Sashe 47
Canjin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
gidanki.
Har Na’ima ta kawo musu abin sha da cincin, su
diblan, da alkaki, irin wanda amare ke ba ma
baqinsu, amma basu daina maganar ba. Kai kurum
Na’ima ta sunkuyar, suka yi mata tatass. Har kuka
saida tayi tana bashi haquri, amma basu daina ba.
Sunyi kusan minti talatin, sannan suka ce zasu tafi.
Har gurin mota ta rakasu, sannan ta dawo cikin
damuwa da takaici mara misaltuwa. Alamu sun nuna
sam ba zata ji dadin dangin mijinnan nata ba. Tun
kafin motarsu tabar harabar gdn, hajiya ladi tace,
hajiya Bilkisu gsky bakiyi sa’ar sarakuwa ba, alamu
sun nuna zatayi rowa. Kin tuna lokacin da muka raka
hajiya mairo gdn danta mansur?
Wace irin kyauta tayi mata harda mu? Hajiya Bilkisu
tayi tsaki. Abinda ke raina kenan ladi. Mu kanmu
surukar hajiya mairo ta bamu turaruka masu tsada,
ita kuwa lesuka ta bata da atamfa. Hajiya zuwaira
tace, ko qannensa da sukaje yini, sai da ta hado su da
kayan shafa. Gsky hajiya Bilkisu ki taka birki tunda
wuri. Domin in kk bari wannan rowar da rashin son
jama’ar nata yayi nisa, to kuwa nan gaba shi kansa
dan naki, kina ji kina gani, zai tsani danginsa, ya
kuma qanqame abin hannunsa.
Ran hajiya Bilkisu ya qara sosuwa, ta ce, ina zai yiwu!
Gobe zan turo su Aisha da samira, har Azima da
jamil, in gani suma rowar zatayi musu. Hajiya ladi ta
saka dariya, kinji hajiya Bilkisu, kema tayi miki rowa
ballantana wasu yaranki? Kawai danki zaki tasa a
gaba ki nuna masa cewa, yayi mata tarbiyyar kyuta
da son jama’a tunda an kasa yi mata gidansu. Hajiya
zuwaira tace, zancen kenan. Tafdijam! Wannan shine
gaba kura baya damisa. Na’imar da bata samu
kwanciyr hankali daga Abbas ba, ta yaya zata san
yadda zatayi abida ya kamata? Muje dai zuwa.
Haka kuwa washe gari sai Na’ima ta sake jin bugun
qofa, guraren qarfe dayan rana. Bata yi qasa a gwiwa
ba, ta tashi ta nufi budewa don kar ayi irin na jiya. Su
Aisha ne da samira da kuma Azima harda auta jamil.
Cikin ‘yar fara’a mai kama da yaqe tayi musu sannu
da zuwa. Suma suka amsa cikin isa, musamman
samira da Azima. Sun zauna, ita kuma ta nufi kicin
don kawo musu abin sha da dan na ta6awa sannan
ta sanar da masu aiki cewa, ga baqi a dora musu
abinci. Taje ta kawo musu hotunan biki.
Sannan ta zauna. Jin basu gaisheta ba tace musu, ina
yininku? Suka ce lfy. Aisha tace, ina bros Abbas fa?
Na’ima tace, ya fita tun safe, don tana daki taji
fitarsa. Samira tace, sis Aisha kin manta jiya bros
daya zo yace, zai koma aiki? Aisha tace, haka ne,
Na’ima tace, eh ya koma aiki yau. Ta fadi hakane
kurum, sbd kar su fahimci irin zaman da sukeyi. Sun
wuni cur, amma bataji dadinsu ba. Komai cikin isa
da nuna mata iyakar ta sukeyi. Sannan Abbas ya
shigo kusan shida na yamma.
Tana dag cikin daki tana jiyosu yana ce musu, kunci
kunsha duk abinda kk so, ko kuma anyi muku
rowar? Samira, wadda tafi kowa rashin kunya, tace,
an ma isa? Bros muzo gidanka ayi mana rowa? Za ma
mu jira kenan. Kowa abida take so, shi tasa masu aiki
suka dafa mata. Yace, kunyi daidai. Bari inyi wanka
inzo in kaiku gida. Aisha ce ta shigo tana ce mata.
Bros fa ya dawo. Tace to, sannan ta taso daga kan
gadon, ta nufi samanshi, cikin fargaba, sbd kar
qannensa su fahimci wani abu.
Ta tura qofar falon ta bude. Na’ima ta shiga cikin
fargaba. Yana zaune kan kujera yana ciro wasu
takardu daga cikin jakarsa. Tace sannu da zuwa. Baiji
shigowar ta ba, sai magana kawai yaji. Ya dago a
fusace, “lafiya? ” A tsorace kuma cikin faduwar gaba
tace, dama Aisha ce tace min ka dawo, kuma su baqi
ne dai, kada su gane cewa akwai wata matsala
Tsakanin mu. Ya watso mata harara. Don Allah fitan
min anan! An dade ba’a gane cewa, Tsakanin mu
akwai matsala ba. Waton ma jiya da Momyn mu
suka zo shine kkyi musu wulaqanci ko?
Na’ima ta riqe kanta sbd wani sarawa da yakeyi.
Tace, ai dai na basu haquri ban zaci sune suka zo ba.
Na zaci wannan matar ce data biyo ka. Yace, in itace
sai kiqi bude qofa tunda gidan babanki ne? To bari in
sanar dake, in baki sani ba, ta fiki matsayi. Ke har iko
ta fiki a gidannan. Sbd haka kibi a sannu. Sannan duk
lokacin da ‘yan uwana suka zo wani yayi kuka dake,
na rantse miki sai na zane ki. Fita! Wawiya kawai!
Na’ima ta dubeshi rai 6ace, kai bakasan darajar dan
adam ba. Ka sake ni kawai, don ba zan iya da wannan
wulaqancin ba. Yace, fita nace kiyi. Da kuka ta fito,
sbd 6acin rai har ta manta da baqin da suke gidan.
Gadonta ta fada tana kuka. Samira, suka kalli juna da
Aisha, lokacin da ta wuce su a falo. Har suka shiga
dakin, sallar magriba tana kwance tana kuka. Aisha
ce ta tambaye ta ko lafiya? Sam Na’ima bata tanka ba
har zuwa lokacin da suka gama shirinsu suka ce,
mun wuce, Na’ima bata daina kuka ba bare ta amsa.
Sun isa gida cike da dokin labarin kaiwa mahaifiyar
su. Aisha tana jinsu tana kallon su, samira Tana sanar
da mahaifiyar su cewa, Bros Abbas yasa Na’imar
kuka. Qila ma dukanta yayi. Azima kuma tace,
sannan munyi abinda muka ga dama a gdn. Aisha
tace, ku dai bakuda hankali, ina ruwan ku da kukan
ta?shiyajiya Bilkisu tace, yayi min daidai! Ai shiyasa
jiya daya zo na fada masa abinda tayi, sbd ya kwa6a
mata. Samira tace, mu ma da zamu taho ba tace
mana komai ba. Aisha tace, ku dai kuna da matsala
wlh, ba kuga tana ta kuka bane? Tayi tsaki, ta miqe ta
nufi dakinta. Ita dai ko a cikin ranta, bata so Bros
Abbas yaci zarafin matarsa ba. Domin ta ba ta
tausayi lokacin da take ta kukan. Na’ima kuwa kiran
layin momy nafisa tayi, amma bata daga ba. Don
haka sai ta tura mata saqon waya kan cewa, ita fa ba
zata iya wannan auren ba. Domin mimi ba qaramar
sa’a tayi ba, da bata kasance matar Abbas ba. Don
Allah ki ceci rayuwa ta. Sam ynxun na haqura da son
Abbas. Saqon yaje sama da minti goma sannan kiran
momy nafisa ya shigo. Na’ima ta tashi zaune, ta
tallafe kanta mai matuqar sarawa, sannan ta daga
wayar, momy tace, Na’ima yaya ne? Na’ima ta soma
kuka. Momy tace kashh! Ke kullum Sallamar ki kenan
kuka? Sake dukanki yayi? Na’ima ta sanar da momy
zuwan mahaifiyar sa da qannensa. Momy tace,
tirqashi! Abin harda danginsa? Na’ima tace, momy
kizo ki daukeni don Allah. Momy tace gobe zamuzo
da hajiya nana. Na’ima tace, don Allah mommy
kuzo. Tace karki damu zamuzo.
Kwanan Zainabu biyu a asibiti, amma babu labarin
alhaji. Innar ta kuwa taci bashi yafi na dubu goma.
Sawunta hudu a gidan Alhajin, amma bata samunsa.
Don haka sukayi shawara da aminiyarta yalwa cewa,
in an sallami Zainabu su wuce da ita gida kai tsaye, in
yazo ya biya kudin saita koma. Baban su Zainabu
kuwa yaje ya duba ta sau daya, bai kuma komawa
ba.
Zainabu kuwa kuka takeyi akan ba zata koma ba,
domin kwanakin nan da bata gidan, duk da cewa a
asibiti take yafi mata zaman gidansa. Hankalinta bai
sake tashi ba, saida ‘yan gidan su Ismail suka zo duba
ta, taji wannan fatu din tana cewa innar su wai sunzo
duba matar Ismail ne tayi hatsari. Innar su Zainabu
tace, ai yayi aure ne? Nan su fatu da sauran matan
gidan suka soma ba innar su Zainabu labari. Ai
maigidansa ne ya bashi ‘yarsa, ita kuma bataso, ta
gudu shine tayi hatsari. Daga nan Zainabu bata iya ci
gaba da saurarensu ba, ta shiga rera kuka. Daren
ranar bata runtsa ba, kenan Ismail yananan asibitin
yana jinyar matarsa.
Ita dai zata so ta sake ganinsa a rayuwar ta ko da
daga nesa ne. Ta san lallai ta rasa Ismail tunda har
yayi aure. Ta yi ta tuno kalaman da yake fada mata
na irin tsantsar son da yake mata. Washe gari da safe
innar ta taje famfo inda zata wanko ‘yan kayan
Zainabun, ita kuma zainabu ta sauko a hankali, ta
dauki zani guda daya daga cikin zannuwanta ta yafa
ta nufi fita. Matar kusa da gadonsu tace, ina zakije
Zainabu, ko bandaki zaki shiga? Tace a’a zan dann
tattaka ne, sbd jikina duk ciwo yake sbd zaman guri
Har Na’ima ta kawo musu abin sha da cincin, su
diblan, da alkaki, irin wanda amare ke ba ma
baqinsu, amma basu daina maganar ba. Kai kurum
Na’ima ta sunkuyar, suka yi mata tatass. Har kuka
saida tayi tana bashi haquri, amma basu daina ba.
Sunyi kusan minti talatin, sannan suka ce zasu tafi.
Har gurin mota ta rakasu, sannan ta dawo cikin
damuwa da takaici mara misaltuwa. Alamu sun nuna
sam ba zata ji dadin dangin mijinnan nata ba. Tun
kafin motarsu tabar harabar gdn, hajiya ladi tace,
hajiya Bilkisu gsky bakiyi sa’ar sarakuwa ba, alamu
sun nuna zatayi rowa. Kin tuna lokacin da muka raka
hajiya mairo gdn danta mansur?
Wace irin kyauta tayi mata harda mu? Hajiya Bilkisu
tayi tsaki. Abinda ke raina kenan ladi. Mu kanmu
surukar hajiya mairo ta bamu turaruka masu tsada,
ita kuwa lesuka ta bata da atamfa. Hajiya zuwaira
tace, ko qannensa da sukaje yini, sai da ta hado su da
kayan shafa. Gsky hajiya Bilkisu ki taka birki tunda
wuri. Domin in kk bari wannan rowar da rashin son
jama’ar nata yayi nisa, to kuwa nan gaba shi kansa
dan naki, kina ji kina gani, zai tsani danginsa, ya
kuma qanqame abin hannunsa.
Ran hajiya Bilkisu ya qara sosuwa, ta ce, ina zai yiwu!
Gobe zan turo su Aisha da samira, har Azima da
jamil, in gani suma rowar zatayi musu. Hajiya ladi ta
saka dariya, kinji hajiya Bilkisu, kema tayi miki rowa
ballantana wasu yaranki? Kawai danki zaki tasa a
gaba ki nuna masa cewa, yayi mata tarbiyyar kyuta
da son jama’a tunda an kasa yi mata gidansu. Hajiya
zuwaira tace, zancen kenan. Tafdijam! Wannan shine
gaba kura baya damisa. Na’imar da bata samu
kwanciyr hankali daga Abbas ba, ta yaya zata san
yadda zatayi abida ya kamata? Muje dai zuwa.
Haka kuwa washe gari sai Na’ima ta sake jin bugun
qofa, guraren qarfe dayan rana. Bata yi qasa a gwiwa
ba, ta tashi ta nufi budewa don kar ayi irin na jiya. Su
Aisha ne da samira da kuma Azima harda auta jamil.
Cikin ‘yar fara’a mai kama da yaqe tayi musu sannu
da zuwa. Suma suka amsa cikin isa, musamman
samira da Azima. Sun zauna, ita kuma ta nufi kicin
don kawo musu abin sha da dan na ta6awa sannan
ta sanar da masu aiki cewa, ga baqi a dora musu
abinci. Taje ta kawo musu hotunan biki.
Sannan ta zauna. Jin basu gaisheta ba tace musu, ina
yininku? Suka ce lfy. Aisha tace, ina bros Abbas fa?
Na’ima tace, ya fita tun safe, don tana daki taji
fitarsa. Samira tace, sis Aisha kin manta jiya bros
daya zo yace, zai koma aiki? Aisha tace, haka ne,
Na’ima tace, eh ya koma aiki yau. Ta fadi hakane
kurum, sbd kar su fahimci irin zaman da sukeyi. Sun
wuni cur, amma bataji dadinsu ba. Komai cikin isa
da nuna mata iyakar ta sukeyi. Sannan Abbas ya
shigo kusan shida na yamma.
Tana dag cikin daki tana jiyosu yana ce musu, kunci
kunsha duk abinda kk so, ko kuma anyi muku
rowar? Samira, wadda tafi kowa rashin kunya, tace,
an ma isa? Bros muzo gidanka ayi mana rowa? Za ma
mu jira kenan. Kowa abida take so, shi tasa masu aiki
suka dafa mata. Yace, kunyi daidai. Bari inyi wanka
inzo in kaiku gida. Aisha ce ta shigo tana ce mata.
Bros fa ya dawo. Tace to, sannan ta taso daga kan
gadon, ta nufi samanshi, cikin fargaba, sbd kar
qannensa su fahimci wani abu.
Ta tura qofar falon ta bude. Na’ima ta shiga cikin
fargaba. Yana zaune kan kujera yana ciro wasu
takardu daga cikin jakarsa. Tace sannu da zuwa. Baiji
shigowar ta ba, sai magana kawai yaji. Ya dago a
fusace, “lafiya? ” A tsorace kuma cikin faduwar gaba
tace, dama Aisha ce tace min ka dawo, kuma su baqi
ne dai, kada su gane cewa akwai wata matsala
Tsakanin mu. Ya watso mata harara. Don Allah fitan
min anan! An dade ba’a gane cewa, Tsakanin mu
akwai matsala ba. Waton ma jiya da Momyn mu
suka zo shine kkyi musu wulaqanci ko?
Na’ima ta riqe kanta sbd wani sarawa da yakeyi.
Tace, ai dai na basu haquri ban zaci sune suka zo ba.
Na zaci wannan matar ce data biyo ka. Yace, in itace
sai kiqi bude qofa tunda gidan babanki ne? To bari in
sanar dake, in baki sani ba, ta fiki matsayi. Ke har iko
ta fiki a gidannan. Sbd haka kibi a sannu. Sannan duk
lokacin da ‘yan uwana suka zo wani yayi kuka dake,
na rantse miki sai na zane ki. Fita! Wawiya kawai!
Na’ima ta dubeshi rai 6ace, kai bakasan darajar dan
adam ba. Ka sake ni kawai, don ba zan iya da wannan
wulaqancin ba. Yace, fita nace kiyi. Da kuka ta fito,
sbd 6acin rai har ta manta da baqin da suke gidan.
Gadonta ta fada tana kuka. Samira, suka kalli juna da
Aisha, lokacin da ta wuce su a falo. Har suka shiga
dakin, sallar magriba tana kwance tana kuka. Aisha
ce ta tambaye ta ko lafiya? Sam Na’ima bata tanka ba
har zuwa lokacin da suka gama shirinsu suka ce,
mun wuce, Na’ima bata daina kuka ba bare ta amsa.
Sun isa gida cike da dokin labarin kaiwa mahaifiyar
su. Aisha tana jinsu tana kallon su, samira Tana sanar
da mahaifiyar su cewa, Bros Abbas yasa Na’imar
kuka. Qila ma dukanta yayi. Azima kuma tace,
sannan munyi abinda muka ga dama a gdn. Aisha
tace, ku dai bakuda hankali, ina ruwan ku da kukan
ta?shiyajiya Bilkisu tace, yayi min daidai! Ai shiyasa
jiya daya zo na fada masa abinda tayi, sbd ya kwa6a
mata. Samira tace, mu ma da zamu taho ba tace
mana komai ba. Aisha tace, ku dai kuna da matsala
wlh, ba kuga tana ta kuka bane? Tayi tsaki, ta miqe ta
nufi dakinta. Ita dai ko a cikin ranta, bata so Bros
Abbas yaci zarafin matarsa ba. Domin ta ba ta
tausayi lokacin da take ta kukan. Na’ima kuwa kiran
layin momy nafisa tayi, amma bata daga ba. Don
haka sai ta tura mata saqon waya kan cewa, ita fa ba
zata iya wannan auren ba. Domin mimi ba qaramar
sa’a tayi ba, da bata kasance matar Abbas ba. Don
Allah ki ceci rayuwa ta. Sam ynxun na haqura da son
Abbas. Saqon yaje sama da minti goma sannan kiran
momy nafisa ya shigo. Na’ima ta tashi zaune, ta
tallafe kanta mai matuqar sarawa, sannan ta daga
wayar, momy tace, Na’ima yaya ne? Na’ima ta soma
kuka. Momy tace kashh! Ke kullum Sallamar ki kenan
kuka? Sake dukanki yayi? Na’ima ta sanar da momy
zuwan mahaifiyar sa da qannensa. Momy tace,
tirqashi! Abin harda danginsa? Na’ima tace, momy
kizo ki daukeni don Allah. Momy tace gobe zamuzo
da hajiya nana. Na’ima tace, don Allah mommy
kuzo. Tace karki damu zamuzo.
Kwanan Zainabu biyu a asibiti, amma babu labarin
alhaji. Innar ta kuwa taci bashi yafi na dubu goma.
Sawunta hudu a gidan Alhajin, amma bata samunsa.
Don haka sukayi shawara da aminiyarta yalwa cewa,
in an sallami Zainabu su wuce da ita gida kai tsaye, in
yazo ya biya kudin saita koma. Baban su Zainabu
kuwa yaje ya duba ta sau daya, bai kuma komawa
ba.
Zainabu kuwa kuka takeyi akan ba zata koma ba,
domin kwanakin nan da bata gidan, duk da cewa a
asibiti take yafi mata zaman gidansa. Hankalinta bai
sake tashi ba, saida ‘yan gidan su Ismail suka zo duba
ta, taji wannan fatu din tana cewa innar su wai sunzo
duba matar Ismail ne tayi hatsari. Innar su Zainabu
tace, ai yayi aure ne? Nan su fatu da sauran matan
gidan suka soma ba innar su Zainabu labari. Ai
maigidansa ne ya bashi ‘yarsa, ita kuma bataso, ta
gudu shine tayi hatsari. Daga nan Zainabu bata iya ci
gaba da saurarensu ba, ta shiga rera kuka. Daren
ranar bata runtsa ba, kenan Ismail yananan asibitin
yana jinyar matarsa.
Ita dai zata so ta sake ganinsa a rayuwar ta ko da
daga nesa ne. Ta san lallai ta rasa Ismail tunda har
yayi aure. Ta yi ta tuno kalaman da yake fada mata
na irin tsantsar son da yake mata. Washe gari da safe
innar ta taje famfo inda zata wanko ‘yan kayan
Zainabun, ita kuma zainabu ta sauko a hankali, ta
dauki zani guda daya daga cikin zannuwanta ta yafa
ta nufi fita. Matar kusa da gadonsu tace, ina zakije
Zainabu, ko bandaki zaki shiga? Tace a’a zan dann
tattaka ne, sbd jikina duk ciwo yake sbd zaman guri