Sashe 38
Canjin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
gara dai ayi mata anan asibitin, kasan dalili? Ismail
yace a’a, Mahmud yace, kasan masu kudinnan aje ayi
mata na gida, Allah ya kyauta ba’a fata, a samu
matsala suce an barta a gd babu kula. Ismail yace
hakane, duk nayi wannan tunanin.
Sannan ga matsalar gurin zama. Ina zan kaita in an
dora ta? Ni mai daki daya a zaure, Mahmud yace,
hakane koma dai yaya ne, mu roqi Allah yasa ayi a
sa’a. Baki suka hada gurin cewa Ameen. Ismail ya
kalli flask din yace, harda ruwan zafi kazo min? yace
eh, inna ce tace in taho maka dashi, ynxun ma zanje
in siyo maka bread, sbd lokacin dana fito duk masu
shagunan basu fito ba. Ismail yace, ka bari sai kamar
qarfe takwas, don ynxun zaiyi wuya ka same su.
Mahmud yace, to shikenan dama kai nake tunani,
qila ma jiya ba kaci komai ba. Ismail yace saida yaya
Amina suka zo, sannan da suka zo da abinci nace nafi
son, ruwan zafi, shine mijinta ya kawo min bayan
sun koma. Mahmud zai sake magana kenan, sai yaga
kamar mimi tana motsi. Da sauri yace Ismail kamar
tana motsi.
Cikin azama suka isa gaban gadon, Ismail yace mimi
kin tashi? Ta lumshe idanunta, sannan ta sake
budesu ta kallesu. Alamu sun nuna yau jikin da
sauqi, Numfashinta ya daidaita. Hawaye suka soma
zuba daga idanunta, Mahmud yace sannu ya jiki?
Bata amsa ba, sai dai hawayen ne ka bin gefen
kumatunta. Ismail ya dora hannunsa akan nata, cikin
damuwa yace sannu kinji? Zaki sha ruwa? Taja wani
numfashi, cikin muryar marasa lfy tace, ni daddy na
zaka kai ni, ban son wannan asibitin.
Mahmud ya daga ma Ismail kai alamun yace mata
eh, zai kai ta, Ismail yace eh zan kai ki, amma sai kin
samu sauqi, sbd kinsan ba za’a iya tafiya dake a haka
ba ko? Ta lumshe ido, ina.. Ina hajiya ta? Da momy
na? Yace duk zasu zo. Sunce inyi miki sannu. Tace
malam kace suzo su tafi damu, ni da khalil, kirasu
ynxun malam. Yace zan kira su, zaki sha ruwa? Ta
sake juyar da kai, dai dai lokacin ne wayar Ismail ta
soma ringing.
Ya ciro ta daga aljihunsa, sannan ya kalli fuskar
wayar, hajiya sauda ce, don haka sai ya fita waje, ya
daga tare da sallama, suka gaisa. Tace masa, Ismail
yaya mai jikin? Yace da sauqi, tace ta farka ne? Yace
eh ta farka kuma Alhmdlh jikin da sauqi sosai. Tace
to mungode ma Allah, kar ka manta ka turomin
account number dinka. Yace insha Allahu. Tace
nagode sosai.
Bayan ya kashe wayar, zai juya kenan sai ya hango
likitan ya nufo dakinsu don haka sai ya jira shi, likitan
ya qaraso. Sun gaisa ta hanyar yin musabaha, sannan
ya tambayi yadda ta kwana da jikin?
Ismail yace jikin da sauqi yau, don ta daina wannan
nishin. Likitan yayo ciki, Ismail ya biyo shi yana masa
qorafin har ynxun bata ci wani abu ba. Daidai sunje
kanta ne, likitan yake bashi amsa da cewa, kar ka
damu da wannan, sbd ruwan da muka sa mata jiya
da daddare yana dauke da sinadaran abinci, so, ko
bata ci ba, ba zai zama matsala ba.
Ynxun muje a debi jininka a gwada mu gani, in yayi
sai muyi qoqarin saka mata a yau. In mun tabbatar
da samun sauqin ta, sai mu saka ranar da za’a yi
mata aiki, ina nufin dori. Ismail yace, na zaci yau
za’ayi mata sbd kar qafar tayi tsami. Likitan yayi
murmushi, kar ka damu zata samu sauqi, ba tare da
wata matsala ba. Haka kuma babu abinda zai faru ko
da takai sati daya ba’a dora ta ba. Ismail yace,
shikenan Allah ya bata lfy.
Ameen, inji likitan, tare da dafa kafadar Ismail ya
jinjina. Sannan ya kalli mimi, sannu khadija. Ta dago,
ta kalli likitan, ya kama hannunta mai lafiyar, inane
yake yi miki ciwo ynxun? Tace duk jikina, amma
qafafu na sunfi yimin ciwo da hannuna. Likitan yace,
bayan nan fa? Ta soma kuka, nidai gidanmu nake son
a kaini, can zanje gurin daddy na. Likitan yace, za’a
kai ki da zaran kin samu sauqi, kinji ko? Tace ina
khalil?
Likitan yace, yana nan yana samun sauqi kinji? Cikin
sigar lallashi yayi maganar. Kar ki damu kisha tea
kinji ko? Tace ni banajin yunwa. Ina son in wanke
baki na. Likitan yace, karki damu k8nji ko? Ya kalli
Ismail, ka bini muje ko? Ismail ya dubi Mahmud, ina
zuwa ynxun. Mahmud ya koma bakin daya gadon ya
zauna tare da cewa to.
Ismail yabi bayan likitan, suna fitowa, sai gasu yaya
Amina, yace su shiga bari ya dawo Yanxun. Likita ne
ya nuna masa har sashen masu dibar jinin, sannan
ya kalleshi, in sun gama, ka sameni a office dina, kar
ka damu ko kaga mutane ga shigo kawai, Ismail yace
to nagode. Bayan an diba ne, sai suka ce ya tafi zasu
kaima likitan sakamakon in sun fitar.
Yace to, nan ya nufi office din likitan, kamar yadda
likitan ya fada masa haka yayi, ya shiga duk da
wadanda ya samu suna ganin likitan. Ya samu yana
ganin wani a ciki, har zai fita, sai likitan yace, dan jira
mu kadan, ynxun zan sallameshi, yana fita, ya nuna
ma Ismail kujera, zauna nan. Ya dora hannuwansa
saman babban teburin dake gabansa, sannan ya kalli
Ismail wace, shawara kuka yanke? Game da daurin
dorin matarka.
Ko baku riga kun yanke shawara ba? Ismail yace
mun yanke, kawai ayi mata anan. Likitan yace,
shikenan za’a kawo maka takardar biyan kudi, sai
kaje ka biya, sannan su baka takardar shedar biyan
kudi, Ismail yace to, na gode. Likita yace, amma shi
wanda ya mutu yaya suke da ita? Ismail yace, shi
take so, likitan ya aje biron dake hannunsa, ya tattara
hankalinsa a gurin Ismail, kamar yaya shi take so,
gaka mijinta?
Ismail saida ya danyi shiru, don ya tsani bada
labarin, sannan yaba likitan labarin aurensu a
taqaice. Likitan ya danyi jim, sannan yace, kayi
haquri, ka kuma riqeta, wata rana zakaji dadin
haqurinka. Ya miqe tare da cewa na gode likita, kar
ka damu zan taimaka iyakar iyawa ta, inji likitan,
Ismail ya sake cewa nagode, yace ba komai kaje, in
sun kawo sakamakon kazo.
Lokacin daya dawo, ya samu mimi tana ta kuka, yaya
Amina tana ta bata haquri, ya isa gurinsu, yaje cikin
damuwa, daidai kunnenta ya rusuna yana cewa, yi
haquri mimi, ki fadamin me kk so? Tace ni gurin
daddy zanje, ka bani wayata in kira daddy na.
Yasa dan yatsansa yana share mata Hawaye, wayarki
ta 6ace a gurin da kukayi hadari, amma ki bari zan
siya miki wata. In kinji sauqi, zan kaiki gurin daddyn
ki. Sabon kuka ta saka, tana fizge-fizge, ya miqe ya
koma kusa da Mahmud yace, nifa gsky zan kira mata
shi suyi magana, Mahmud yace ka kira shi kawai don
kada ta zarge ka. A handsfree ya saka wayarsa,
sannan ya kira layin daddyn nata, tayi ta katsewa
ba’a daga ba. Ya sake kira, gab da zata katse aka daga,
tare da cewa hello! Ta gane muryar daddy, don haka
cikin kuka tace, daddy kazo ka tafi dani. Zan mutu
anan. Daddyn cikin zafin rai, a fusace yace kar ki sake
kiran layina.
Ni ba mahaifinki bane, baki daga cikin ‘ya’ya na, da
farko nayi niyyar in huce sbd kinyi min biyayya a
karo na biyu, kinbi wanda na baki, ashe ke kina kan
bakanki, to inaso ki sani, ko mahaifiyarki na samu
labarin inda kk, sai na kada ta ta barmin gidana, bare
wata nafisa da kk kira tazo, kisa a ranki bakida kowa
sai wannan mijin naki. In kinga dama ki zauna. In
kuma sake tafiyar za kiyi, duk ba damuwa ta bace.
Nidai gargadina kar ki sake kirana, ko ke ko mijinki!
Yakai qarshen zancen tare da kashe wayar sa. Ihu
mimi ta saka, tare da fizge ruwan da aka sa mata a
hannunta mai lafiyar. Saboda tsananin kukan da
takeyi, ya hana Ismail lallashinta, don bai san ta ina
zai fara ba. Tayi kuka har muryarta ta dushe, babban
takaicin ta, ba zata iya tashi ba, don da tuni ta fita titi,
mota ta taka ta ta huta.
Ganin abin bana qarewa bane, yasa Ismail kiran
likitan. Yayi fada sosai, ganin halin da mimin ke ciki,
yace bai dace mara lfy irin haka a sata cikin damuwa
ba. Ya kalleta, khadija kiyi haquri dadyn ki zai huce
yace a’a, Mahmud yace, kasan masu kudinnan aje ayi
mata na gida, Allah ya kyauta ba’a fata, a samu
matsala suce an barta a gd babu kula. Ismail yace
hakane, duk nayi wannan tunanin.
Sannan ga matsalar gurin zama. Ina zan kaita in an
dora ta? Ni mai daki daya a zaure, Mahmud yace,
hakane koma dai yaya ne, mu roqi Allah yasa ayi a
sa’a. Baki suka hada gurin cewa Ameen. Ismail ya
kalli flask din yace, harda ruwan zafi kazo min? yace
eh, inna ce tace in taho maka dashi, ynxun ma zanje
in siyo maka bread, sbd lokacin dana fito duk masu
shagunan basu fito ba. Ismail yace, ka bari sai kamar
qarfe takwas, don ynxun zaiyi wuya ka same su.
Mahmud yace, to shikenan dama kai nake tunani,
qila ma jiya ba kaci komai ba. Ismail yace saida yaya
Amina suka zo, sannan da suka zo da abinci nace nafi
son, ruwan zafi, shine mijinta ya kawo min bayan
sun koma. Mahmud zai sake magana kenan, sai yaga
kamar mimi tana motsi. Da sauri yace Ismail kamar
tana motsi.
Cikin azama suka isa gaban gadon, Ismail yace mimi
kin tashi? Ta lumshe idanunta, sannan ta sake
budesu ta kallesu. Alamu sun nuna yau jikin da
sauqi, Numfashinta ya daidaita. Hawaye suka soma
zuba daga idanunta, Mahmud yace sannu ya jiki?
Bata amsa ba, sai dai hawayen ne ka bin gefen
kumatunta. Ismail ya dora hannunsa akan nata, cikin
damuwa yace sannu kinji? Zaki sha ruwa? Taja wani
numfashi, cikin muryar marasa lfy tace, ni daddy na
zaka kai ni, ban son wannan asibitin.
Mahmud ya daga ma Ismail kai alamun yace mata
eh, zai kai ta, Ismail yace eh zan kai ki, amma sai kin
samu sauqi, sbd kinsan ba za’a iya tafiya dake a haka
ba ko? Ta lumshe ido, ina.. Ina hajiya ta? Da momy
na? Yace duk zasu zo. Sunce inyi miki sannu. Tace
malam kace suzo su tafi damu, ni da khalil, kirasu
ynxun malam. Yace zan kira su, zaki sha ruwa? Ta
sake juyar da kai, dai dai lokacin ne wayar Ismail ta
soma ringing.
Ya ciro ta daga aljihunsa, sannan ya kalli fuskar
wayar, hajiya sauda ce, don haka sai ya fita waje, ya
daga tare da sallama, suka gaisa. Tace masa, Ismail
yaya mai jikin? Yace da sauqi, tace ta farka ne? Yace
eh ta farka kuma Alhmdlh jikin da sauqi sosai. Tace
to mungode ma Allah, kar ka manta ka turomin
account number dinka. Yace insha Allahu. Tace
nagode sosai.
Bayan ya kashe wayar, zai juya kenan sai ya hango
likitan ya nufo dakinsu don haka sai ya jira shi, likitan
ya qaraso. Sun gaisa ta hanyar yin musabaha, sannan
ya tambayi yadda ta kwana da jikin?
Ismail yace jikin da sauqi yau, don ta daina wannan
nishin. Likitan yayo ciki, Ismail ya biyo shi yana masa
qorafin har ynxun bata ci wani abu ba. Daidai sunje
kanta ne, likitan yake bashi amsa da cewa, kar ka
damu da wannan, sbd ruwan da muka sa mata jiya
da daddare yana dauke da sinadaran abinci, so, ko
bata ci ba, ba zai zama matsala ba.
Ynxun muje a debi jininka a gwada mu gani, in yayi
sai muyi qoqarin saka mata a yau. In mun tabbatar
da samun sauqin ta, sai mu saka ranar da za’a yi
mata aiki, ina nufin dori. Ismail yace, na zaci yau
za’ayi mata sbd kar qafar tayi tsami. Likitan yayi
murmushi, kar ka damu zata samu sauqi, ba tare da
wata matsala ba. Haka kuma babu abinda zai faru ko
da takai sati daya ba’a dora ta ba. Ismail yace,
shikenan Allah ya bata lfy.
Ameen, inji likitan, tare da dafa kafadar Ismail ya
jinjina. Sannan ya kalli mimi, sannu khadija. Ta dago,
ta kalli likitan, ya kama hannunta mai lafiyar, inane
yake yi miki ciwo ynxun? Tace duk jikina, amma
qafafu na sunfi yimin ciwo da hannuna. Likitan yace,
bayan nan fa? Ta soma kuka, nidai gidanmu nake son
a kaini, can zanje gurin daddy na. Likitan yace, za’a
kai ki da zaran kin samu sauqi, kinji ko? Tace ina
khalil?
Likitan yace, yana nan yana samun sauqi kinji? Cikin
sigar lallashi yayi maganar. Kar ki damu kisha tea
kinji ko? Tace ni banajin yunwa. Ina son in wanke
baki na. Likitan yace, karki damu k8nji ko? Ya kalli
Ismail, ka bini muje ko? Ismail ya dubi Mahmud, ina
zuwa ynxun. Mahmud ya koma bakin daya gadon ya
zauna tare da cewa to.
Ismail yabi bayan likitan, suna fitowa, sai gasu yaya
Amina, yace su shiga bari ya dawo Yanxun. Likita ne
ya nuna masa har sashen masu dibar jinin, sannan
ya kalleshi, in sun gama, ka sameni a office dina, kar
ka damu ko kaga mutane ga shigo kawai, Ismail yace
to nagode. Bayan an diba ne, sai suka ce ya tafi zasu
kaima likitan sakamakon in sun fitar.
Yace to, nan ya nufi office din likitan, kamar yadda
likitan ya fada masa haka yayi, ya shiga duk da
wadanda ya samu suna ganin likitan. Ya samu yana
ganin wani a ciki, har zai fita, sai likitan yace, dan jira
mu kadan, ynxun zan sallameshi, yana fita, ya nuna
ma Ismail kujera, zauna nan. Ya dora hannuwansa
saman babban teburin dake gabansa, sannan ya kalli
Ismail wace, shawara kuka yanke? Game da daurin
dorin matarka.
Ko baku riga kun yanke shawara ba? Ismail yace
mun yanke, kawai ayi mata anan. Likitan yace,
shikenan za’a kawo maka takardar biyan kudi, sai
kaje ka biya, sannan su baka takardar shedar biyan
kudi, Ismail yace to, na gode. Likita yace, amma shi
wanda ya mutu yaya suke da ita? Ismail yace, shi
take so, likitan ya aje biron dake hannunsa, ya tattara
hankalinsa a gurin Ismail, kamar yaya shi take so,
gaka mijinta?
Ismail saida ya danyi shiru, don ya tsani bada
labarin, sannan yaba likitan labarin aurensu a
taqaice. Likitan ya danyi jim, sannan yace, kayi
haquri, ka kuma riqeta, wata rana zakaji dadin
haqurinka. Ya miqe tare da cewa na gode likita, kar
ka damu zan taimaka iyakar iyawa ta, inji likitan,
Ismail ya sake cewa nagode, yace ba komai kaje, in
sun kawo sakamakon kazo.
Lokacin daya dawo, ya samu mimi tana ta kuka, yaya
Amina tana ta bata haquri, ya isa gurinsu, yaje cikin
damuwa, daidai kunnenta ya rusuna yana cewa, yi
haquri mimi, ki fadamin me kk so? Tace ni gurin
daddy zanje, ka bani wayata in kira daddy na.
Yasa dan yatsansa yana share mata Hawaye, wayarki
ta 6ace a gurin da kukayi hadari, amma ki bari zan
siya miki wata. In kinji sauqi, zan kaiki gurin daddyn
ki. Sabon kuka ta saka, tana fizge-fizge, ya miqe ya
koma kusa da Mahmud yace, nifa gsky zan kira mata
shi suyi magana, Mahmud yace ka kira shi kawai don
kada ta zarge ka. A handsfree ya saka wayarsa,
sannan ya kira layin daddyn nata, tayi ta katsewa
ba’a daga ba. Ya sake kira, gab da zata katse aka daga,
tare da cewa hello! Ta gane muryar daddy, don haka
cikin kuka tace, daddy kazo ka tafi dani. Zan mutu
anan. Daddyn cikin zafin rai, a fusace yace kar ki sake
kiran layina.
Ni ba mahaifinki bane, baki daga cikin ‘ya’ya na, da
farko nayi niyyar in huce sbd kinyi min biyayya a
karo na biyu, kinbi wanda na baki, ashe ke kina kan
bakanki, to inaso ki sani, ko mahaifiyarki na samu
labarin inda kk, sai na kada ta ta barmin gidana, bare
wata nafisa da kk kira tazo, kisa a ranki bakida kowa
sai wannan mijin naki. In kinga dama ki zauna. In
kuma sake tafiyar za kiyi, duk ba damuwa ta bace.
Nidai gargadina kar ki sake kirana, ko ke ko mijinki!
Yakai qarshen zancen tare da kashe wayar sa. Ihu
mimi ta saka, tare da fizge ruwan da aka sa mata a
hannunta mai lafiyar. Saboda tsananin kukan da
takeyi, ya hana Ismail lallashinta, don bai san ta ina
zai fara ba. Tayi kuka har muryarta ta dushe, babban
takaicin ta, ba zata iya tashi ba, don da tuni ta fita titi,
mota ta taka ta ta huta.
Ganin abin bana qarewa bane, yasa Ismail kiran
likitan. Yayi fada sosai, ganin halin da mimin ke ciki,
yace bai dace mara lfy irin haka a sata cikin damuwa
ba. Ya kalleta, khadija kiyi haquri dadyn ki zai huce