← Book details Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 114

Sashe 4

Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe baki tayi, ta ce "Allah dai ya biya da aljanna, gadanga na Mama" ta É—au kofin kununta ta turawa Mama kunun ta ce "Mama ki shanye kunun na bar miki" tayi waje.

***
Da ƙyar ta ƙarasa makaranta yau, saboda ciwon cinyoyi da take yi, sakamakon horon da Yaya Umar ya bata a daren jiya.

"Ruma hatsari kika yi ne?" Cewar wata matashiyar yarinya sa'ar Ruman, gannin yadda take tafiya da ƙyar.

Ta haÉ—e rai ta ce "Me kika gani?"

"Gani nayi kina tafiya da ƙyar, kamar wadda ta warke daga karaya"

Cikin gatse Ruma ta ce "Eh, tirela ce tabi ta kaina, da ta wuce na taso na taho"

"A'a Allah ya baki haƙuri"

Duk da yadda jikinta babu daɗi, hakan bai hanata faɗace-faɗace da neman rigima ba, dan idan ba tayi hakan ba ace lafiyarta ƙalau ba.

Bayan an tashi ba ta tsaya ko ina ba ta tafi gida, tana zuwa ta tarar da katifarta a tsakar gida kamar yadda ta barta.

"Mama yanzu dan Allah a nan aka bar mini katifata, sai anyi baƙi sun tambayi ba'asi ace fitsarin kwance nayi?"

"Au ba ke kika yi ba, ni nayi kenan?"

Ta ƙarasa ta zauna a kusa da Mama ta ce "Haba Mama, kema fa kin san tsautsayi ne, rabona da fitsarin kwance tun ina jairiya, tun ban fi wata huɗu ba na daina fitsarin kwance" wani irin kallo Mama tayi mata, jin uwar ƙaryar da ta saki.

Mama ta ce "Tashi ki cire Uniform, kiyi wanka ki zo kiyi salla, ki tsefe wannan kan naki, ƙazamar banza da yake ban yi magana ba, baki ga dama kin mayar da kai kin tsefe ba, kuma wallahi ya kai gobe in Allah ya kaimu baki gama tsifar nan ba, sai na zaneki".
Hannu ta saka ta shafa kanta, ƙanann kitso ne a kanta, a ƙalla guda arba'in da ɗoriya, Mama ta bata kuɗi ta je ayi mata kitson hannu guda biyar, saboda ba ta son tsifa, amma ta karɓi kuɗi a wurin Yaya Usman ta je aka yi mata ƙanana.
Ta san yau ko Mama zata kwaɗanta ta ta cinye ba zata iya gama wannan tsifar ba, haka nan ta tashi ta je ta yi wanka, ta yi alwala ta saka wasu kayan. Ganin Mama ta tada salla, ta leƙa Window ta ga Usman da sallaya a hannu zai tafi masallacin juma'a, ta ɗau hijjabinta ta bi bayansa.
Sai da ta fito ƙofar gida sannan ya kalleta ya ce "Ina zaki?"

"Masallaci mana" ta bashi amsa.

"Kin tambayi Mama?"

Ta gyaÉ—a masa kai alamar eh.

Ya ce "Shikenan muje" ya sanyata a gaba suka tafi masallaci.

Mama ta daÉ—e tana yiwa Rumaisa Addu'a bayan ta idar da salla, kullum cikin Addu'a take yi mata, amma tana girma tamkar ana sake turata, ko alamar hankali babu a tare da Rumaisa.

Da suka dawo daga masallaci tana kallon Rumaisa, ba ta ce mata uffan ba, Rumaisa sai raragefe take yi, tana sauraron ko Mama zata yi mata magana amma taga ta shareta.

Ba tare da ta yi tsifar ba, ta ci Abincin ranarta tare da Yaya Aliyu, ya siyo kifi É—auri biyu, ya bawa Mama É—aya ya ce gashi nan duka gidan, É—auri É—aya kuma suka ci shi da Rumaisa.

Bayan sallar la'asar, ta É—au allonta ta tafi makarantar allo.
Tana zuwa Habiba ta tare ta da harara, tare da sheda mata cewar Sani ya ce sai ya yi mata dukan tsiya, idan ba ta biya shi tayarsa ba.
Tsaki Rumaisa tayi ta ce "To, ya kasheni ya huta mana, tayar banza da ta wofi, shi bai san tsautsayi ba"

A ƙufule Habiba ta ce "Au hakama zaki ce? Ki zo girma da arziki na ara miki tayar, amma ki je ki ɓatar ko a jikinki?"

"To tayar da kuÉ—i ya saya? Idan da kuÉ—i ya saya ya faÉ—i kuÉ—inta, yayyena su biya shi"

Habiba da ta gama fusata ta ce "Dalla can, uwar meye a gidan naku, banda gayyar maza da tsiya, sai ka ce wata uwar kuka ajiye, har kike a faÉ—i kuÉ—in tayar a biya"

"Ku kun ajiye wata uwar É—in ne, da kuna da wani abun ai babarku ba zata sayar da fanke da safe ba" Tayi maganar tana murguÉ—a baki.

Cikin rawar murya Habiba ta ce "Kar ki sake ki zagar mana uwa"

"Ni ban zagi babarku ba, ni dai na san fanke take sayarwa, fanken naku ma mai Shegiyar tsada, ƙanana kamar ƙuli-ƙuli, dan ranar Yasir ya ce har kiyashi ya gani a cikin fanken" kan Rumaisa ta rufe bakinta, tuni Habiba ta shaƙo hijjabinta, zata rufeta da duka.
Abinka dai mai nema a duhu, balle ya samu a sarari, nan Rumaisa ta zage ƙwanji ta tabattarwa da Habiba ita ɗin ƘANWAR MAZA ce.
Abin takaici da malami a gefe yana biyawa wasu allo suka harƙe da dambe.
A fusace ya miƙe ya saka bulala ya zane musu jiki, musamman Rumaisa, tsabar masifarta ya sanya baya son ta a ajinsa, kullum cikin rigima take, ga allonta sai yayi wata ba tayi wani rubutun ba, ga daƙiƙanci da surutu.

Idan da abin da Rumaisa ta tsana bai wuce duka ba, ta ji zafin dukan bulalar da Malam Ashiru yayi mata  ba kaɗan ba, dan haka ta koma gefe tayi shiru tana kuka. Ta rasa meya sanya ya tsaneta haka.

Habiba kuwa da ƙawayenta, suka ƙudiri aniyar idan aka tashi sai sun naɗawa Rumaisa duka saboda suna jin haushinta suma, a kan damben da aka yi a ƙofar gidan mai markaɗe ranar Alhamis, gashi ta zagi fanken babar ƙawarsu.

Ana tashi cike da takaicin dukan da Malam yayi musu, Rumaisa ta É—au allonta ta nufi gida, sai share hawaye take. Sai dai yau babu tsokana a hanya, babu neman magana saboda bayanta sai raÉ—aÉ—i yake na dukan da malam yayi mata, gashi ba ta warke daga ciwon jikin punishment É—in Yaya Umar ba.
Babu tsammani ta tarar da su Habiba a wani lungu suna jiran isowarta.
Turus tayi tana binsu da kallo kamar ba ta sansu ba.

Babu ko ɗar ta cigaba da tafiya tana yinƙurin ratse su ta wuce.

Shan gabanta Habiba ta yi ta ce "Ke kin isa ki tafi, ba dai ni kika zaga ba, kika kuma zagi babarmu ba, wallahi yau sai kin gane kuskurenki, kuma wallahi Sani ma ya ce sai kin biya shi tayarsa.
ÆŠaya daga cikin yaran ta ce "Ai wallahi yau sai kin daku, haka nima ranar kika zubar mini da markaÉ—e, zaki gane baki da wayo".

Bin su Rumaisa take da ido, sai kurari suke amma an rasa wadda zata kaiwa Rumaisa duka.
Sake yinƙurin wucewa tayi, amma Habiba ta janyo Rumaisa ta baya, yaran suka fara kai mata duka.
Tayi kukan kura, ta É—aga allonta saukewa Habiba allonta a fuska, wani uban ihu Habiba ta kurma, jin danshi a hancinta.
Tamkar namiji a filin dambe, haka Rumaisa ta zage ita kaɗai ta dinga dukan yaran nan, yadda ta dunƙule hannu tana kai naushi, kai ba ka ce 'ya mace bace.

Da ƙyar da siɗin goshi wani mutum ya rabasu, saboda Rumaisa akwai taurin kai, zuciyarta a bushe ana rabasu tana cigaba da kai duka.
Ta É—au allonta ta nufi gida, tana ta huci, duk da dukan da tayi musu sai dai jikinta duk yayi tsami ita ma. Dama ga jikin nata babu daÉ—i ji

Sai dai kash, tuni wasu daga cikin yayyen yaran maza suka samu labari, suka yi gaba zasu datse Rumaisa a hanya, su zaneta.

Ayshercool
08081012143

[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA:                    ƘANWAR MAZA

      BY AISHA ADAM (AYSHERCOOL)

Ku yi subscribing YouTube channel É—in mu, domin samun daÉ—aÉ—an litattafan hausa na sauraro.
https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
Arewabooks @ ayshercool7724
Watpad@ ayshercool7724

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION

Page3

'yan matasan yaran maza sun girmi Rumaisa, kuma duk da haka ƙarfin namiji da na mace ba ɗaya bane ba.
Tana cikin tafiya ta ji ana ke!ke! Ta tsaya waiwaya ta ga da wa ake.

tawagar yara ta gani sun nufota gadan-gadan, tana ganinsu ta san masu dukanta ne, sam bata karaya ba, maimakon ta gudu sai ta durƙusa ta fara kwasar duwatsu, ta shirya duk wanda ya kawo kai, sai ta ƙwale masa kai da dutse.

Amma a haka sai da wasu daga cikin su suka cim mata.

Sani Yayan Habiba, ya na zuwa ya kwarfeta da ƙafarsa ta faɗi ƙasa, wani danƙo ya ɗauko a aljihunsa, ya fara dukanta da shi, duka take kai masa ko ta ina da allonta har ta samu ta tashi tsaye da ƙyar a kan ƙafafuwanta.

Ta yi kukan kura ta kafa masa haƙora a kafaɗarsa, tsananin azabar zafi ya sanya ya kurma wani uban ihu ya ja da baya, dan har ƙashinsa ya ji haƙoram Ruma, sai ka ce mayya.

Ganin ta gigita Sani, wasu daga abokan nasa kuma suna fama da raɗaɗin jifan da suka sha, ya sanya ta durƙusa ta ɗauki takalminta da hijjabinta a hannu, ta tsula da gudun tsiya.
Rufa mata baya yaran suka yi, suna a taro ta, amma kamar walƙiya haka take sheƙa da gudu, ba ta tsaya a ko ina ba sai da ta kai filin ball ɗin su Yaya Aliyu. Suna tsaka da ball, sai ratsa cikin ƙartin mazan nan take sai gata a tsakiyar filin da maza ke uban gudu suna ball, ta cinma Aliyu a tsakiyar filin ƙwallon ta rirriƙe shi.

Mamaki ne ya kama shi, ganin hijjabinta a hannu, kanta sai hula idanunta duk sun yo waje, tana ta haki tana waige-waige.

Riƙeta yayi yana tanbayarta lafiya? Wasu daga cikin abokansa suma suka tsaya suna tambayarta ko lafiya, amma taƙi magana sai ajiyar zuciya take yi.

Aliyu ya ja ta gefe, ya sanya mata hijjabinta, ya kalleta a tsanake ya ce 'Menene?" Shiru ta yi bata yi magana ba sai sauke numfashi take.

Haushi ne ya fara kama shi ya ce "Dan ubanki menene, me aka yi miki kika biyoni nan cikin maza?" Yayi mata maganar a hasale.
Chapter 4 · 0% Book details