← Book details Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 47

Sashe 7

Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kokarin rabata da jikinshi yake yana fadin Ohh sorry gaisuwa ce fah, *Duna* kenan meyasa kin cika tsoro.......

Heart beat
*Mmn Yazeed*鈥�
[22:50, 12/19/2017] 鈥�+234 806 858 0203鈥�: 馃挆馃挐馃挐馃挆
鈥�*BUGUN ZUCIYA*鈥�
( 鈥婬eartbeat鈥�)

馃挀馃挐馃挆
馃挆

馃挀馃挐馃挆
鈥婤y鈥�
馃挆
鈥嬧€�*Fadeela Lamido*

*@AM拢拢NCI WRITER'S ASSOCIATION馃*

*Na sadaukar da wannan shafin gareki馃憞*
馃憫Queen馃憫馃槝

*Nima ILove u wojuga wojuga wlh馃槏*馃嵀

1鈨�5鈨� to 1鈨�6鈨�

馃搾 Jin ya ambaci gaisuwa ce yasata jan jikinta ta koma gefe, tare da karabin karan da kallo"

Haryanzun hijjabinta na bakin shi, matsowa yayi ya ajiye hijjabin akasa sannan ya koma kusa da deeni yana goga kanshi ajikin deeni"

Sai alokacin ma'u ta tuna jikinta babu hijjabi hannu tasa ta rufe kirjinta, sannan ta matsa ta dauki hijabinta ta saka"

Karan tabi da kallo har yanzun Yana gaban deeni sai shafamai kai yake alman lallashi"

Tsaki taja azuciyarta sannan tace wannan bakin karan ne duna, ganin inda yake lallashin karan abin yai matukar bata haushi, hawaye ta fara matsowa acikin zuciyarta tace yanzun akwai miyon wannan mumman karan ahijjabi na wlh Allah ya isa, bata san cewa mgnr ta fito fili ba saiji tayi deen na fadin wa kikeyiwa Allah ya isa.....

Atsora ce tace ni bada kai nake ba, da wannan mummunan karan naka nake"

Ke *duna* kike kiran mummuna kinyi na farko yariya karki kara, idan kuma kika kara zan barki dashi"

Kallo kawai ta bishi dashi har yanxun lailaya kan Karen yake, harga Allah haushi yake bata dan me xaisa hannun sa yaita shafa kare batasan lokacin da tace toh kadaina shafashi haka mana"

Inaruwan ki ko kanki nake shafawa?

Kasa tayi dakai tana cigaba da kunkun"

Tunda ta fara motsa bakinta deen
yake kallon bakin amman ya kasa gane kalma daya da take Dada dan haka yace banajin abinda kikecewa"

Turo baki tayi sannan tace ai badakai neke ba"

OK da *Duna* kike kenan?

Shiru tayi batare da tace komai ba dan haka deen yayiwa caka mgn da hannusa gani tayi ya matsa can gefe ya tsaya atsakiyan hanya"

Kallonta ta mayar kan deeni gani tayi ya dago kan *Duna* yana mai mgn da ido aguje yayo kanta tare da haushi irin na mahaukatan karnuka"

Cikin gidan su deen tashiga aguje ummi na zaune tana wanke2 tayi fatali da ruwan cikin jikita ta shige ta kwakumeta"

Kobata tambaya ba tasan karen deen ne ya biyota dan tun dazun takejin haukan sa, rungumeta tayi ajikinta tare da fadin uban gidan nasa baya wajen ne ya bari yana tsorata Ki?

Sai alokacin kuka ya kwace mata cikin kukan tace ai shine yace mai ya biyoni"

Daidai lokacin deen ya shigo yana murmushi harara ummi a zubamai sannan tace nadai hanaka shigowa da karan nan uguwar nan kaki bari ko?

Ummi nakawoshi ne yagaida wannan yariyan ita kuma sai zaginshi take"

Ai dole ta xageshi auta tunda bata saba ba ita gani take tsoratata yake, yanxun zoka rakata ta shiga makaranta"

Makaranta ? Yau bazata makaranta ba lokacima ya kure"

Bude baki ummi tayi xatayi mgn amman deen sai ya mata wani irin siririn fito tare da kada mata hannu nan danan taja bakinta ta tsuke , shiko deen dakin sa ya shiga"

Daga ma,u har ummi tsaye suke saidai jikin ummi asanyaye yake kamar tana cikin damuwa"

Zuwa can ta waigo tace Asmau dan Allah ga abincin auta nan a kitchen taimaka ki kai masa rabon sa da abinci ya dade basan me yake damunsa ba"

Shiru ma,u tayi kanta akasa acikin zuciyarta tace toh meyasa bayacin abinci? Afili ko cewa tayi ummi wlh tsoron shi nakeji"

Murmushi ummi tayi sannan tace a'a karkicemin kinajin tsoron sa keda mutumin ki kuma? bubu abinda zaiyi miki tashi maza kije"

Jikinta babu kwari ta nufi dakin da taga deeni ya shiga sallama tayi abakin kofar bayan ya amsa tashiga"

Dakine dan karami daga can gefe akwai yar karamar katifa gefen katifan ko wukakene an jigine su a jikin bango"

Gyare dakin yake tsaf ahankali ta karasa gaban katifan ta aje kwanan tana kokarin mikewa ya rike hannun cikin sauri ta dago ta kalleshi"

Ido suka tsurawa juna natsayon wanni lokaci take ma,u taji tsigan jikinta na tashi nan danan idonta yacika da kwalla amman takasa dauke idonta akanshi"

Shiko deen wani irin farin ciki yakeji wadda betabajin irinsa ba har yanajin inama su kwana ahaka"

Murmushi yasaki wadda yai matukar dacewa da fuskanshi azuciyar ma,u cewa tayi inama ace haka fiskarshi take kullum"

Kasa ta sauke idonta tare da sauke ajiyan zuciya, haka shima deeni ajiyan zuciya ya sauki sannan yasa hannun shi ya sake dago fuskanta"

Runtse idonta tayi cikin wata dashashshiyar murya taji yace *Asmau* bude idonki ki kalleni"

Koro na farko da deeni ya kira sunanta agabanta dan haka taji yafi kowa iya kiran sunanta"

Bude idon tayi saidai baxata iya kallon sa ba kamar yadda yace dan haka ta durkusan da kanta kasa"

Jawota yayi daf dashi ya zaunar sannan yace meyasa kwana 2 baki zuwa makaranta?

Ina xuwa ta fada atakaice"

A'a karya ne bayan kullum inajiran ki akofar gida amman ban ganin wucewan ki"

Wlh kullum ina zuwa bandai wucewa ta nan ne "

Me yasa ?

Shiru tayi tana tunanin tagayamai abbanta yace zaiyi mata aure ne ko karta gayamai, idan bata gayamai ba toh mezata cemai?

Tunanin me kikeyi?

Bakomai "

Shiru yayi xuwa can yasake dagowa yace yau kinji ganina kenan shine kikazo kina leka mana gida"

Turo baki tayi kaman zatai kuka zuwa can taji ya sake cewa wadda ya dauki ki a mota ranan shine babanki?

Eh tace tare da kurawa kirjin shi ido"

Shiru yayi yana kallonta zuwa can yace me kike kallo?

Kai tsaye ta nunamai sarkan dake wuyan sa"

Kina sone?

Tana wasa da yatsunta take fadin a'a kacire ne beyi maka kyauba"

Dariya yayi sosai har hakoran shi suka baiyana zuwa can yace naji tunda bakison ganina da sarka saikizo kicire da kanki"

Tana cigaba da wasa da hannunta tace kacire da kan ka ai babu kyau mace ta dinga taba namiji"

Axuciyar shi yace kina da wayo babu kaifi afili kuwa cewa yayi toh bakison nadaina sawa kenan?

Mikewa tayi tare da fadin nixan tafi kar atashi amakarata bansani ba"

Daure fuska yayi sannan yace dawo ki zauna, idan lokaci yayi zan fada miki"

Zama tayi nesa dashi badan ranta yaso ba, kanshi ya turo mata ahankali ta fara warware sarkan duguwa ce sosai, kallon sarkan take tana mamakin wai mutum da hankalin sa ya dauki wannan karfen yasa ajikin sa"

Shiko deeni kallonta yake yana murmushi yana da tabbacin yadda *ZUCIYAR* shi ke buguwa haka ta ma'u ma take bugawa, xuben da ke karamin yatsan shi yacire ya kamo hannun ma'u ya zura mata"

Harcikin zuciyarta taji dadi kallon zuben tayi sannan tace nagode"

Murmushi yayi sannan yace toni me xaki bani?

Tsintan kanta tayi da cewa me kakeso na baka?

Duk abinda kika bani zanyi farin ciki dashi"

Cikin sauri ta ciro xoben da abban ta ya saya mata ta mikamai"

Nuke kafada yayi kaman yadda yara keyi yace bazan karba ba, ni ai saka miki nayi dan me xaki bani ahannu"

Shiru tayi cikin rashin jin dadi zuwa can tace ka karba ai be dace bane ina mace kuma.. ..

Kasa karasawa taayi dan haka deen yaja tsaki ya kwatar da kanshi akan katifan"

Ganin haka yasa ma'u taji babu dadi dan haka ta kamo hannun saidai duk yatsan da ta nufa zuben baya shi, daker ya shiga karamin yatsan shi, shima be gama shewa ba"

Tagama sawa tana kokarin mikewa ya mirginota jikinsa ya rungumeta tsam ajikin shi, tare da sunbata goshinta kumatunta zuwa kan lebenta, neman rikicewa yake, dan haka ma'u tafara kokari kwace kanta take mgnr abbanta ya fado mata, hawaye taji yana zubu mata"

Daidai lokacin ummi ta dago labulen cikin sauri deen ya mirgina ma'u gefe sannan ya cigaba da sauke ajiyan *ZUCIYA*"

Cikin sauri ma'u tamike tana gyara hijjabinta"

Itako ummi kallon deen take cikin bacirai zuwa can tace auta har ka manta alkawarin dakamin?

Be iya cewa komai ba dan koya bude baki besan me zaice ba"

Yana kwance yanajiyo fadan ummi, dakanta ta rike ma'u tayo waje da ita"

Jin asmau zata tafi yasashi mikewa dasauri ya fito samu yayi daidai ummi ta budewa ma'u kafar cikin sauri ya rike hannuta tare da zuba mata jajayen idon shi sannan yace gobe zaki zo ?

Tana share hawaye tace eh"

Murmushi yayi kadan sannan ya karkata kai"

*****

Tafe take tana kuka dan daganin yanayin garin andade da tashi makaranta"

Ta saka wannan ta kwance wancen tana tunanin wata karyan zata shirya"

Taci rabin ta fiya taga motar yaya usman ta wuceta"

Innalillahi ta fada azuciyarta Allah yasa be ganeni ba"

Hango motar tayi ta tsaya tana dawowa da baya"

Jitayi 'ya'yan hanjinta na motsawa daidai saitinta yaya usman ya tsaya ya zubo mata idonta shi sannan yace ke sai yanzun kike dawowa daga makarantar?

Mutumin dake zaune agefen shi ta kure da ido, gani take kaman kunki ne domin kwata2 baya motsi, jarida ce bude ahannun shi idonshi sanye da farin glass"

Yaya usman ne yace kagamin shegiyar yariya ina mata mgn tana kallon wani guri"

Zabura tayi ta dawo cikin hankalinta ta kara matso kuka tace"

Yaya wlh kare ne ya tareni ahanya ya hanani wucewa.....

Kutumar ubanki shigiya yar iska, ni xaki rainawa hankali duk cikin daluban be tare kowa ba saiki ? A ina kika tsaya?

Cikin kuka ta tattaro hijjabinta tace wlh yaya da gsk ne kagama yadda karan ya lalatamin hijjabi"

Takaici ne ya kama usman dan haka yace Allah ya kara, dayasani ma ya ciccije ki dan ubanki, kin tsaya shashanci duk dalubai sun wuce sun barki dallah dobeki saikace doluwa, ni shiga mota mutafi"

Tashiga mota? mutumin dake kusa da yaya usman ya tambaya batare da ya waigo ya kalleta ba har yanzun idonshi nakan jaridan"

Waigawa usman yayi ya kalleshi sannan yace wannan itace kanwata *Asma'u* danake baka lbr, wlh kwata2 yariyar nan batajin mgn"

Idonshi akan jaridan yace aina ganeta, kanta na rawa, naji kaman kana cewa ta hau mota, ai kamata yayi ta isa gida kafin mu isa"
Chapter 7 · 0% Book details