← Book details Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 47

Sashe 47

Bugun Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Aliyu nada wata 7 Nafisa ta sake haihuwan Jafar"

Zuwa wannan lokacin Jamal da deeni suna mgn sama sama, yadda yaga deeni na nuna soyayyar nafisa ako ina yasa jamal ya saki jikinshi, kullum cikin kara ririta ma'u yake"

Sosai Abba yakejin daddy idan ya tuna Asma'u na dakin mijinta, Jamal betaba kaimai karanta ba, kullum yaje gaida Abba idan xai tafi ya dinga godiya kenan"

Ita ko ma'u akullum suka hadu da Abba albarka yake saka mata"

Bayan ma'u ta yaye aliyu ne Jamal ya maida ma'u makaranta domin ta cigaba da karatunta"

Manyan hijjabai ya saya mata dakan shi yake kaita indai yana gari"

Bayan shekara 3

Ma'u na daf da karasa karatunta, ta fara laulayin ciki, tashin hakali ta nuna sosai, ganin haka Jamal yaita kwantar mata da hankali tare da nuna mata ai ciki bazai hanata karasa karatu ba"

Lallashinta yaita yi tana dada narkewa ajikinshi tare damai shagwaba iri iri, biye mata yai tayi, har ta saki jikinta"

Itako nafisa cikin na hudu ne ajikin ta, kulawa deeni yake sosai wajen basu tarbiya, baya wasa, beciga son kaisu gidan abbashi bashir ba, daya kaisu aranan yake komawa ya dauko su betaba bari sun kwana agidan ba, duk da yasan cewa komai ya zama daidai amman hankalin shi baya kwanciya"

Gidan momy ko aduk sanda suka samu hutu can yake kaisu har hutun ya kare, dan haka mushkur da yan biyu suka kule, wasa suke sosai"

Cikin ma'u ya tsufa dan haka Jamal ya matsa zai koma gidan shi, momy taso ya bari sai ma'u ta haihu amman ya dage"

Acewar shi tunda da tace tsoro take ji yanzun ai ga yara nan ta samu"

Sun koma da sati 2 ma'u ta haifi 'ya mace"

Kowa ya kalli yariyar cewa yake da ma'u tai kama, amman Jamal dagewa yayi wai shi ta dauko, haushi ma'u takeji idan jamal yace shi ta biyo, dan haka ta fara daure fuska"

Nafisa ce taita sintiri zuwa gidan da goyota abaya har akayi suna ayanzun yaran nafisa 4 kuma duk maza ne, yayin da ma'u keda 4 amman haihuwanta 3"

***

Yanzun Hassan da Hussaini suna da shekara 10, girma sukai na ban mamaki farare ne tas idan ba wadda ya sansuba baya iya babbaci su"

Wayon tsiya gare su, idan ka kalli ma'u baka taba cewa ita ta haife su, shi kanshi Jamal idan ya fita dasu cewa ake kannin sa ne, dan sun kusa kafardar shi"

Wata rana jamal ya kwaso duk gidan domin zuwa gidan momy, akan hanyar ne hira ta barke tsakanin Jamal da yaran shi, inda yake tambayan so idan sun gama karatu me suke so su zama?

Hassan ne ya fara cewa nidai daddy SOJA zan yi"

Kai amman ka burgeni kaifa hussaini?

Tura kanshi yayi gaban motar inda Jamal da ma'u ke zaune yace.....

Nidai daddy so nake kawaai na auri Hussaina"

Gaba dayan su dariya sukayi ban da ma'u data zafgawa Hussaini harara"

Itama Fatima wadda suke kira shikuriya zuboro baki tayi tare da matso hawaye"

Bayan jamal ya gama dariya ya waiga ya kalli Hussaini yace amman ai saika gama karatu ka samu aiki zakai auren ko?

Kafin Hussaini ya bashi amsa yaga Shukuriyya na shirin kuka dan haka ya juya ya kalli ma'u yace....

Toh fah, ita kuma wannan rigimanmar waya bata mata rai, nakula duk dabi,unta naki ne"

Juyawa yayi ya sake kallon shukuriya yace gaya min wanene ya bata miki rai?

Cikin shagwaba tace ba hussaini bane yake cewa baxai aureni ba, wai Hussaina zai aura"

Murmushi Jamal yayi kadan sannan yace wace wacece Hussaina?, rabu dashi aina zai samu Husaina ?, karya yake yi"

Hassan ne yayi dariya tare da fadin dolowa kawai, yaya za, ayi ya aureki ?, mamarmu daya babamu daya ai ba'a aure, saidai ki Aure mashkur"

Azuciye ma'u ta waga ta daka musu tsawa tare da fadin wlh duk wadda ya kara mgnr aure cikin ku saina fasamai baki, waigawa Jamal yayi ya kalli ta ya dauke Kai domin ya lura kamar ranta bace yake"

Babu wadda ya sake mgn har suka isa gidan' bayan Jamal ya gaida mikewa yayi zaifita saitin kunnen ma'u yaje yace.....

My Sweet Heart idan nina bata miki rai kiyi hakuri, idan kuma yara ne ki musu uzuri yarinta ce ba wani abuba"

Yana gama fadan haka yajuya ya tafi"

Da daddare ya dawo ya dauke su suka koma gida"

Jamal na kwace agefen gadon ma'u yake tambayan ta wai dazun menene ya bata miki rai ne?

Cikin damuwa tace....

Yaya tsoro Hussaini ke bani bashi da zance saina aure kusan kulum sai yayi mgnr, sai naga kamar babu karatu agaban shi"

Murmushi yayi sannan yace......

Ki daina damun kanki Husna yarinta ce ke damun shi, babu abin da ya sani fada kawai yake"

Washari da safe daddy ya bugawa Jamal waya cewa nafisa ta haifi 'yan biyu duk mata"

Cikin fara'a Jamal ya fadawa ma'u, shiri tahau yi cikin tsan tsan farin ciki"

Tunda Hassan da hussaini sukaji suka kama murna tare da rukon suma zasu"

Lokacin da suka isa gidan cike suka samu falon ciki harda dadddy da momy, alhaji bashir da ummi, deeni har kuka yake saboda farin ciki, kasa amsa barkan da Jamal kemai yayi sai hawaye dake zuba a idon shi, bayan shi Jamal ke bugawa tare da fadin ba kuka yakamata kayiba ka godewa Allah"

Addu'io Jamal yayiwa Hassana da hussaina sanan ya mikawa ma'u"

Kwlla cike da idonta bakinta dauke da murmushi take kallon su"

Damunta yan biyu sukayi dan haka ta mikawa husaini Hasssana girza kai yayi tare da fadin momy Husaina zaki bani"

Hararan shi tayi sannan kowanne ya dauki takwaran sa"

Kinbawa kowa su sukayi, momy ce tace, nifah 'yan biyu ban gane bane, me kuke nufi?

Dariya ummi tayi tare da fadin kika sani ko yar gida za'ayi?

Dariya daddy yayi sannan yace kudai kuce kishi na damun ku"

Tun daga ranan ma'u ke zarya zuwa gidan har akai suna, kulum idan ma'u zata tafi sai 'yan biyu sunce ashafa musu kan jarirai"

Abba da kanshi ya kawo mama suna sannan yaita sawa yaran albarka dayaga deeni be iya shaidashi ba, saida daddy yagaya masa"

Ma'u nakai ziyara kano akai akai, inda lokaci bayan lokaci yaya usman yake kai mata fa'iza da dada"

Wata rana dada ta kawo mata ziyara da gangan tajata gidan nafisa, suna shiga tsakiyan harabar gida ma'u ta juya ta kalli dadda tace......

Dada kinsan Gidan wa na kawoki?

Saikin fada takwara"

Dariya ma'u tayi sannan tace gidan me kare"

Rawan jiki dada ta fara tare da fadin La haula fisha'atillahi azubika, Allahu akkubar Allah da kirma kake, fitsari ne ya fara zubowa ajikinta, banda dariya babu abinda ma'u keyi"

Daida kokacin deeni ya fito daga gida, ganin haka yasa ma'u ta tsaya da dariya tare da kama hannun Dada tana fadin zomuje"

Tirjewa dada take tana cigaba da surutun ta"

Deeni ne
ya matso yana fadin yaya akayi ne dada?

Yauwa bawan Allah zoka tai make ni, ka maida ni Kano ya riyar nan bata kyaunata so take taga bayana, zata kaini inda za'a akashe ni"

Ganin in da dada take arikece yasa ya kama hannun ta, motar shi ya bude ta shiga, ma'u dariya take tayi badan kar dada ta sumaba data kara cewa wani abu, cikin gidan ta shige"

Shiko deeni bayan sunyi nisa yaga jikin Dada ya daina rawa, anan ya fara tambayanta meya hadata da asma'u?

Warware mishi komai tayi, kwashewa yayi da dariya acikin zuciyan shi yace sai yashe asma'u zatai hankali ta daina tsokana, daman har yanzun tana nan da halinta?

Gidan daddy yakai dada sannan ya gaya musu abinda ke faruwa, dariya sosai daddy yayi sannan yace ai ga mekaran nan agaban Ki"

Mamaki ne ya kama dada daman Abba ya gaya mata deeni ya shirru Amman batasan takai haka va"

Hira sukaci gaba tsakanin deeni da dada daddy da Momy na souraran su"

Bayan shekara 10

Soyayya ce me karfi tsakanin Hassan da Hassana, Husaini da Hussaina, tun suna kana suka taso da kyaunar juna, duk da cewa su hassana basu wuce shekara 12 ba"

Jamal da deeni zumuci suke sosai har sun yake shawaran hada inbiyun su aure, da zaran ko wannen su ya kammala karatun shi"

Ma'u tun daga shikuriyya bata sake haihuwa ba, Jamal kara shagwabata ma'u yake idan ka gansu adaki bakace suna da yara 'yan shakara
20 da duriya ba"

ALHAMDULILLAH

Heat Beat
The End🙋🏻

*Mmn Yazeed*
Chapter 47 · 0% Book details