka fito duniya ka bayar da haƙuri, a kan abun da ya faru, wai sunan masarauta na neman ɓaci saboda kai, hakan ya sanya ni na bayar da haƙurin, kar ka ji komai"
"Amma Allah ya taimake ka..."
Turaki ya girgiza wa adam kai ya ce "An rufe wannan babin, ina Æ´a ta?"
Adam ya ce "Wace Æ´ar ta ka?"
Turaki yayi murmushi ya ce "Ƴa ta yarinyar da ta kawo jikana, rumaisa"
Adam ya É—an tsuke fuska ya ce "Tana gidansu"
"Allah sarki, duk lokacin da aka ganta, ace muna gaisuwa, Allah ya ƙara mata lafiya" turaki yayi maganar yana murmushi, yana tuna lokacin da rumaisa ta zauna a gabansa tana ta zuba shirme son ranta.