Sashe 39
Canjin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
insha Allahu, kinji ko? Tace ya daina so na, tunda ya
iya hadani aure da talaka, nasan ya daina so na,
kuma da gske yake yi, abinda yz fadamin, ya cire ni
daga cikin ‘ya’yan sa. Likita ka taimake ni, kayi min
allurar guba in mutu, likita yaja kujera ya zauna, bai
kamata ki nemi mutuwa ba bayan Allah ya raya ki,
kun yi mugun hadari fa, da Allah ya ga dama, sai ya
dauki ranki a lokacin.
Ki natsu koda daddyn ki ya qi ki, ba ga mijinki ba?
Tace bana sonshi! Malami ne fa? Ismail ya lumshe
ido cikin takaici, kar ki damu, ki bari ki qara samun
sauqi, muga yadda za’ayi, kinji? Ta dago ido ta
dubeshi, zaka barni mu tafi tare da khalil? Ynxun
bani da kowa sai shi, yace zaku tafi, da qyar suka
lallashe ta tayi shiru
Kwadayi madudin wahala na’im da mom Nafisa
bakuga komaibama ai, Ismail yace, ga ruwan da ta
cire nan a maida mata. Likitan yace, babu damuwa,
tunda ta dawo hayyacinta, zata iya cin komai ba sai
an maida ba. Sannan jininka za’a iya ba kowa, don
haka za’a zo a diba ynxu. Ismail yace, zanje can ne?
A’a ba sai kaje can ba, inji likitan. Anan ma za’a zo a
diba.
Da qyar Mahmud ya matsa ma Ismael yasha ruwan
tea. Shi kansa duk ya rame sbd tashin hankali. Tara
da kusan rabi, Sai ga wata nurse ta shigo da wasu
mata guda biyu, lokacin yaya Amina tana cewa bari
ta tafi, shi kuma Ismail yana cewa Mahmud, ya
kamata kaima ka tafi. Shi kuma yana cewa, bari dai
in an dibi jininka din sai na wuce. Sallamar wasu
matan ne, yasa su yin shiru daga zancen da suke yi
don jin ko su waye.
Dai dai lokacin mimi ta dangana daga kukan da
takeyi har ma ta yanke hukuncin yadda zatayi. Nata
ganin, abin da zai fissheta, in sun samu sauqi ita da
khalil, zata bishi gidansut tunda shi hajiyarsa tana
sonsu tare, sai ta zauna a gidansu, in ya kammala
karatu sai ayi musu aure, Amma ta daukar ma kanta
alqawarin yadda daddy yace ya barta, ita ma har
abada ba zata sake nemansu ba.
Dama hajiya bata sonta, shikenan zata yi Rayuwar ta
da khalil, ta amince bata da kowa sai shi din.
Sallamar matan ne ta katse mata tunani. Ta daga ido
ta kalle su. Ko cikin mata dubu ba zata kasa sheda
fuskar mahaifiyar khalil ba. Ba wai don kamar da
sukayi dashi ba, domin tun kafin suje gidansu a
kwanan baya ita da khalil din, ta mallaki hotunan
mahaifiyar tasa masu dinbin yawan gske a wayar ta
wadanda khalil din ke turo mata. A ranta tace
shikenan ma tazo tafiya damu. Nasan khalil ya riga
ya fada mata komai. Sai taji wani farin ciki ya darsu
acikin zuciyar ta.
Kukan da mahaifiyar khalil din ta fashe dashi ne ya
katse tunaninta, tare da tattaro dukkan hankalinta
zuwa gurin ta. Ji tayi tana fadin. Alahu Akhbar!
Yarinyar nan babu rabon kuyi aure da khalil, ajalinsa
ya jawo miki wahala. Ni dama nayi tunanin wannan
zazzafar s soyayyar da khalil ya kamu da ita, da qyar
in zai rayu, yaron nan bai ta6a min sata ba tunda ya
taso, sai dalilin wannan soyayya. In da mahaifinsa ya
bada hadin kai, kila da ynxun khalil yana raye. Allah
ya baki lfy. Mimi ta zaro idanu tana kallonsu.
Qwaqwalwarta ta kasa saita zantukansu. Wai suna
nufin khalil ya mutu ne?
Ismail kuwa ya rikice, yana ta yi wa nurse din alama
da yatsansa a baki wai suyi shiru, amma sam basu
lura ba. Saima fadi da nurse din take yi, wai iyayen
wanda ya mutu dinne suka zo daukar gawarsa, shine
suka ce a rakosu su duba ta. Daya matar kuwa
wadda suka zo tare, fadi takeyi, kiyi haquri aunty
Amina, Addu’a kawai zaki yi masa, kinyi dauriya a
gida, baki masa kuka ba, sai anan? Cikin kuka mai
tsanani mahaifiyar take cewa, ban gaskata
mutuwarsa ba saida nazo naga gawar khalil. Ihun da
mimi keyi ne ya katse mahaifiyar khalil.
Wani yunquri da mimin tayi shine ya saka su nufar
gadonta. Sai dai Ismail ya rigasu isa. Duk da haka
kafin yakai ta riga ta kai qasa a sume. Ya dauke ta
yana fadin, inata alamta muku cewa kuyi shiru. Sbd
batasan komai game da mutuwarsa ba, amma sam
baku kula ba, gashi kunsa itama za’a rasa ta. Ya dora
ta akan gadon yana cewa, ku taimaka ku kiramin
likita! Mahaifiyar khalil fadi take, Inna lillahi wa inna
ilaihi raji’un! Ai ban san bata sani ba, nurse kuwa tuni
tayi qasa da gudu don kiran likita.
Qarfe sha daya da mintina momy Nafisa ta shiga
gidan ‘yarta Na’ima. Aljannar duniya. Ha ta furta
lokacin data iso cikin falon farko, Ta kalli ‘yar tata,
wadda tazo ta bude mata qofa. Na’ima kina cikin irin
wannan gdn kk daga hankalinki? Na’ima ta turo baki,
momy ni wannan gdn yayi mintg girma, abin haushi
kuma ni hadai ke yini a cikin sa. Momy tace, a’a ina
masu aikin da akace an kawo miki? Tace, suna
gefensu. To ai su ba abokan hirana bane momy. Suje
su raina ni? Momy tace, ba nufi na kenan ba, ba wai
kuyi hira ba, ina nufin a qalla kina jin motsin wasu a
cikin gdn. Na’ima ta turo baki, to momy shifa bashi
da lokaci na.
Momy tace, matsalarki dai mijinki ko? Na’ima tace
eh. Momy nafisa tace, kije kice masa inason ganinsa,
ko har ya fita? Na’ima tace, yananan banji fitar sa ba.
Ta miqe ta nufi sama cikin zumudi. Tana bude qofar
ta jiyo shi yana waya, yana zaune a kujerar
computer. Daidai abinda kunnenta ya jiyo yana
cewa, “tsaya mana kiji Jennifer. Kar kisa ma kanki
damuwa, na fada miki ba wadda nakeso din na aura
ba, ko da ita dince ma kinsan cewa ke ta musamman
ce, kina tsammanin rayuwa ta zata tafi sak ne in
babu ke? Cikin turanci yake magana. Yayi jim,
alamun yana sauraron abinda take fada. Sannan yayi
‘yar dariya, tare da cewa, na san dai zaki iya bada
sheda ta kan fadar gsky komai dacinta. Ya sake yin
jim, sannan yace, to zan tabbatar miki da cewa kinfi
wadda aka kawomin a matsayin mata. Zan tabbatar
miki yadda ke da kanki zaki gamsu da batun, ya sake
saurawa. Sannan yace, fadamin me zan miki ki yarda
tunda naga kina tantama, kamar kin manta ni waye.
Dariya taji ya saki, tare da fadin, ai wannan mai sauqi
ne, in dai kwana da nine, ina me yi miki albishir
cewa, ni da ke yau a gida na zamu kwana. In nayi
miki haka, zaki gamsu cewa ni dake mutu-ka-raba?
Maganar ta maqale, bai qarasa ba, sakamakon jin
muryar Na’ima da yayi cikin kuka tana cewa, dama
mata kk nema? Ya saki murmushi, sannan ya maida
wayarsa kunnensa. Baby zan kira ki zuwa Anjima. Ya
kashe wayarsa, sannan ya juyo da kujerarsa gaba
daya, don irin mai jujjuyawarnan ce, cikin fara’a
yace, baki sani ba dama? Ta tsaya tana Numfashi,
tare da mamaki, gami da zaro idanu. Yayi murmushi
mai sauti, kina nufin dama bakuyi bincike ba? Ya
girgiza kai ayya.
Ni qasurgumin manemin mata ne. Sannan ina shan
wiwi da giya kadan, akwai wata matsala ne? Ta rasa
me zata ce, sai kuka. Cikin kuka take cewa, ba zan iya
zama dakai ba. Mutumin da baya iya 6oye laifinsa.
Yace, oho, dama kinzo kin la6e min ne? Kada ki
zauna dani din mana, dama ni na kawoki? Ko na riqe
ki ne? To kazo momy na tana jiran ka a falo, ya ta6e
baki, wacece kuma momy? Tace, don wulaqanci,
mahaifiyata dince baka sani ba? Ya kalli danqareren
agogon bangon falon, me kuma tazo yi da wannan
safiyar?
Ya kalli computer dake gabansa. Ta jirani, aiki nakeyi,
in zata iya, in kuma ba tada lokaci, taje ta dawo wani
lokacin, in abinda tazo dashi ya dame ta. Na’ima
tace, wadda ta haifeni ce fa? Yayi mata wani kallon
banza, cike da izgili yace, don ta haifeki, ni ta haifa?
Kuka ta fasa, sannan ta juya ta tafi ranta a 6ace,
hankalinta kuma a tashe. Cikin kuka ta sami momy
nafisa
zaune a falo, tana zaune tana jiranta. Momy kinji
abinda na sameshi yanayi? “me? ” inji momy. Na’ima
ta fada jikinta, tana kuka, na sameshi yana waya. Don
nayi masa magana, kai tsaye yace min waishi yana
neman mata. Kuma wai yana shan giya da wiwi.
Momy nafisa ta zaro idanu, cikin faduwar gaba tace,
iya hadani aure da talaka, nasan ya daina so na,
kuma da gske yake yi, abinda yz fadamin, ya cire ni
daga cikin ‘ya’yan sa. Likita ka taimake ni, kayi min
allurar guba in mutu, likita yaja kujera ya zauna, bai
kamata ki nemi mutuwa ba bayan Allah ya raya ki,
kun yi mugun hadari fa, da Allah ya ga dama, sai ya
dauki ranki a lokacin.
Ki natsu koda daddyn ki ya qi ki, ba ga mijinki ba?
Tace bana sonshi! Malami ne fa? Ismail ya lumshe
ido cikin takaici, kar ki damu, ki bari ki qara samun
sauqi, muga yadda za’ayi, kinji? Ta dago ido ta
dubeshi, zaka barni mu tafi tare da khalil? Ynxun
bani da kowa sai shi, yace zaku tafi, da qyar suka
lallashe ta tayi shiru
Kwadayi madudin wahala na’im da mom Nafisa
bakuga komaibama ai, Ismail yace, ga ruwan da ta
cire nan a maida mata. Likitan yace, babu damuwa,
tunda ta dawo hayyacinta, zata iya cin komai ba sai
an maida ba. Sannan jininka za’a iya ba kowa, don
haka za’a zo a diba ynxu. Ismail yace, zanje can ne?
A’a ba sai kaje can ba, inji likitan. Anan ma za’a zo a
diba.
Da qyar Mahmud ya matsa ma Ismael yasha ruwan
tea. Shi kansa duk ya rame sbd tashin hankali. Tara
da kusan rabi, Sai ga wata nurse ta shigo da wasu
mata guda biyu, lokacin yaya Amina tana cewa bari
ta tafi, shi kuma Ismail yana cewa Mahmud, ya
kamata kaima ka tafi. Shi kuma yana cewa, bari dai
in an dibi jininka din sai na wuce. Sallamar wasu
matan ne, yasa su yin shiru daga zancen da suke yi
don jin ko su waye.
Dai dai lokacin mimi ta dangana daga kukan da
takeyi har ma ta yanke hukuncin yadda zatayi. Nata
ganin, abin da zai fissheta, in sun samu sauqi ita da
khalil, zata bishi gidansut tunda shi hajiyarsa tana
sonsu tare, sai ta zauna a gidansu, in ya kammala
karatu sai ayi musu aure, Amma ta daukar ma kanta
alqawarin yadda daddy yace ya barta, ita ma har
abada ba zata sake nemansu ba.
Dama hajiya bata sonta, shikenan zata yi Rayuwar ta
da khalil, ta amince bata da kowa sai shi din.
Sallamar matan ne ta katse mata tunani. Ta daga ido
ta kalle su. Ko cikin mata dubu ba zata kasa sheda
fuskar mahaifiyar khalil ba. Ba wai don kamar da
sukayi dashi ba, domin tun kafin suje gidansu a
kwanan baya ita da khalil din, ta mallaki hotunan
mahaifiyar tasa masu dinbin yawan gske a wayar ta
wadanda khalil din ke turo mata. A ranta tace
shikenan ma tazo tafiya damu. Nasan khalil ya riga
ya fada mata komai. Sai taji wani farin ciki ya darsu
acikin zuciyar ta.
Kukan da mahaifiyar khalil din ta fashe dashi ne ya
katse tunaninta, tare da tattaro dukkan hankalinta
zuwa gurin ta. Ji tayi tana fadin. Alahu Akhbar!
Yarinyar nan babu rabon kuyi aure da khalil, ajalinsa
ya jawo miki wahala. Ni dama nayi tunanin wannan
zazzafar s soyayyar da khalil ya kamu da ita, da qyar
in zai rayu, yaron nan bai ta6a min sata ba tunda ya
taso, sai dalilin wannan soyayya. In da mahaifinsa ya
bada hadin kai, kila da ynxun khalil yana raye. Allah
ya baki lfy. Mimi ta zaro idanu tana kallonsu.
Qwaqwalwarta ta kasa saita zantukansu. Wai suna
nufin khalil ya mutu ne?
Ismail kuwa ya rikice, yana ta yi wa nurse din alama
da yatsansa a baki wai suyi shiru, amma sam basu
lura ba. Saima fadi da nurse din take yi, wai iyayen
wanda ya mutu dinne suka zo daukar gawarsa, shine
suka ce a rakosu su duba ta. Daya matar kuwa
wadda suka zo tare, fadi takeyi, kiyi haquri aunty
Amina, Addu’a kawai zaki yi masa, kinyi dauriya a
gida, baki masa kuka ba, sai anan? Cikin kuka mai
tsanani mahaifiyar take cewa, ban gaskata
mutuwarsa ba saida nazo naga gawar khalil. Ihun da
mimi keyi ne ya katse mahaifiyar khalil.
Wani yunquri da mimin tayi shine ya saka su nufar
gadonta. Sai dai Ismail ya rigasu isa. Duk da haka
kafin yakai ta riga ta kai qasa a sume. Ya dauke ta
yana fadin, inata alamta muku cewa kuyi shiru. Sbd
batasan komai game da mutuwarsa ba, amma sam
baku kula ba, gashi kunsa itama za’a rasa ta. Ya dora
ta akan gadon yana cewa, ku taimaka ku kiramin
likita! Mahaifiyar khalil fadi take, Inna lillahi wa inna
ilaihi raji’un! Ai ban san bata sani ba, nurse kuwa tuni
tayi qasa da gudu don kiran likita.
Qarfe sha daya da mintina momy Nafisa ta shiga
gidan ‘yarta Na’ima. Aljannar duniya. Ha ta furta
lokacin data iso cikin falon farko, Ta kalli ‘yar tata,
wadda tazo ta bude mata qofa. Na’ima kina cikin irin
wannan gdn kk daga hankalinki? Na’ima ta turo baki,
momy ni wannan gdn yayi mintg girma, abin haushi
kuma ni hadai ke yini a cikin sa. Momy tace, a’a ina
masu aikin da akace an kawo miki? Tace, suna
gefensu. To ai su ba abokan hirana bane momy. Suje
su raina ni? Momy tace, ba nufi na kenan ba, ba wai
kuyi hira ba, ina nufin a qalla kina jin motsin wasu a
cikin gdn. Na’ima ta turo baki, to momy shifa bashi
da lokaci na.
Momy tace, matsalarki dai mijinki ko? Na’ima tace
eh. Momy nafisa tace, kije kice masa inason ganinsa,
ko har ya fita? Na’ima tace, yananan banji fitar sa ba.
Ta miqe ta nufi sama cikin zumudi. Tana bude qofar
ta jiyo shi yana waya, yana zaune a kujerar
computer. Daidai abinda kunnenta ya jiyo yana
cewa, “tsaya mana kiji Jennifer. Kar kisa ma kanki
damuwa, na fada miki ba wadda nakeso din na aura
ba, ko da ita dince ma kinsan cewa ke ta musamman
ce, kina tsammanin rayuwa ta zata tafi sak ne in
babu ke? Cikin turanci yake magana. Yayi jim,
alamun yana sauraron abinda take fada. Sannan yayi
‘yar dariya, tare da cewa, na san dai zaki iya bada
sheda ta kan fadar gsky komai dacinta. Ya sake yin
jim, sannan yace, to zan tabbatar miki da cewa kinfi
wadda aka kawomin a matsayin mata. Zan tabbatar
miki yadda ke da kanki zaki gamsu da batun, ya sake
saurawa. Sannan yace, fadamin me zan miki ki yarda
tunda naga kina tantama, kamar kin manta ni waye.
Dariya taji ya saki, tare da fadin, ai wannan mai sauqi
ne, in dai kwana da nine, ina me yi miki albishir
cewa, ni da ke yau a gida na zamu kwana. In nayi
miki haka, zaki gamsu cewa ni dake mutu-ka-raba?
Maganar ta maqale, bai qarasa ba, sakamakon jin
muryar Na’ima da yayi cikin kuka tana cewa, dama
mata kk nema? Ya saki murmushi, sannan ya maida
wayarsa kunnensa. Baby zan kira ki zuwa Anjima. Ya
kashe wayarsa, sannan ya juyo da kujerarsa gaba
daya, don irin mai jujjuyawarnan ce, cikin fara’a
yace, baki sani ba dama? Ta tsaya tana Numfashi,
tare da mamaki, gami da zaro idanu. Yayi murmushi
mai sauti, kina nufin dama bakuyi bincike ba? Ya
girgiza kai ayya.
Ni qasurgumin manemin mata ne. Sannan ina shan
wiwi da giya kadan, akwai wata matsala ne? Ta rasa
me zata ce, sai kuka. Cikin kuka take cewa, ba zan iya
zama dakai ba. Mutumin da baya iya 6oye laifinsa.
Yace, oho, dama kinzo kin la6e min ne? Kada ki
zauna dani din mana, dama ni na kawoki? Ko na riqe
ki ne? To kazo momy na tana jiran ka a falo, ya ta6e
baki, wacece kuma momy? Tace, don wulaqanci,
mahaifiyata dince baka sani ba? Ya kalli danqareren
agogon bangon falon, me kuma tazo yi da wannan
safiyar?
Ya kalli computer dake gabansa. Ta jirani, aiki nakeyi,
in zata iya, in kuma ba tada lokaci, taje ta dawo wani
lokacin, in abinda tazo dashi ya dame ta. Na’ima
tace, wadda ta haifeni ce fa? Yayi mata wani kallon
banza, cike da izgili yace, don ta haifeki, ni ta haifa?
Kuka ta fasa, sannan ta juya ta tafi ranta a 6ace,
hankalinta kuma a tashe. Cikin kuka ta sami momy
nafisa
zaune a falo, tana zaune tana jiranta. Momy kinji
abinda na sameshi yanayi? “me? ” inji momy. Na’ima
ta fada jikinta, tana kuka, na sameshi yana waya. Don
nayi masa magana, kai tsaye yace min waishi yana
neman mata. Kuma wai yana shan giya da wiwi.
Momy nafisa ta zaro idanu, cikin faduwar gaba tace,