← Book details Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 47

Sashe 39

Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dagowa Jamal yayi ya kalli usman sannan yace eh ninayi"

Kaika yi?

Eh, ya fada tare da jawo bargo ya rufe kansa"

Girgiza kai yayi tare da fadin gaskiya Jamal basan baka da hankaliba saiyau, banga amfanin zamana agidan nan ba wlh, yau yau zanbar garin nan, nakashe komai nawa nabaro aikina da iyalina dan nayi jinyanka amman kun maidani hoto, ni dan iskane haka kawai zakasa yariya ta rainani, Ashe shiyasa kwanaki da doctor yace ansawa kafa ruwa, dagewa kayi kai baka saba har kanacewa wai nina zuba maka, narantse da Allah dakai karamin yaro ne saina maka matsiyacin duka zanbar garin nan"

Bude fuska Jamal yayi sannan ya kalli usman yace....

Haba usman yazaka tasani agaba kaitamin fada, Husna fa matata ce, ba zina nayi ba"

Ai bance ba matarka mace amman ai anabarin halas kodan kunya sannan ga ciyon dake jikin ka, baka tunanin gurin ya samu matsala ko fah taka kafar ance karkayi"

Nifah usman bantaba karanta aya ko hadisi daya fadi haka ba, kuma ni wannan ciwon be isa ya kashemin rayuwa ba"

OK toh shikenan, azuciye usman ya fita"

Daddare ma'u na zaune momy ta shiko tace biyoni"

Hijjabinta tasa tabita abaya, dakin da Jamal yake ta nufa dan haka tabi bayan Sa"

Ma'u na shiga taga daddy adakin dan haka hankalinta ya kara tashi"

Tunkafin momy ta zauna daddy yace....

Asma'u taho nan Ki zauna"

Inda ya nuna mata ta zauna tare da matso hawaye"

Ahankali daddy yace.....

Jamal ance matarka nada cikin sati 2, shine nake son sanin ko naka ne?

Muyar kasa kasa yace eh"

Shiru daddy yayi sannan yace toh nakane dai kace ko?

Eh yasake fada ahankali"

Shiru daddy yayi zuwa can yace....

Toh Alhamdulillah Allah ya rabasu lfy, daman bawani abu bane yasa na tambaya saidan naga baka lfy, kuma matsalar acinya take, shiru ya sake yi sannan ya sake cewa toh shikenan babu koma, jiya usman yace ka kwana kafa na damun ka, dan haka yanzun likita zaizo ya dubaka"

Momy ko babu abunda take banda hararan Jamal ammam saiyaki kallonta"

Karfe 8:00pm likita ya shigo kwance kafar yayi yana mamakin yadda akayi gurin ya rarike haka"

Ganin inda doctor yake kallon gurin yasa daddy da momy lekawa, sosai gurin ya zurma, juwa yayi ya kalli Jamal yace kafannan anasa mata ruwa meyasa bazaka taimaki kanka ba, kaifa ba karamin yaro bane, meyasa zakana mayar mana da aiki baya"

Haka Dr yaita fada daga karshe ya wanke wajen sannan ya kara ja musu kunne"

Likitan na fita momy ta rufe Jamal da fada, ta inda take shiga ba tanan take fitaba"

Daidai lokacin usman ya shigo nan momy ta kwashe yadda sukayi da dr ta gayamai, sannan ta kara da cewa ashe Jamal da kanshi yake shekawa kansa ruwa saboda rashin hakuri irin nashi, wai ahaka dinnan ya danne yariya ya dirka mata ciki"

Daddy ne ya fara dakawa momy tsawa tare da fadin wai menene haka?

Itama cikin takaici tace barni alhaji abin ne yake bani takaici wlh, ji inda usman ya kashe komai nasa ya zauna dan yaga kasamu lfy"

Jamal ji yayi kamar ya nutse saboda tsabar kunya"

muyar usman game yana cewa.....

Aini momy gobe da sassafe zanbar garin nan, Asma'un tayi jinyar shi"

Kwama cala kenan, usman babu inda zaka, dan wlh idan akabar Jamal da asma'u adakin nan kafar Jamal rubewa zatayi"

Daddy kallo yabi Momy dashi sannan ya girgizakai ya fice domin kalamanta kunya take bashi agaban yara"

Momy naganin fitan dadddy tace....

Gobe idan Allah ya kaimo dakaina zankai Asma'u Kano taje taji da abinda ke cikinta, badan bazan iya jinyarta ba, saidan dan wannnan me wutan cikin....

Heart Beat
*Mmn Yazeed*
💗💝💝💗
​*BUGUN ZUCIYA*​
( ​Heartbeat​)

💓💝💗
💗

💓💝💗
​By​
💗
​​*Fadeela Lamido*

*@AM££NCI WRITER'S ASSOCIATION🤝*


Dedicated
*Sadnaf*👍🏻💋

9⃣6⃣to9⃣8⃣

Jamal be sake kallon inda suke ba, itako ma'u tana takure agefe"

Tattaunawa suka cigaba tsakanin momy da usman daga karshe momy taja ma'u suka wuce"

Adakinta ma'u ta kwana motsi kadan momy taji ma'u tayi zatace me kike so?

Washegari da safe momy da kanta ta hadawa ma'u kayanta sannan tace tayi wanka su tafi"

Wankan taje tayi saidai jikinta babu dadi hakama zuciyarta, azahiri batason Tafiyan tafison ta zauna gurin mijinta"

Bayan ta gama shiryawa ta zauna momy kadai take jira, tsintan kanta tayi da rafka uban tagumi"

Ahaka Momy ta sameta, dan haka ta tsaya cak tanabin ta da kallo sannan ta karasa kusa da ita tare da kiran sunan ta"

Ma'asawa tayi tare da kallon momy"

Ahankali momy tace.....

Asma'u anya kuwa kinason tafiyan nan?, kodai za'abar tafiyan ne?

Cikin sauri ta girgizakai tare da fadin inaso"

A'a asma'u bayan gashi naga duk kin shiga damuwa, ni asma'u bawai inason na rabaki da Jamal bane, wlh ciwon shine yake tayar min da hankali, kuma shi duk abinda likita yafada beji, idan wani abu ya faru Mu zai bari da wahala"

Nisawa tayi sannnan taci gaba da cewa kiyi hakuri nasani daga ke har Jamal bazakuji dadin hukunci na ba amman nan gaba zaku gane gata ake muku"

Tashi sukayi da nafisa kadai sukai sallama suka dauki hanya"

Karfe 2:38pm suka isa Kano suna isa gidan ma'u taga komai ya canja, kamar bata taba rayuwa agidan ba"

Mehadin ne yafara shiga da akwatin ma'u anan ne mama tagane sunyi baki"

Har sukashi falon momy na rike da hannun ma'u"

Da fara'a mama ta tarbe su, nan tashiga hidima dasu, bayan sun natsa ma'u tashi ta basu guri"

Dakinta na da ta shiga nan abubuwa da dama suka dawo mata, kwallace tacika mata ido, rayuwan su da deeni ne ya fara fado mata, dan haka batasan sanda ta fara hawaye ba"

Anan bacci ya kwasheta batare da tasan lokacin ba"

Ta dauki dogon lokaci tana bacci sai can kusan yamma ta farka"

Tana tashi taga wayarta tare da kudin masu yawa agefenta, kwasan kudin tayi ta nufi falo"

Babu kowa afalon dan haka ta nufi kitchen acan ta samu mama tana aikace2"

Mama na kallonta tayi murmushi tare da fadin Asma'u kin tashi?

Cikinjin kunya tace natashi mama ina momy"

Ai tuni ta wuce"

Mun shigo kina bacci tace abarki kar atashe Ki"

Wani iri taji azuciyarta, amman taki bari mama ta gane"

Tare da ma'u suka karasa aikin, bayan sungama tacewa mama zata gidan yaya usman"

Shiru mama tayi zuwa can tace......

Kin ganki, daga zuwanki zaki fara yawace yawace"

Turbune fuska ma'u tayi sannan tace.....

Mama gidan yaya usman din ne yawo? ni idan na tafima sai gobe zan dawo"

Tabe baki mama tayi sannan tace toh ai saiki bugawa mijinki waya idan ya amince drive ya sauke ki"

Da saurinta ta juya daki gyalenta ta dauka ta saka sannan ta fito ta samu mama zaune agefen kujera"

Kallonta tayi tace kinmai wayan ko?

Eh kawai tace tare da gyara gyalenta"

Sosai fa'iza tayi murnan ganin ma'u suna rungume da juna, zuwa can ta kalli ma'u ta sheke da dariya"

Dariya taitayi harda rike ciki, ma'u ta tsaya sororo tana kallonta"

Zuwa can fa'iza ta sarara da dariyan sannan ta kalli ma'u tace.....

Asma'u kenan, jiya keda mijin ki kuncikawa yayan ki ciki, ashe Jamal dan duniya ne ban sani ba?

Tsaki ma'u taja sannan ta daure fuska tare da fadin anty dan duniya fa kika ce?, kina nufin dan iska ne?

Cikin sauri fa'iza tasa hannunta abaki tare da fadin alallai, ni karkimin fassara bahaka nake nufi ba, kallon ma'u ta karayi har yanzun ranta abace yake, cikin ido ta kalli ma'u tace sai yau na yadda kiyayya tana komawa soyayya, kuma na yadda duk abinda babba ya hango yaro ko yahau rimi bazai gano shiba"

Saboda me kika ce haka?

Murmushi fa'iza tayi sannan tace.......

Na tuna lokacin da kike cewa ke bakison jamal kin tsane sa, ke har cewa kikayi idan aka aura miki shi saikin kasheshi, sai gashi yanzun kin fada kyaunar Jamal dumu dumu, lokacin da Jamal ya bace kika zama kamar zararriya, da ace har yanzun ba'aga Jamal ba wata kila dakin zare"

Shiru ma'u tayi tana nazari, zuwa can tace Anty?, wlh da kwata kwata bani da hankali, idan na zauna ina tunani sainace da wani hauka ne ya shigeni, dan rashin hankali na zauna naita musu dasu Abba, yana cewa ga abinda zanyi inacewa ga wadda nake so, sai yanzun naki ganin illar sarashin jin maganar iyaye, ba dama nayiwa yaya jamal wani dan abu nan danan saiya hassala yaita fada, dan haka yanzun duk abinda yace banamai musu inba haka ba saiyace ai lokacin deeni kaza, akwai wata mgn da mukayi nida deeni bakaramin mamaki nayi da naji abakin yaya Jamal ba, nan ta kwashe komai tagayawa fa'iza"

Jinjina kai fa'iza tayi tare da fadin gsky kuruciyar ki kinyi hauka da yawa, to yanzun gayamin matsayin deeni azuciyar Ki"

Cikin sauri tace....

Deeni?, wlh bana son ganin deeni domin idan naganshi tausayin shi yana kamani, Anty bazan boye miki ba, ayanzun inajin son Jamal kuma bana neman abun da zai rabani dashi, zama na dashi yasa na fahimci halin shi, halayen shi masu kyaune, dabi,un shi suna burgeni, anty yaya Jamal be faye son mgn ba duk abin da zai fito bakinsa me mahimmanci ne, sannan nakula yana tsananin sona dukda yana boyewa bayason nagane ko wani ya gane haka"

Nisawa tayi sannan taci gaba da cewa anty yaya jamal ya dade yana sona amman be bari kowa ya saniba yaita dannewa, kuma koda naje gidansu amatsayin matar sa ko kallo na bayayi, yana nuna bana gaban shi, Amman bayan bacewan shi da aka gano jakarshi nagono sirrikan shi da dama, hutonane bila adadin awayar yaya Jamal wadda bansan sanda ya dauke su ba, sannan hutonane akan wayar Sa, tun alokacin naji sonshi ya ratsa ko ina ajikina"

Dariya fa'iza tayi sannan tace Jamal dai yaci gari kenan?, ya ture gwamnatin deeni"

Girgiza kai tayi tare da fadin to anty idan ma inasonshi yaya zanyi?, da dai ammana umarni da auren maza 2 to wlh dana kara da deeni dan wlh tausayin deeni ya hanani nayi walwala, ina tananin tausayin sa, kuma inaso rayuwar sa ta inganta, wani lokacin inaganin laifin zuciyata data fada son jamal"
Chapter 39 · 0% Book details