← Book details Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 114

Sashe 1

Kanwar Maza Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

[16/06, 9:00 pm] JAKADIYAR AREWA:        ƘANWAR MAZA
 
              

Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER'S ASSOCIATES

Page1

Bismillahirahmanirrahim

Daji Ajiyar Allah! La'asar sakaliya, a lokacin da hasken rana ya fara disashewa, ta doshi yamma za ta faɗi, duhun magariba na ƙoƙarin shigowa ya maye ragowar hasken da ranar ta bari kan ta ƙarasa faɗuwa.
Gamayyar bishiyoyi ne, dogaye da da madaidaita, haɗe da ciyayi da ga mabanbantan tushe, suka haɗu suka yiwa dajin ƙawanya. Zai iya kasancewa abin sha'awa ga wanda ya zo yawon buɗe ido, idan har bai san mai dajin ya ƙunsa ba.
Ga wanda ya san abin da ya ƙunsa kuwa, zai kasance wuri mafi razani, firgici da kuma tashin hankali.
Gudu take yi a tsakanin rayuwa da mutuwa, tana rungume da wani zani a ƙirjinta, babu yadda za ayi daga nesa ka gane me ta rungumo haka take wannan uban gudun.
Ƙafafuwanta babu takalmi, jikinta babu mayafi, duk da yanayin garin babu zafi, amma laɓɓanta sun bushe tamkar dutsen da ya shekara ruwa bai zuba a kansa ba, babu alamar tana gane in da take jefa ƙafarta. Duk da wannan mawuyacin hali da take ciki, ta bawa abin da take rungume da shi muhimmanci sosai da sosai.
Cikin rashin sani, tayi karo da wani abu da ita kanta ba ta kai ga tantance ko meye ba, sai dai ƙarfi da nauyin abun ya sanya ta faɗi ƙasa, take ta saki wani marayan kuka, a lokacin da jini ya fara zuba daga ƙeyarta.
Sai a lokacin abin da take rungume da shi ya tsala kuka, saboda firgitar da ya yi shima.
Jariri ne ɗanyen goyo, cibinsa ko faɗuwa bai yi ba, jikinsa duk busashshen ƙazantar haihuwa da alama yaron ya kwan biyu, amma ko ruwa bai taɓa gani ba balle a wanke wannan ƙazantar!.

**************

Cikin garin Kano, unguwar ɗorayi tinga, misalin ƙarfe huɗu na yammacin ranar Alhamis, wani matsakaicin gida ne, cikin rukunin gidajen dake ɗan ƙaramin layin,  kallo ɗaya zaka yi wa gidajen, ka san na masu ƙaramin ƙarfi ne, duba da yanayin kwatoci da kuma kasancewar gidajen awon igiya, ba magudanan ruwa, babu layuka masu kyau, kowa da in da fuskar gidansa ta kalla, haka zalika kowa in da ya ga dama yake sako kwatar gidansa, wasu da gyara wasu babu, ga gidajen 'yan ƙanana tamkar wani zai hau kan wani.

"Wai ba zaki fito ki je mini aiken ba, har sai gawayin ya ƙare tukuna?" Cewar wata matashiyar dattijuwa, da take zaune a gaban kurfoti, hannunta riƙe da mafici tana firfitawa, gefe ga farantin silba ɗauke da garin tuwon masara a kai.

Wata  yarinya ce ta fito daga wani ɗakin da yake bayan matar, hannunta ɗaya riƙe da hijjabinta, ɗaya kuma sai matsar hawaye take yi.

Matar ta kalleta ta ce "Kukan me  ki ke yi?"

Aikuwa kamar mai jiran ƙiris, cikin sangarta yarinyar ta ce "Ba Huzaifa bane ba ya....

"Ni yi mini shiru, haka dai kuka iya faÉ—a kamar kuna ganin hanjin junanku, idan na hana ki zuwa in da yake ai ba zaki hanu ba, maza ki É—au kuÉ—in nan ki je mini gidan Laure, ta baki kuka ta sittin, daddawa ta arba'in sai manja na naira É—ari ki kawo mini canjin, na yi maza in kaÉ—a miyar nan kan magariba".

Kwaɓe fuska yarinyar ta yi ta ce "Wai yau ma miyar kuka za ayi Innalillahi wa innalillahi raji'un"

Baki buÉ—e ta bi Yarinyar da kallo, cikin hasala ta ce "Idan na kaÉ—a kukar kar ki sha, zaki É—au kuÉ—in ki fita ko sai na yi fatali da kanki a wurin?"

Ta durƙusa ta ɗau kuɗin, ta zura hijjabinta ta nufi hanyar fita, a ranta tana jin gara ace yau babu abin da zasu ci, da wannan tuwon kamar na ibada.

Cike da kashedi matar ta ce "Idan kin ga dama kuma ki je ki zauna, kar ki yi sauri kiga yadda zan yi da ke, ko ki biyewa yara ki tsaya shashanci a hanya"

Ba to ko waiwayo ba, ta yi gaba abinta tana kalle-kalle.

Gidansu ƙawarta Habiba ta fara biyawa, ta tarar da maman Habiba a tsakar gida ana yi mata kitso, ta durƙusa ta gaida Maman Habiba, sannan ta ce mata wurin Habiba ta zo.
Habiba ta fito daga ɗakinsu tana kallonta tana murmushi, ta ƙaraso in da take tsaye ta ce "Ruma ina zuwa ne?"

Cikin muryar RaÉ—a Ruma ta ce "Dan Allah Habiba aron tayar Sani zaki bani, Mama ce ta aikeni so nake nayi sauri na je na dawo".

Habiba ta ce "Kaii, Ruma kin san Sani yafi kashi É—oyi, kar na baki ki je ki salwantar da ita, daga ni har ke mu shiga uku".

Ruma cikin ƙwarin gwiwa ta ce "Wallahi ba zata salwanta ba, ke dai ki aramini, so nake na yi gudu na ne na dawo".

Habiba ta ja Ruma soron gidansu, ta duba saman kejin kajin da ke cikin É—an tsukakken zauren gidan, ta É—aukowa Ruma tayar Sani ta bata ta ce "Dan Allah Ruma ki kula, kar wani abu ya samu tayar nan, ki yi maza mi garata ki je ki dawo"

Ruma tayi murmushi ta ce "Kar ki damu, yanzu zan fyalla naje na dawo, ina son tayar nan ta sani dama ya bar mini, 'yar dandaɓasa da ita, yanzu zaki ga naje na dawo".

Habiba tayi murmushi ta ce "To shikenan, yi sauri kafin ya dawo".

Ruma ta dafe kan taya, ta garata ta dinga zura gudu ta lunguna kamar wata namiji ba mace, ba ta tsaya da gara tayar ba har sai da ta isa gidan Laure.
Ta yo sayayyarta ta gama, ta fito ta kuma garo taya zata tafi gida, can ta hango wasu 'yan makarantar allonsu, a ƙofar gidan Hanne mai markaɗe suna 'yanta, ba tare da ta tuna da kashedin Mama ba, ta ajiye kayan aiken da canjin haɗi da tayar da ta aro, ta shiga aka hau 'yanta da ita.

Kasancewar ƙwararriya ce a harkar shagala da iya rinto, nan da nan wasa ya ɗau zafi, ganin tana ta cinyesu a 'yantar ta hanyar rinto, sai wasa ya koma faɗa, daga nan aka hau dambe, a wurin Ruma ta kifar wa da wata markaɗenta ga ta da ƙarfi kamar doki. Da ƙyar wani mutum ya raba faɗan, Ruma ta haɗa yaran mutane ta zane musu jiki, sai da mutumin yayi mata barazanar zai gayawa yayanta, sannan ta haƙura da damben.

Yarinyar da suka yi damben, ganin an musu asarar markaɗe, an kifar ga duka, ya sanya ita da ƙannenta suka fasawa Ruma Manjan da ta sayo wa Mama, suka kwashe canjin aiken, suka farke ledar aiken suka gudu, daddawar ma sai da ƙyar ta tsinto wasu, an fasa ledar kuka duk ta watse.

Ta kwashi sauran kayan, ta tafi gida, tana tafe tana tunanin wace ƙaryar za ta jirgawa Mama, dan ta kaucewa faɗanta, dan a duniya ba ta son faɗan Mama, gefe guda kuma tana tunanin irin dukan da zata naɗawa Safiya idan suka haɗu a makaranta allo, saboda abin da suka yi mta.
Lokacin da Ruma ta isa gida tuni an fara kiraye-kirayen sallar magariba, domin wasu masallatan har sun tayar, sai a lokacin ta sake shan jinin jikinta, tsoro ya ziyarce ta.

A soro ta rakuɓe tana leƙa cikin gidan, ta hango Mama a gindin rariya tana alwala, Mama ta ɗaga ido tayi mata kallo ɗaya, ta mayar da kai ta cigaba da alwalarta.

Cikin sanÉ—a Ruma ta shiga tana satar kallon Mama, ta ji mai Maman za tace mata, amma ta ji ba tace mata komai ba.
Ta lallaɓa ta ajiye abin da yayi saura na aiken, ita ma ta faɗa banɗaki tayi alwala.
Ta lallaɓo falo, ta tsaya a bayan Mama ta tayar da sallar ita ma.
Mama ta idar, ta tashi ta fita tsakar gida, ta duba abin da Ruma ta kawo mata na aiken, taga irin aika aikar da Ruman ta yo.
Ta dawo falon tana jiran Ruma ta idar da salla ta dirar amata, amma Ruma ta ƙi idarwa, ta hau nafifilin babu gaira babu dalili, matar da wataran sallar ma sai Mama ta haɗa .mata da duka take yi, amma yau sai gashi har da nafila.

Can da Mama taga abin nata bana ƙare bane ba, sallar taƙi ƙarewa, ta damƙo wuyanta ta baya ta zaunar da ita, ta kalleta cikin haɗe fuska ta ce "Gidan uban wa ki ka je dana aike ki?"

Cikin tsoro Ruma ta girgiza kai ta ce "Ba ko ina Mama"

"Ƙarya kike yi, zaki gaya mini ko sai na murɗe miki wuya, tun la'asar na aike ki amma sai magariba kika shigo mini, gidan uban wa kika je?"

Cikin zazzare ido Ruma take jujjya kai tana rantse-rantsen rashin gaskiya, "Wallahi Mama ban je ko ina ba"

Cikin tsananin Fushi, Mama ta ce "Ba zaki gaya mini ba!"

"Mama wallahi dagaske nake"

"Assalamu alaikum" aka yi sallama a tsakar gida.

Mama ta amsa sallamar tana huci, wani matashin saurayi ne ya shigo É—akin, yana faÉ—in Mama na dawo".

Mama ta ce "Sannu da zuwa"

Ya amsa da yauwa, ya dubi Mama dake tsaye a kan Ruma, Ruma sai wulƙita ido take, kamar ta zagi sarki.

"Mama meyafaru ne?" Yayi Maganar yana son jin ba'asi.

Cikin ɗacin rai Mama ta ce "Saboda tsabar iskanci na yarinyar nan, nan da gidan Laure, ta je ta sayo mini kayan miya, tun bayan la'asar sai yanzu ta shigo mini gida, babu aiken babu dalilinsa, kuma babu canjina, nayi-nayi ta gaya mini in da ta tsaya amma taƙi faɗa sai rantse-rantse take yi".

Ya kalli Ruma ya ce "Ba zaki faÉ—i inda kika tsaya ba, kuma ina canjin? Ko zuwa ki ka yi ki ka kashe mata kuÉ—i tunda kin saba"

Cikin tsiwa da rashin kunya, Ruma ta ce "Ban sani ba, kai kuma waye ya saka da kai, zaƙin zaƙafere mai gida feraye kabewa, ai ba da kai ake yi.....
Kan ta ƙarasa Mama ta rufe bakin nata da duka, da sai da tayi zaton bakinta ya fashe.

Ja da baya tayi da sauri, ta dafe bakinta tana yarfe hannu, saboda ta ji zafin dukan nan sosai da sosai.
Chapter 1 · 0% Book details