Sashe 70
Canjin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
4⃣9⃣Lokaci yana qhudewa kwanaki quna qarewa, yau gashi su Na'ima anyi arba'in. Ta matsu qwarai tabar gidan minister, domin ko abincin da zataci sai taje kicin da kanta ta kar6a. Hatta 'yan aikin gidan sunsan batada wata kima, tunda a gabansu za'a zage ta tass. Don haka ko aiki tasa su basa yi mata. Sannan ga gadara da yaron, kullum akayi masa wankan safe, za'a tafi dashi gefen kakarsa, sai yamma ko in ya buqaci Nono. Da ma mai wanka da shirya shi musamman aka dauko. Shi kuwa Abbas sai dai ta jiyo muryarsa daga can sasan. Bata damu ba don ita ynxun ya gama sire mata. Kwana arba'in da bakwai suka maida ta gidanta bayan an kafa mata dokoki da sharudda akan yaron, sai kace ba itace ta haifeshi ba. Lokacin ne ma ta samu zuwa gidansu yini. Kuka momy Nafisa ta tasa Na'ima tayi tayi, sbd baqi data qara akan nata, gashi duk tayi zuru-zuru, idanu sun shige. Lokacin Alhaji bayanan Abuja, tace, bari dai yau dadynku ya dawo zan fada masa komai game da halin da kk ciki. Na gaji, gara komai zai faru, ya faru. Na'ima tace, yauwa momy don Allah ki taimaka min. In ba haka ba, wata rana zakije ki dauko gawata a gidan Abbas. Har dare Na'ima tananan tana jiran dawowarsa. Sun zauna sun karanto masa komai game da halinda Na'ima take ciki. Yace sam qarya ne, domin ta jima tanason kashema Na'imar aurenta. Su tashi su bashi guri. Ya kalli Na'ima, "karki daka ta mahaifiyarki, ki zauna dakinki shine cikar mutuncinki. Na'ima tace, Allah dady duk abinda kaji dinnan shine yake faruwa, yace kije zan bincika. Fitarta keda wuya, Alhaji Bashir ya kira layin Abbas. A tunanin Alhaji Bashir, Abbas da Na'ima duk daya ne agurinsa. Bayan sun gaisa, sai Alhaji Bashir yace, zantuka nakeji marasa dadi abakin Na'ima, tana fadamin wai bakwa zaman lfy tunda taje gidan. Shine na kira ka inji menene gskyr zancen? Abbas yace e.. to kusan akwai hakan daddy. Alhaji Bashir yace, to menene dalilin hakan Abbas? Abbas babu kunya ko shayi, yace, gsky daddy ina matuqar qoqari gurin zama da Na'ima, sbd gsky ni na wai ina sonta bane sam, Mimi nake so. "kalaman sukazo ma Alhaji Bashir a bazata, ya kuma fassarasu da cin fuska.
5⃣0⃣Amma sai ya danne, yace, in banda abin Abbas abinda yayi Mimi aishi yayi Na'ima, dukkansu 'ya'yana ne. Abbas yace, daddy Mimi fara ce mai aji. Na'ima baqa ce mai naci, amma aka dauki dauki Mimi aka ba wanda baisan darajata ba... "Dakata Abbas! Alhaji ya katseshi, cikin zafin zuciya. Yaya inayi maka magana kanayi min wani shirme? Zancen Mimi ba naka bane, qanwarta ce matarka, kuma a kanta muke yin magana. Bakason ta shine baka fada ba tuntuni, sai ynxun da kuka soma samun qaruwa? Ynxun dai abinda nakeso dakai, in tana yi maka wani laifi ne to sanar dani, sai in tsawata mata ta daina. Abbas yace, nidai son da banayi mata shine kawai matsalarmu. Alhaji Bashir yayi shiru, cikin Mamaki ya rasa me zaice, sai kawai yace, shikenan in ka samu lokaci kazo ina nemanka. Mamakin Abbas ne ya cika Alhajin, yadda yake magana cike da rashin ladabi. Kar dai ace yaronnan bashida tarbiyya. Sai kuma ya canza kiran wayarsa zuwa ga minista. Bayan sun gaisa, sai yace, ashe dama yaran nan zaman rashin jituwa sukeyi tun tuni? Minister yace, kamar yaya? Nan Alhaji ya kwashe komai ya fadawa minister har yadda suka yi ynxunnan. Sai kawai yaji minister yasa dariya, tare da fadin, karka shiga zancen yarannan. Baya sonta, yaya akayi ta haihu? Ya kamata da kayi masa wannan tambayar, lokacin daya ke fada maka cewa baya sonta. Alhaji Bashir yace, neman mata da tace yanayi shine matsalar ai. Minister yasa wata dariyar. "kar ta damu da wannan, in dai ya sauke mata nata haqqin. Kasan yarannan ba'a rabasu da son nishadi. Su kuwa mata, ai sune nishadin rayuwa. Kan Alhaji Bashir ya kulle, kenan ya daure ma dansa gindi yayi duk abinda yakeso, kuma bazai iya hanashi sa6ama Allah ba kenan? Minister ya katseshi da cewa, nayi zaton zakayi min magana akan hauhawar farashin man fetur ne? Alhaji Bashir yace, a'a ba wannan bane. Shi kenen saida safe mayi maganar kasuwanci, in Allah ya tashemu lfy, minister yace, Allah ya kaimu. Kada kasa kanka a damuwa game da batun wadannan yaran.
[22/09 11:55 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa
5⃣1⃣Kwana Alhaji Bashir yayi da abin a ransa. Washegari ya nufi katsina. Tun saukarsa hajiya sauda ta karanci damuwa can qasa tare dashi. Amma data tuntu6eshi, sai yace, wai babu komai. Ta takura masa da tambaya don ta fada masa cewa, saidai inba zai fada mata ba, to ba zata takura masa ba. Amma batun matsala tabas tasan yana ciki. Sannan ya fede mata komai. Yace, ni damuwata ban san ta ina zan 6ullo ma lamarin ba. Hajiya sauda cikin damuwa tace, dama Alhaji baku binciki halinsa ba? Yace, ni ina na wani bincika. A zatona yayi tarbiyyar 'ya'yansa, nayi hasashen sunada lfy tamkar nawa. Ashe nayi kuskure. Shi kansa ministan, sai ynxun nake sanin nasa halayen, sbd haduwarmu babu dadewa muka qulla wannan auren. Hajiya sauda tace, duk abinda ya faru, da kuma wanda zai faru nan gaba, duk laifinka ne, kai kawai ka duba abinda zaka samu ne kawai, ka dauki 'yarka ka bada. Yace, sauda abinda ya faru, ya riga da ya faru, sai dai a kori gaba. Ni ynxun roqo na a gurinki, ki bani shawara, domin kaina ya riga ya kulle. Hajiya sauda tayi shiru, tana tunanin me zatace. Gashi dai lokacin da za'a qulla abin ba'a nemi shawararta ba, sai ynxun da za'a kwance shi. Tanason ganin mijinta cikin kwanciyar hankali, musamman shida ke fama da ciwon suga. Don haka ba tare da ta tuno masa wani abu da yayi mata abaya ba tace, shawara dai daya ce, tunda shi uban yaqi kuyi batun, ka samu shi abbas din kuyi magana. In har baya sonta, da zaman uquba gara su rabu kawai, Allah ya hada kowa da rabonsa. Yace hakane kawai mafita, ai nayi da na sani babu adadi, har ina tozarta Mimi, ina cin zarafinta, ashe ba dan mutunci bane, kuma bai fito daga cikin mutunci ba. Hajiya sauda tace, kuskure ne dai ya riga ya faru, sai dai muce, Allah ya tsare gaba. Kwanansa uku ya koma Abuja sbd kawai ya gana da Abbas. Da safe Abbas ya sameshi a Gida. Bayan sun gaisa, yace, na kiraka ne don muyi magana ta fahimta, ni da kai. In har kana ganin bakason Na'ima to kawai ku rabu. Allah ya raya muku danku. Abbas yace, daddy ka samu daddy na kuyi magana, kamar yadda kukayi lokacin da zaku qulla auren, in ba haka ba zaice nine na saketa sbd banajin maganarsa. Alhaji yace ni zan masa bayani, abinda nawai nakeso shine ka fadamin abinda ke ranka Abbas yace, daddy nima inason a rabamu. Alhaji u, shikenan jeka zanyi magana da Dadyn naku.
5⃣2⃣Sai dai duk yadda Alhaji Bashir yaso suyi maganar da minister sam yaqi. Ransa ya 6aci sosai. Don haka ya taka har gidan Abbas ya samu Na'ima, ya tambaye ta ko akwai wani canji tsakaninta da mijinta? Tace, babu wani canji, domin ynxu ko wace irin mace kawowa yakeyi, kuma dole inyi musu girki, sannan ya daukarmin yaro ya kai musu shi, kowace jaruwa tayi ra daqunarsa. Yace, dauko mayafinki da kayanki kizo muje gida. Wannan shine mafarin tsiyar data 6arke Tsakanin Alhaji Bashir da minister. Qiriqiri minister yace, shifa bai yadda da wannan hukuncin ba, saidai inta koma can Gidansa da zama har zuwa lokacin da zata yaye jikan nasa, tabashi abinsa. Alhaji Bashir yace, wannan kuma wani abu ne da ba zai yiwu ba ko a cikin mafarki. Buqatarsa kawai Abbas yaba 'yarsa takarda, in ta yaye dansu, suzo su dauka. Wannan rigima itace ta datse kasuwancin da suka qulla suke aiwatarwa. Ikon Allah kenan. Shiyasa akace, komai mutum zaiyi, tofa yayishi don Allah.
Masu son Zainabu sunata fitowa tun daga lokacin da ta haifi danta saurayi, amma kowa fada masa takeyi tanada wanda takeso, duk da cewa ba tada tabbaci akan samun wanda takeson, ko inda yake bata samu labari ba, bare tasan ko zata samu shiga. Amma begensa yananan cikin Zuciyarta, dashi take kwana, tana tashi. Bugu da qari, dole inna ta zuba mata ido, sbd tsoron hukuma, duk da irin son kudinta. Ita fatanta Zainabu tunda ta haufi danta lfy, ta samu miji ta qara gaba, ko bata yaye danta ba. Su kuwa mutan madina suna can suna ta karatu, babu ji babu gani. Ismail ya qware sosai a fannin tafsiri, yana da haddar litattafai da dama a cikin kansa. Malamansu suna jinjina ma Qwaqwalwarsa sosai. Sun sake samun wani hutun, lokacin Rabi'a matar Mahmud tanada tsohon ciki. Wannan hutun sun sameshi daf da azumin watan Ramadan. Sunso tsayawa, amma sai Malam Aminu yace, su dawo sbd shine sukeson ya gabatar da tafsir a sabon masallacin da aka gina nan Unguwar su. Masallacin Juma'a ne katafare. Kuma lokacin azumi za'a budeshi. Don haka suka nufo gida cike da doki, sbd shi Ismail mutum ne maison ganin yana daukaka kalmar Allah, kuma jama'a su qaru da iliminsa.
[22/09 4:38 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa
5⃣0⃣Amma sai ya danne, yace, in banda abin Abbas abinda yayi Mimi aishi yayi Na'ima, dukkansu 'ya'yana ne. Abbas yace, daddy Mimi fara ce mai aji. Na'ima baqa ce mai naci, amma aka dauki dauki Mimi aka ba wanda baisan darajata ba... "Dakata Abbas! Alhaji ya katseshi, cikin zafin zuciya. Yaya inayi maka magana kanayi min wani shirme? Zancen Mimi ba naka bane, qanwarta ce matarka, kuma a kanta muke yin magana. Bakason ta shine baka fada ba tuntuni, sai ynxun da kuka soma samun qaruwa? Ynxun dai abinda nakeso dakai, in tana yi maka wani laifi ne to sanar dani, sai in tsawata mata ta daina. Abbas yace, nidai son da banayi mata shine kawai matsalarmu. Alhaji Bashir yayi shiru, cikin Mamaki ya rasa me zaice, sai kawai yace, shikenan in ka samu lokaci kazo ina nemanka. Mamakin Abbas ne ya cika Alhajin, yadda yake magana cike da rashin ladabi. Kar dai ace yaronnan bashida tarbiyya. Sai kuma ya canza kiran wayarsa zuwa ga minista. Bayan sun gaisa, sai yace, ashe dama yaran nan zaman rashin jituwa sukeyi tun tuni? Minister yace, kamar yaya? Nan Alhaji ya kwashe komai ya fadawa minister har yadda suka yi ynxunnan. Sai kawai yaji minister yasa dariya, tare da fadin, karka shiga zancen yarannan. Baya sonta, yaya akayi ta haihu? Ya kamata da kayi masa wannan tambayar, lokacin daya ke fada maka cewa baya sonta. Alhaji Bashir yace, neman mata da tace yanayi shine matsalar ai. Minister yasa wata dariyar. "kar ta damu da wannan, in dai ya sauke mata nata haqqin. Kasan yarannan ba'a rabasu da son nishadi. Su kuwa mata, ai sune nishadin rayuwa. Kan Alhaji Bashir ya kulle, kenan ya daure ma dansa gindi yayi duk abinda yakeso, kuma bazai iya hanashi sa6ama Allah ba kenan? Minister ya katseshi da cewa, nayi zaton zakayi min magana akan hauhawar farashin man fetur ne? Alhaji Bashir yace, a'a ba wannan bane. Shi kenen saida safe mayi maganar kasuwanci, in Allah ya tashemu lfy, minister yace, Allah ya kaimu. Kada kasa kanka a damuwa game da batun wadannan yaran.
[22/09 11:55 am] Inna👬👫: Canjin rayuwa
5⃣1⃣Kwana Alhaji Bashir yayi da abin a ransa. Washegari ya nufi katsina. Tun saukarsa hajiya sauda ta karanci damuwa can qasa tare dashi. Amma data tuntu6eshi, sai yace, wai babu komai. Ta takura masa da tambaya don ta fada masa cewa, saidai inba zai fada mata ba, to ba zata takura masa ba. Amma batun matsala tabas tasan yana ciki. Sannan ya fede mata komai. Yace, ni damuwata ban san ta ina zan 6ullo ma lamarin ba. Hajiya sauda cikin damuwa tace, dama Alhaji baku binciki halinsa ba? Yace, ni ina na wani bincika. A zatona yayi tarbiyyar 'ya'yansa, nayi hasashen sunada lfy tamkar nawa. Ashe nayi kuskure. Shi kansa ministan, sai ynxun nake sanin nasa halayen, sbd haduwarmu babu dadewa muka qulla wannan auren. Hajiya sauda tace, duk abinda ya faru, da kuma wanda zai faru nan gaba, duk laifinka ne, kai kawai ka duba abinda zaka samu ne kawai, ka dauki 'yarka ka bada. Yace, sauda abinda ya faru, ya riga da ya faru, sai dai a kori gaba. Ni ynxun roqo na a gurinki, ki bani shawara, domin kaina ya riga ya kulle. Hajiya sauda tayi shiru, tana tunanin me zatace. Gashi dai lokacin da za'a qulla abin ba'a nemi shawararta ba, sai ynxun da za'a kwance shi. Tanason ganin mijinta cikin kwanciyar hankali, musamman shida ke fama da ciwon suga. Don haka ba tare da ta tuno masa wani abu da yayi mata abaya ba tace, shawara dai daya ce, tunda shi uban yaqi kuyi batun, ka samu shi abbas din kuyi magana. In har baya sonta, da zaman uquba gara su rabu kawai, Allah ya hada kowa da rabonsa. Yace hakane kawai mafita, ai nayi da na sani babu adadi, har ina tozarta Mimi, ina cin zarafinta, ashe ba dan mutunci bane, kuma bai fito daga cikin mutunci ba. Hajiya sauda tace, kuskure ne dai ya riga ya faru, sai dai muce, Allah ya tsare gaba. Kwanansa uku ya koma Abuja sbd kawai ya gana da Abbas. Da safe Abbas ya sameshi a Gida. Bayan sun gaisa, yace, na kiraka ne don muyi magana ta fahimta, ni da kai. In har kana ganin bakason Na'ima to kawai ku rabu. Allah ya raya muku danku. Abbas yace, daddy ka samu daddy na kuyi magana, kamar yadda kukayi lokacin da zaku qulla auren, in ba haka ba zaice nine na saketa sbd banajin maganarsa. Alhaji yace ni zan masa bayani, abinda nawai nakeso shine ka fadamin abinda ke ranka Abbas yace, daddy nima inason a rabamu. Alhaji u, shikenan jeka zanyi magana da Dadyn naku.
5⃣2⃣Sai dai duk yadda Alhaji Bashir yaso suyi maganar da minister sam yaqi. Ransa ya 6aci sosai. Don haka ya taka har gidan Abbas ya samu Na'ima, ya tambaye ta ko akwai wani canji tsakaninta da mijinta? Tace, babu wani canji, domin ynxu ko wace irin mace kawowa yakeyi, kuma dole inyi musu girki, sannan ya daukarmin yaro ya kai musu shi, kowace jaruwa tayi ra daqunarsa. Yace, dauko mayafinki da kayanki kizo muje gida. Wannan shine mafarin tsiyar data 6arke Tsakanin Alhaji Bashir da minister. Qiriqiri minister yace, shifa bai yadda da wannan hukuncin ba, saidai inta koma can Gidansa da zama har zuwa lokacin da zata yaye jikan nasa, tabashi abinsa. Alhaji Bashir yace, wannan kuma wani abu ne da ba zai yiwu ba ko a cikin mafarki. Buqatarsa kawai Abbas yaba 'yarsa takarda, in ta yaye dansu, suzo su dauka. Wannan rigima itace ta datse kasuwancin da suka qulla suke aiwatarwa. Ikon Allah kenan. Shiyasa akace, komai mutum zaiyi, tofa yayishi don Allah.
Masu son Zainabu sunata fitowa tun daga lokacin da ta haifi danta saurayi, amma kowa fada masa takeyi tanada wanda takeso, duk da cewa ba tada tabbaci akan samun wanda takeson, ko inda yake bata samu labari ba, bare tasan ko zata samu shiga. Amma begensa yananan cikin Zuciyarta, dashi take kwana, tana tashi. Bugu da qari, dole inna ta zuba mata ido, sbd tsoron hukuma, duk da irin son kudinta. Ita fatanta Zainabu tunda ta haufi danta lfy, ta samu miji ta qara gaba, ko bata yaye danta ba. Su kuwa mutan madina suna can suna ta karatu, babu ji babu gani. Ismail ya qware sosai a fannin tafsiri, yana da haddar litattafai da dama a cikin kansa. Malamansu suna jinjina ma Qwaqwalwarsa sosai. Sun sake samun wani hutun, lokacin Rabi'a matar Mahmud tanada tsohon ciki. Wannan hutun sun sameshi daf da azumin watan Ramadan. Sunso tsayawa, amma sai Malam Aminu yace, su dawo sbd shine sukeson ya gabatar da tafsir a sabon masallacin da aka gina nan Unguwar su. Masallacin Juma'a ne katafare. Kuma lokacin azumi za'a budeshi. Don haka suka nufo gida cike da doki, sbd shi Ismail mutum ne maison ganin yana daukaka kalmar Allah, kuma jama'a su qaru da iliminsa.
[22/09 4:38 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa