Sashe 88
Canjin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
1⃣0⃣7⃣Watan Al'amin uku, yaro mai cike da kuzari da lfy. Sukazo katsina suka sallami dangi suka wuce Madina don yin digiri dinsa na biyu. Yaso Mahmud ya taho, amma shi yace sai nan gaba. Don haka komai na game da makarantarsa ya barma Mahmud. Watansu uku da zuwa, Azumi gazo, don haka suka dawo gida sukayi Azumi, sbd tafsir din da ismail keyi. Bayan sallah suka koma. Lokacin aikin Hajji sukayi shiri da dansu don yin aikin Hajji. Mimi ta zazzo umura, amma bata ta6a aikin Hajji ba. Koda yake umura dinma, lokacin zuwa kawai take, amma batasan me zatayi ba sai siyayya. Rayuwarsu irin ta larabawa suke kwaikwayo gurin soyayya. Don haka ko yaushe suna nane da juna. A makka ne sun fito harami zasu je masaukinsu, Ismail dauke da Al'amin a kafada sanye cikin jallabiyya fara sol, Mimi cikin baqar doguwar riga ta rufe fuskarta da niqabi tana rataye da jakar tarkacen Al'amin, tana kuma maqale da hannun mijinta suna tafe kamar taurari. Sai kawai ta hango Na'ima. Tace, Malam ga Na'ima suka tsaya a gabanta. Zata kauce, Mimi ta daga niqabinta, tace Na'ima. Wata kunya ce ta rufeta, sai kuma ta rungume Mimi. Mimi tace keda wa kuka zo? Tace nida Momy. Masaukinmu zan koma wancan Hotel din. Mimi tace, muma nan muka sauka. Ta kalli Malam ta gaida shi, sannan suka wuce zuwa masaukin.
Momy Nafisa taji kunyar ganinsu, nan suka gaisa ta dauki Al'amin tana fadin yaro yayi girma. Na'ima bata tsaya 6ata lokaci ba ta shiga neman gafarar Mimi cikin kuka. Itama Momy sai tayi narai-narai tana roqon gafara. Mimi ta rungume Na'ima, tace babu komai, komai ya wuce, nima ku ya feni. Ismail yayi musu nasiha tare da nuna musu illar hakan. Sukayi godiya. Anan ne ma Na'ima tace, ai Malam ina ganinka a makarantarmu, 6oyewa nakeyi. Bayan ya dauki Al'amin ne yace bari suyi gaba kafin ta shigo. Na'ima tace, sis Mimi sai kin qara riqe wuta, sbd 'yan Makarantarmu suna bala'in son Mijinki, don dai dai ne yarinyar da bata labarinsa. Mimi tace, sunyi au gama. Momy tace ke Na'ima karki tada mata hankali, gashi kun saje da larabawa. Mimi tace hakane momy, gsky ta fada, kiran wayarshi da mata keyi ma kadai in nace zan damu, sai jini na ya hau. Sauqi na basa gabansa. Ta jima sannan ta koma dakinsu.
1⃣0⃣8⃣Duk lokacin da suka samu wani dan hutu ko na sati daya ne sai sunje Nigeria. Hakanan daddy yakan nuqo gari yazo ya gansu. Bayan sun shiga shekara ta biyu, lokacin Al'amin yana da wata takwas yana gudunsa ko ina, sunzo. Da zasu koma, Ismail yace, Dija ina ganin ya kamata mubar Al'amin gurin su Hajiya, don mu samo Rumaisarmu ko? Ta kalli dan nata dake varci tace Allah sarki Aminullah, har ya bani tausayi. Zanyi kewarsa. Yace ko yaya kk gani? Tace duk yadda kace babban Malami. Alhaji Bashir tamkar ya goya su Mimi don murna sun bar masa jikan daya shiga ransa. Saidai bai nuna ba don tsoron kar yayi masa irin na Uwarsa. Shekara kwana ce inda rayuwa, domin su Mimi sun dawo gida bayan Ismail ya samu shaidarsa mai kyau, ta samun digirinsa na biyu. Ya iso cike da burika, musamman gina jami'ar Musulunci a katsina. Sun gyara gidansu sosai. Da yake Mimi ma bata zauna ba, a Nadina taci gaba da neman ilimin addini, sai Makarantar nan tasu ta koma qarqashin kulawarta. Zumunci kuwa ita da Rabi'a, tamkar 'yan uwa. Ta sa Ismail ya gyarawa su yaya Amina gida. Ita kuma ta bata jari. Suna yin taimako sosai, duk na kusa da maqota sun shaida haka. Rashin samun cikinta yana damunta, da tace suje Asibiti yace a'a su sake jira, tunda wancan babu inda sukaje. Kwana biyu da yin haka ta soma mura. Yace shikenan gashinan Allah ya bamu. Tace ba ciki bane. Yace na Al'amin daga irin murannan ne. Haka kuwa da suka je asibiti sati shida. Wata Alhamis mimi ta gama hada masa kayan buda baki, sai ta nufi dakinta tace kaci zan dan watsa ruwa Malam, banason ina kusa da kai bana qamshi. Yace sai kin dawo dalibar Malam. Tana barin gurin message na shigowa, kamar yadda ya zata zainabu ce. Ya bude ya karanta. Tunda suka dawo, kullum sai samun saqonta tana fada masa halin da take ciki na sonshi. Kuma in zata mutu babu aure, to kuwa zata jirashi. Yayi shiru yana tunani. Shi gsky ynxu babu ko 6ur6ushin son Zainabu a ransa. Sai dai tausayinta. A fili yace bari dai mai ni din tazo muji ko zata lallasu.
[01/10 8:05 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa
1⃣0⃣9⃣Bai munafunceta ba ya nuna mata komai. Shiru tayi ta rasa me zata ce. Yace, me kk gani? Ta ban tausayi ne. Sai kurum Mimi ta miqe zata wuce, ya janyo ta jikinsa. "Wlh ba sonta nakeyi ba kinsan dai baki bina bashin rantsuwa. Tace shikenan duk wadda ta baka tausayi sai ka aureta har mu zama mu hudu? Yace shikenan batun ya wuce. Sun zanta da Mahmud akan batun zainabu, Mahmud yace, inda hali a duba yarinyarnan. Tazo gurina yafi sau talatin. Ismail yace to nidai kasan mijin tace ne, sbd banason damuwar matata, kamar yadda batason tawa. Mahmud yace nidai naga wata nan kusa dasu yaya Amina. Kuma dama inason fada maka ne, sai in yiwa su Malam magana suje su nemo min izini. Ai kaima Ismail kayi kuskure yaya zaka nemi shawarar mace, akan zakayi mata kishiya? Ai bari zakayi sai zance yayi nisa sannan ka fada mata. Shiyasa dana fada ma Rabi'a naga wadda nakeso, tayi fushinta ta gama. Ismail ya samu yaya Amina da batun, tace duk da batason ayiwa Mimi kishiya , tana tausayin zainabu. Wani dare ya yanke shawarar ziyartar Zainabu don bata shawarar ta nemi miji tayi aure. Sai dai ya kasa fada mata hakan lokacin da ta fito ta ganshi ta kuma saki kuka. Duk ta rame, tace Malam na sani ko yaushe Allah zai turomin kai. Domin a bakinka naji addu'ar daya kamata bawa yayi in yana neman buqata gurin Allah, litinin da Alhamis in nakai azumi, kafin nasha ruwa, ina fada ma Allah kaine nakeson Allah ya bani. Duk tsawon shekarunnan ban cirema raina ba. Ismail ya kasa magana, sai dai sun rabu da alqawarin zai dawo, don jikinsa ya mutu da kalaman zainabu. Shawarar mahmud itace abinyi. Ya koma gida ya kasa sukuni. Mimi kuma ta tsareshi don son jin dalili. Yace in kinji ma bashida amfani, don haushi zakiji. Ta nace, shi kuma ya fada mata komai. Ranar ce ta farko da suka raba daki tunda suka hada, saidai in daya baya gidan. Cijewa Ismail yayi baije lallashi ba don yasan ba zata saurareshi ba. Ita kam hakan ya sata zaton ko ismail ya daina yayinta. Kwana tayi kuka, sannan tunda duku-duku taja motarta ta nufi gidan Ubanta. Yaji fitarta daya duba sai yaga tabar Al'amin. Shine yayi masa shirin makaranta, ya kaishi. Daga can ya samu malam Aminu suka zanta akan batun zainabu, shima Malam ya amince da Ismail ya auri zainabu, sbd ubanta yazo gurinsa kusan sau biyar. Yace, suje aji sadaki, ya bada, a daura kawai ta tare. Daganan sai ya wuce gidansu gimbiyar sa.
1⃣1⃣0⃣Sun gaisa da Alhaji bayn sun shiga falon baqi. Alhaji yace, saiga mutuniyar fuska kumbure kuma har ynxun sai kuka taqi cewa komai. Ismail ya koro ma Alhaji komai. Alhaji yayi murmushi, "Ni dama nasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi. Mata sun tsani kishiya, kuma bayan da biyu ma akace mu fara, sannan uku ko hudu. Ita dama tana auren Malami zata ce ita daya zata zauna? Ismail yace nida banida ra'ayin sake aurema daddy, amma in yana cikin qaddara ta dole nayi. Yace karka damu, kaidai kayi qoqarin adalci, Mahaifiyarta tanada abin ce mata, kuma zata dawo anjima. Ko da Alhaji ya fadama Hajiya sauda maqasudin zuwan Mimi gida, a gaban Mimin Hajiya sauda tace haka ne? Mimi tace hakane. Ran Hajiya sauda ya 6aci, tace dama kina zaton mijinki ya zauna dake daya ne har abada? Ta dago ido ta kalli Hajiyar, "ya fa yi alqawarin ba zaimin kishiya ba, Hajiya sauda tace ga mahaifinki nan zaune, ni ma yayi min alqawarin ba zai min kishiya ba, amma yau kishiyoyi nawa gareni? Mimi tayi shiru. Hajiya ta sake cewa, inace harda ke kun hada baki aka auro miki Momynki Nafisa? Kin manta duk da wannan? To inaso ki sani, mata da yawa suna hana mazajensu aure, a qarshe sai mazajen suje suna bin matan banza. Sannan wasu suna hana mazan su aure a qarshe sai kuma su mutu ayi auren. Banda ma wannan qannai nawa gareki mata? Ce miki akayi ko wacce an bugo mata mijinta ne? In kin hana a auri qanwar wasu waccan ta hana a auri qanwarki, shikenan sai su tabbata babu aure? Inaso ki koma gidanki, ki nutsu ki ba mijinki qwarin gwiwa yayi muku adalci. Karki canza daga son da kk masa. Ki qara gurin kyautata masa. Ki riqe amanarsa, ki zama mai haquri da kuma ki hada da addu'a. In dai ni na haifeki, to karki kuma zuwa gidannan da sunan yaji. Ku kashe, ku rufe keda mijinki. Alhaji ya dubeta, "Mahaifiyarki ta gama fada miki komai. Ni dai zan qara miki da cewa kiyi haquri. Haka mimi ta koma gidanta cikin damuwa, sai dai zantukan mahaifiyarta sun isheta tunani. Ko da ya dawo lallashin ta yayi, tare da nuna mata cewa ba don bai sonta bane. Har zuwa ranar asabar din da aka daura auren, sama-sama suke, sai dai Mimi tace ya nemi gurin da zai saka matarsa, ba zata zauna tare da ita ba. Baiji komai ba, dama ya kama gida, unguwarsu Mahmud, can ya sata. Ranar farkonsu ya tausaya ma Zainabu sbd irin son da take masa. Ita kuwa Mimi kwana tayi kuka, ta san cewa ynxu sun zama su biyu masu shi. Daga masallanci, gidan ya wuto. Tana varci shima ya kwanta kusa da ita. Data farka ta ganshi, sai kawai ta fita ta koma kicin tana hada abin kari. Sai da ta gama soya dankali, da qwai da sauransu, sai taga ya dauki kwando ya jera, yace kiyi wani, wannan zan tafi dashi. Ta daga murya sbd me? Yace sbd Allah da kuma cewa kin isa. Ya debo dankali, muyi in tayaki. Banason ki zubar da kanki gurin zainabu, don a komai bata kaiki ba. Inason kiyi zama da ita na adalci, ki nuna mata girma. Kar kiyi wasa da muqaminki na Uwar gida.
[01/10 8:09 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa
Momy Nafisa taji kunyar ganinsu, nan suka gaisa ta dauki Al'amin tana fadin yaro yayi girma. Na'ima bata tsaya 6ata lokaci ba ta shiga neman gafarar Mimi cikin kuka. Itama Momy sai tayi narai-narai tana roqon gafara. Mimi ta rungume Na'ima, tace babu komai, komai ya wuce, nima ku ya feni. Ismail yayi musu nasiha tare da nuna musu illar hakan. Sukayi godiya. Anan ne ma Na'ima tace, ai Malam ina ganinka a makarantarmu, 6oyewa nakeyi. Bayan ya dauki Al'amin ne yace bari suyi gaba kafin ta shigo. Na'ima tace, sis Mimi sai kin qara riqe wuta, sbd 'yan Makarantarmu suna bala'in son Mijinki, don dai dai ne yarinyar da bata labarinsa. Mimi tace, sunyi au gama. Momy tace ke Na'ima karki tada mata hankali, gashi kun saje da larabawa. Mimi tace hakane momy, gsky ta fada, kiran wayarshi da mata keyi ma kadai in nace zan damu, sai jini na ya hau. Sauqi na basa gabansa. Ta jima sannan ta koma dakinsu.
1⃣0⃣8⃣Duk lokacin da suka samu wani dan hutu ko na sati daya ne sai sunje Nigeria. Hakanan daddy yakan nuqo gari yazo ya gansu. Bayan sun shiga shekara ta biyu, lokacin Al'amin yana da wata takwas yana gudunsa ko ina, sunzo. Da zasu koma, Ismail yace, Dija ina ganin ya kamata mubar Al'amin gurin su Hajiya, don mu samo Rumaisarmu ko? Ta kalli dan nata dake varci tace Allah sarki Aminullah, har ya bani tausayi. Zanyi kewarsa. Yace ko yaya kk gani? Tace duk yadda kace babban Malami. Alhaji Bashir tamkar ya goya su Mimi don murna sun bar masa jikan daya shiga ransa. Saidai bai nuna ba don tsoron kar yayi masa irin na Uwarsa. Shekara kwana ce inda rayuwa, domin su Mimi sun dawo gida bayan Ismail ya samu shaidarsa mai kyau, ta samun digirinsa na biyu. Ya iso cike da burika, musamman gina jami'ar Musulunci a katsina. Sun gyara gidansu sosai. Da yake Mimi ma bata zauna ba, a Nadina taci gaba da neman ilimin addini, sai Makarantar nan tasu ta koma qarqashin kulawarta. Zumunci kuwa ita da Rabi'a, tamkar 'yan uwa. Ta sa Ismail ya gyarawa su yaya Amina gida. Ita kuma ta bata jari. Suna yin taimako sosai, duk na kusa da maqota sun shaida haka. Rashin samun cikinta yana damunta, da tace suje Asibiti yace a'a su sake jira, tunda wancan babu inda sukaje. Kwana biyu da yin haka ta soma mura. Yace shikenan gashinan Allah ya bamu. Tace ba ciki bane. Yace na Al'amin daga irin murannan ne. Haka kuwa da suka je asibiti sati shida. Wata Alhamis mimi ta gama hada masa kayan buda baki, sai ta nufi dakinta tace kaci zan dan watsa ruwa Malam, banason ina kusa da kai bana qamshi. Yace sai kin dawo dalibar Malam. Tana barin gurin message na shigowa, kamar yadda ya zata zainabu ce. Ya bude ya karanta. Tunda suka dawo, kullum sai samun saqonta tana fada masa halin da take ciki na sonshi. Kuma in zata mutu babu aure, to kuwa zata jirashi. Yayi shiru yana tunani. Shi gsky ynxu babu ko 6ur6ushin son Zainabu a ransa. Sai dai tausayinta. A fili yace bari dai mai ni din tazo muji ko zata lallasu.
[01/10 8:05 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa
1⃣0⃣9⃣Bai munafunceta ba ya nuna mata komai. Shiru tayi ta rasa me zata ce. Yace, me kk gani? Ta ban tausayi ne. Sai kurum Mimi ta miqe zata wuce, ya janyo ta jikinsa. "Wlh ba sonta nakeyi ba kinsan dai baki bina bashin rantsuwa. Tace shikenan duk wadda ta baka tausayi sai ka aureta har mu zama mu hudu? Yace shikenan batun ya wuce. Sun zanta da Mahmud akan batun zainabu, Mahmud yace, inda hali a duba yarinyarnan. Tazo gurina yafi sau talatin. Ismail yace to nidai kasan mijin tace ne, sbd banason damuwar matata, kamar yadda batason tawa. Mahmud yace nidai naga wata nan kusa dasu yaya Amina. Kuma dama inason fada maka ne, sai in yiwa su Malam magana suje su nemo min izini. Ai kaima Ismail kayi kuskure yaya zaka nemi shawarar mace, akan zakayi mata kishiya? Ai bari zakayi sai zance yayi nisa sannan ka fada mata. Shiyasa dana fada ma Rabi'a naga wadda nakeso, tayi fushinta ta gama. Ismail ya samu yaya Amina da batun, tace duk da batason ayiwa Mimi kishiya , tana tausayin zainabu. Wani dare ya yanke shawarar ziyartar Zainabu don bata shawarar ta nemi miji tayi aure. Sai dai ya kasa fada mata hakan lokacin da ta fito ta ganshi ta kuma saki kuka. Duk ta rame, tace Malam na sani ko yaushe Allah zai turomin kai. Domin a bakinka naji addu'ar daya kamata bawa yayi in yana neman buqata gurin Allah, litinin da Alhamis in nakai azumi, kafin nasha ruwa, ina fada ma Allah kaine nakeson Allah ya bani. Duk tsawon shekarunnan ban cirema raina ba. Ismail ya kasa magana, sai dai sun rabu da alqawarin zai dawo, don jikinsa ya mutu da kalaman zainabu. Shawarar mahmud itace abinyi. Ya koma gida ya kasa sukuni. Mimi kuma ta tsareshi don son jin dalili. Yace in kinji ma bashida amfani, don haushi zakiji. Ta nace, shi kuma ya fada mata komai. Ranar ce ta farko da suka raba daki tunda suka hada, saidai in daya baya gidan. Cijewa Ismail yayi baije lallashi ba don yasan ba zata saurareshi ba. Ita kam hakan ya sata zaton ko ismail ya daina yayinta. Kwana tayi kuka, sannan tunda duku-duku taja motarta ta nufi gidan Ubanta. Yaji fitarta daya duba sai yaga tabar Al'amin. Shine yayi masa shirin makaranta, ya kaishi. Daga can ya samu malam Aminu suka zanta akan batun zainabu, shima Malam ya amince da Ismail ya auri zainabu, sbd ubanta yazo gurinsa kusan sau biyar. Yace, suje aji sadaki, ya bada, a daura kawai ta tare. Daganan sai ya wuce gidansu gimbiyar sa.
1⃣1⃣0⃣Sun gaisa da Alhaji bayn sun shiga falon baqi. Alhaji yace, saiga mutuniyar fuska kumbure kuma har ynxun sai kuka taqi cewa komai. Ismail ya koro ma Alhaji komai. Alhaji yayi murmushi, "Ni dama nasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi. Mata sun tsani kishiya, kuma bayan da biyu ma akace mu fara, sannan uku ko hudu. Ita dama tana auren Malami zata ce ita daya zata zauna? Ismail yace nida banida ra'ayin sake aurema daddy, amma in yana cikin qaddara ta dole nayi. Yace karka damu, kaidai kayi qoqarin adalci, Mahaifiyarta tanada abin ce mata, kuma zata dawo anjima. Ko da Alhaji ya fadama Hajiya sauda maqasudin zuwan Mimi gida, a gaban Mimin Hajiya sauda tace haka ne? Mimi tace hakane. Ran Hajiya sauda ya 6aci, tace dama kina zaton mijinki ya zauna dake daya ne har abada? Ta dago ido ta kalli Hajiyar, "ya fa yi alqawarin ba zaimin kishiya ba, Hajiya sauda tace ga mahaifinki nan zaune, ni ma yayi min alqawarin ba zai min kishiya ba, amma yau kishiyoyi nawa gareni? Mimi tayi shiru. Hajiya ta sake cewa, inace harda ke kun hada baki aka auro miki Momynki Nafisa? Kin manta duk da wannan? To inaso ki sani, mata da yawa suna hana mazajensu aure, a qarshe sai mazajen suje suna bin matan banza. Sannan wasu suna hana mazan su aure a qarshe sai kuma su mutu ayi auren. Banda ma wannan qannai nawa gareki mata? Ce miki akayi ko wacce an bugo mata mijinta ne? In kin hana a auri qanwar wasu waccan ta hana a auri qanwarki, shikenan sai su tabbata babu aure? Inaso ki koma gidanki, ki nutsu ki ba mijinki qwarin gwiwa yayi muku adalci. Karki canza daga son da kk masa. Ki qara gurin kyautata masa. Ki riqe amanarsa, ki zama mai haquri da kuma ki hada da addu'a. In dai ni na haifeki, to karki kuma zuwa gidannan da sunan yaji. Ku kashe, ku rufe keda mijinki. Alhaji ya dubeta, "Mahaifiyarki ta gama fada miki komai. Ni dai zan qara miki da cewa kiyi haquri. Haka mimi ta koma gidanta cikin damuwa, sai dai zantukan mahaifiyarta sun isheta tunani. Ko da ya dawo lallashin ta yayi, tare da nuna mata cewa ba don bai sonta bane. Har zuwa ranar asabar din da aka daura auren, sama-sama suke, sai dai Mimi tace ya nemi gurin da zai saka matarsa, ba zata zauna tare da ita ba. Baiji komai ba, dama ya kama gida, unguwarsu Mahmud, can ya sata. Ranar farkonsu ya tausaya ma Zainabu sbd irin son da take masa. Ita kuwa Mimi kwana tayi kuka, ta san cewa ynxu sun zama su biyu masu shi. Daga masallanci, gidan ya wuto. Tana varci shima ya kwanta kusa da ita. Data farka ta ganshi, sai kawai ta fita ta koma kicin tana hada abin kari. Sai da ta gama soya dankali, da qwai da sauransu, sai taga ya dauki kwando ya jera, yace kiyi wani, wannan zan tafi dashi. Ta daga murya sbd me? Yace sbd Allah da kuma cewa kin isa. Ya debo dankali, muyi in tayaki. Banason ki zubar da kanki gurin zainabu, don a komai bata kaiki ba. Inason kiyi zama da ita na adalci, ki nuna mata girma. Kar kiyi wasa da muqaminki na Uwar gida.
[01/10 8:09 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa