← Book details Halysaah Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 180

Sashe 49

Halysaah Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

What is ur point??" Jay ya shafa sumar kansa a hankali yace "My point is, na kai Housemate dita dakin ka for the meantime before i find a way out, nasan can ne kadai su Aunty baza su ganta ba, tunda dakin ka out of bound ne" Haka AJ yayi dropping jaw yana kallon Jay baya ko kiftawa with shock written all over his face, Jay ya sosa kansa zai yi magana suka ji muryar Hajiya Rukayya warce suke kira da Aunty, ta karaso parlon tace "Jay ka je Abbanku na magana a parlor" Jay yace "To gani nan zuwa Aunty" Ta
an kalli AJ sannan ta juya ta bar parlon, Jay ya sauke ajiyar zuciya yana kallon AJ that was still looking at him ko kwakkwaran motsi baya yi, da alama ya ma kasa cewa komai, Jay yayi patting
in shoulder dinsa yace "I know u gat my back Bruh, you won't love seeing Abba Mad at me" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan Aunty yana sauke wani ajiyar zuciya, after almost 15 mins Jay ya dawo sama, zaune ya tarda AJ a parlon dake sama ya tallabi chin dinsa da duk hannunsa biyu yana girgiza kafa, he looks restless, Jay dai ya danne dariyar da ya taho masa da kamar zai juya ya koma downstairs, AJ na ganinsa ya mike ya nufesa a fusace ya fixgosa yace "What offense have i done to you Jawwad?

Why my room?

Why will u take her to my privacy, my own comfort zone, what sort of nonsense is this plss?

Dakina fa?

Meye hadina da ita zaka kai ta har Bedroom dina?" AJ was so mad at him, nan da nan idonsa suka sauya launi, Jay yace "To Abba dai na kiran ka, je ka dawo sai ka ci gaba" AJ dai sai kallonsa yake yana huci, can ya turasa ya bar parlon kamar zai tashi sama, Jay ya wara ido yana shafa kansa yana
an murmushi, karkari dai iya abinda zai yi kenan bazai wuce haka ba, kuma ba wani kiransa da Abba yake yi kawai wahala ne bai so yasa yace masa ana kiransa downstairs, dakin Khaleesat ya koma ya dauko mata box dinta da abubuwan da yasan zata yi needing ya kai dakin AJ, Khaleesat ta mike da sauri ganinsa, a hankali tace "But Housemate i am not comfortable in this room" ya
an bude ido yace "Why?

Meye da dakin Halysaah?" Tayi shiru bata ce komai ba, Calmly yace "C'mon Halysaah wannan ma ai yafi wancan da kike ciki" Yana murmushi ya kare maganar, ita dai tayi shiru bata ce komai ba, ya ajiye mata kayanta da wayarsa yace "If you need anything just call my line" Ta gyada masa kai, ya nuna mata hanyar bandakin dake babban dakin yace "In zaki yi sallah ga bandaki can" Nan ma dai ta gyada masa kai kawai, ya juya ya fita daga dakin ta koma ta zauna, gajiya tayi da zama tana son kwanciya amma ta kasa kwantawa saman gadon, ita kanta ta rasa dalili, can dai ta zamo kasa a hankali ta kwanta saman lallausan carpet dake dakin ai ko nan da nan bacci ya dauketa, throughout ranan haka Khaleesat ta yini a dakin ita kadai, tun da Housemate dinta ya kawo mata lunch har lokacin magrib yayi bai dawo dakin ba, sai Cook din gidan ne ya kawo mata dinner, tana zaune saman darduma bayan ta idar da sallahn isha taji an bude kofar dakin ta daga kai, sosai gabanta ya fadi ganin AJ, ta sauke idonta daga kallonsa, shi kam ko kallon inda take bai yi ba fuskarsa a murtuke ya tafi ya dau second phone dinsa da laptop, ya bude press dinsa ya dau pajamas dinsa sannan ya fice daga dakin, sai a sannan ta daga kai ta bi sa da kallo tana mamakin abinda ya shigo yi, don bata san me ma ya dauka a dakin ba, har sannan bata kawo cewar dakinsa bane, har ta fara bacci Jay ya shigo dakin da sallama, ta mike zaune daga kwancen da take a kasa, da mamaki yake kallonta yace "Me yasa kika kwanta a kasa Halysaah?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "C'mon don't do that pls, ga gado zaki wani kwanta a kasa" Ta kalli gadon tace "Zan kwanta" Yace "Good, hope u need nothing?" Tace "Bana bukatar komai" Yace "Alright then, good night" A hankali tace "Thank you" ya mata murmushi yace "In kashe maki wutan dakin ko a maida maki dim light?" Tace "Dim light" Ya mayar mata wutan mara haske sosai sannan ya juya ya fita daga dakin, bayan fitarsa ta koma tayi kwanciyarta a kasa, ita gani take kamar master bedroom din gidan ne, may be that's why she is not comfortable, wajen karfe dayan dare dakin yayi sanyi sosai amma taki daukan duvet din saman gadon ta rufa, kawai ta lullube da Hijab dinta, she was so cold gashi Safiyyah bata hado mata kayanta da Sweater ba, tana ta kwance ta kasa bacci saboda sanyin da ya dameta sai juye juye take taji an bude kofar dakin, a hankali ta sauke Hijab dinta kasa kadan tana son ganin wanda ya shigo don har kanta ta rufe, taga AJ ne ya shigo, kallo daya yayi mata ya tafi daukar abinda zai dauka, zaro ido tayi bayan ta zargi anya ba dakinsa bane nan kuwa, sai bayan da ya fita taji ya kullo kofar ta mike zaune tana sake bin dakin da kallo with shock, dumin da taji dakin ya fara dauka gradually ne yasa ta gane ya kunna mata heatern dakin, ta koma a hankali ta kwanta sai da dakin yayi dumi sannan bacci ya dauketa.....

Washegari da safe Jay na zaune main parlor tare da Abba da Aunty, cikin nutsuwa Abba ke masa magana amma shi gaba daya hankalinsa na sama kan Halysaah don tun da gari ya waye bai je wajenta ba, kawai dai Cook din gidan ne ya kai mata breakfast, AJ ya shigo parlon daga reading nook da yake zaune ya nufi dinning area zai yi breakfast, Abba ya bi sa da kallo, after a while yace "Baka yi breakfast din bane" Jay ya
an kalli AJ, Aunty kanta kallonsa take ita ma, without turning back AJ yace "Ban yi ba" Aunty tace "To ai naga cook din gidan ya kai maka Breakfast din sama daxu" Ko tankata AJ bai yi ba ya tafi dinning ya zauna, Abba na kallon Jay calmly yace "Is he Okay?" Jay ya
an shafa kai yayi kasa da murya yace "I think supervisor dinsa ne bai yi approving Article din da yayi publishing ba tukunna" Aunty tace "To banda abun sa ai ba wani abu bane he should add in more effort to his work kawai" Shi dai Jay bai ce komai ba, haka shi kansa Abba, after a while Jay ya mike ya tafi sama, direct part din AJ ya nufa bayan yayi sallama ya tura kofar dakin ya shiga.

Wajen la'asar AJ na zaune parlorn dake sama, gaba daya he look moody, dama jiya da daddare a nan parlorn ya kwana tsabar takaici, har zuwa yanzu yaki ce ma Jay komai a gidan, Jay kuwa ko a jikinsa don ko kallonsa ma baya yi, su biyu ne kadai a gidan don Abba ya fita tare da Aunty da autarta zuwa gidan wani prominent friend dinsa a garin, da yake gobe da safe za su bar kasar zuwa Nigeria, AJ ya gyara zama yana bin Jay da kallo trying to be sure of what he is holding in his hand, he was very shock ya dai bi sa da kallo har yaga ya nufi bangarensa, ya tallabi chin dinsa yana girgiza kafa, sai bayan da Jay ya fito for the first time since yesterday AJ yace "Wallahi i will never forgive you for these Jawwad, i promise you am not forgiving you" Jay dai ya dake bai yi dariyar da ya basa ba, kuma yaki tankasa yayi wucewarsa ya bar sa zaune a gun, da daddare Khaleesat na duba laptop dinta Jay ya shigo dakin da sallama ta daga kai tana kallonsa ya zauna kan kujeran dakin yace "Hope you are better now?" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya sauwake, amma ki tabbatar kin sha maganin so that u get enough night rest" Tace "Zan sha" Yace "Alright Good night Housemate, bacci nake ji" Ta
an yi murmushi tana kallon agogo dake nuna karfe goma tace "Ai baka ma yi da wuri ba" Yayi murmushi kawai yace "Saura kar ki kwanta saman gadon yau" A hankali tace "Zan kwanta" Yace "Good" Daga haka ya fita daga dakin, shi kansa yasan tunda ta dawo gidan yake tauye ma kansa bacci, kuma ba wai baccin baya damunsa bane kawai daurewa yake yi, har ciwon kai yake yawan yi yanzu saboda baya bacci sosai, Khaleesat ta kashe laptop dinta ta ajiye sannan ta mike a hankali ta dauko maganin da ya kawo mata daxu ta sha sannan ta kwanta saman gadon, amma fa a dar dar take saman gadon, Jay na isa parlorn dake sama ganin AJ kwance kan kujera yana danna wayarsa yace "Do you care sharing my room with me today?" AJ yaki tankasa yana danna wayarsa, Jay ya daga kafada yayi wucewarsa dakinsa, after like an hour AJ ya mike zaune jin muryar Abbansa, Abba dake kallonsa yace "Is everything Alright Ahmad?
Chapter 49 · 0% Book details