← Book details Zeenatu Complete Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 35

Sashe 4

Zeenatu Complete Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

********
duk dukan nan da tasha bai sa ta hak'ura ba, haka tai ta falfalar gudu ga k'afarta na Mata zafii dukan da bogaza Tai Mata ,sai da ta kamo su munay har sun kusa Zuwa gida ta cakumo munay, munay tace" me nai miki"? Ai" kema kin san me ki kai mun dariyar da kikai mun kin d'auka zata tafi a banza ne"? Haka ta gasawa munay rak'washi take suka hautsine  Aneeaa na rabasu lokacin 6 dai-dai dadyn Zee zai tafi masallaci ya ganota, dak'yar ya rabasu yace "yanzu zeena yauma fad'an naki kika tsaya"? ga maminki can na nemanki " ya kalli munay daketa gurshek'en kuka ya bata hak'uri ya tambayeta meya had'asu nan ta rattaba mai cikin Jimami ya kalle Zee "yanzu kan hakan kika yaga Mata hijab har Abada ke baki da hak'uri wace irin zuciya gareki ne ehe"? naira hamsin ya d'auko ya bawa munay yace  taje a d'inke Mata.
haka ya juya ya kalli Zee ya nuna Mata hanyar gida,haka ta tafi duk fuska a karce saboda fad'a ga Shi tana d'ingishi.

*By*
   *Queen meemi* .

.
[9:24pm, 01/11/2016] meemi basheer: . . *ZEENATU by Queen meemi page 9*

♠.          ♠.          ♠.           ♠.            ♠.           ♠
♠.               ♠.            ♠
             *®NWA*
*dedicated to Lubie nd bena*
           *[17sep2016]*

Haka taje gida tana d'ingishi mum dake kitchen tana kwashe tuwo ta ganta tace" Aa Zee meya faru da k'afar ne"?sukwi dakai tai bata ce komi ta shiga d'aki mum ta girgiza kai tabbas tasan fad'an nata ta janyo ,fitowa Tai ta d'ebo ruwa a buta ta fara Alwala dede zuba ruwan da Tai a fuska ta k'wala k'ara mum ta fito " ke mene" ?ganin fuskarta duk akarce yasa mum ta sa dariya "ai maganinta kema. Ayi mutum bai da Aiki se fushi da fada tunda Naga fuskarki nasan kinyi fad'a,da k'yer Tai Alwalar taje Tai sallah .

*8 :pm*
******
duk suna zaune Ana ta kallo Zee ta had'e rai sai k'wafa take,tsam ta tashi ta ta shiga d'aki ta d'au qur'aninta tana hadda "mum wai me akaiwa Zee ne"? cewar sadiq mum tace" kasan Halin yayar taka kutsuwa ce" haka suka kwanta ba wanda ta cewa k'ala.

*7:am*
da safe kuwa kowa ya tashi Zee ta kasa tashi.
Sai da mum ta shiga d'akin ta tadda ta  tana kuka sosai "wayyo mum k'afata na kasa tashi" taci gaba da kuka "muga kafar " mum ta d'aga k'afar taga ta kumbura daga gefe "Ashsha! garin yaya haka Zee"? sadiq dake k'ok'arin shiga d'akin yace "mum inaga fad'an da sukai  ne da ita da wasu kawayenta ,domin Naga suna ta dambe Allah mum Dan bakiga wadda suke fad'an da itaba gandamemiya ".
dariya mum tasa ah" da walakin ai dama tin jiya na gano
    Ai ga Shi nan Wata abanza ta jibgeki ke zeena ki Dena neman fad'a ayi mutum baya yafiya wallhi ke zaki sha wahala banza ahofi " zumb'ura baki Tai "mum dariya fa suke mun "
    d'aga ta mum tayi k'ara ta saki sadiq sai dariya yake "Allah mum inna warke sai sadiq ya sani ".
   Mum tace " Allah de ya Sawwak'e miki Zee ".
   Da k'yar ta tashi ta kaita falo ta ebo ruwan zafi tana gasa Mata ,lokacin dadyn su ya fito zai kai su sadiq da sadeey da faty school nan ya tambayi meya faru,take mum taga ya mai.
  Dady yace"Ai jiya nan nan na ganota suna fad'a da yaran gidan Alhaji tanko wai sun Mata dariya don takasa hadda"
   Mum tace "Ah to Wanda baiji bari ba ai yaji hoho ai gashi nan jikinta ya gaya Mata".
  Dady ya fita yace zai dawo da mai gyaran targad'e don da Alama Tai targad'e haka Tai sallah a zaune .
  Wajen 12 Dady ya dawo da mai gyaran targad'e kama k'afarta yai ya duba nan ya fara gyarawa tun tana matsae -matse har ta fara ihu mum na rik'eta kuka sosai take.
     Bayan ya gama ya bada magani asha fa agun haka ta zauna tana jinya .
   Da yamma Dady ya kawo Mata hanta gasashshiya da milk nan Zee ta hau murna haka Tai taiwa su sadiq dangwaliliya .

*7pm*
********
su munay da Aneesa suka zo dubiya Zee sai harare-Harare take Aneesa ta fito da Iv ta mik'awa Zee "gashi na bikin Anty ramla ne ranar Sunday" dariya tasa don Zee akwai son zuwa biki ko ba a gayyace ta ba.
  Munay tace" to idan lokacin baki warke ba fa"?
   "To 'yar bak'in ciki wlh ko ban warke ba senaje shine first fa da aka fara gayyatana biki"
   Shiru sukai san nan suka tafi ,haka Zee Tai ta jinyar fuskrta da k'afarta har Ana I gobe bikin gidan su Aneesa Fes Zee ta mik'e ko Dan washe gari taje biki.....

*© Queen meemi*
[9:24pm, 01/11/2016] meemi basheer: . *ZEENATU by Queen meemi page10*

♠.             ♠.           ♠.       ♠.              ♠.            ♠
♠.                ♠.              ♠
               *®NWA*
*dedicated to Lubie & bena*
     *[18 Sep,2016]*

Tun sassafe Zee ke duba kalar Kayan da zata sa ko wanne se taje ta duba mirrow ta ga yanayin zamansa a k'alla ta d'auki kaya sun kai kala 5 duk basi Mata ba se ak'arshe ta gano wani kayan ta da Anty bara ta d'in koma Mata Harda mayafinsa ta aje gefe har wani yanga take .

Haka taje ta duba takalman ta ta gano wani me d'an uban tsini Wanda sanda sukaje kano aka sai Mata ,Shi ma ta d'auko ta aje a gefe.
   Mum dake shiga d'akin "oh su Zee gargaji ga ke tun yanzu kike had'a kayan zuwan bikin sekace Wata shaharriyar budurwa " dariya tasa mum" wallahi kwalliya zanci don har powder da lips stick zan sa"                   "haka ai akeso ki nutsu saura kuma kije ki neman fad'an agun biki"
   "Mum ai bazanba "
Bud'e kanta Tai tagan shi a cunkushe nan mum Ta taje Mata tasa ribborm .
  Saboda dad'in za ta biki sai Aiki take yau har dasu wak'e -wak'e lokaci kad'an -kad'an sai ta kalli agogo haka da rana kowa ya kwanta bacci da yake weekend ne amma Banda Zee ta kafawa agogo Ido.

*3:pm*
*******
Zumbur Zee ta mik'e ta shiga wanka so biyu tana sab'a sabulu da gudu ta fito ta shige d'akinsu ta tsane jiki ta mulka mai Abu kad'an sai ta kalli agogo haka ta zira kayan dai-dai sun Mata kyau adai-dai shekarunta d'akin mum ta shiga lokacin tana kan sallaya "mum ki mun kwalliya na kasa kin san ni ban iya ba "
   "To dama wane kwalliya za ki iya aise fad'a" dariya Tai" kai mum ai na Dena "
   To Allah yasa my Zee haka mum ta zizarawa Zee kwalliya tasa Mata kwalli sosai a idon da yake masha Allah Tana da wadatattun idanuwa dara-dara tasa Mata lipstick ta taje Mata gira da yake irin girar nan ce da ita cunkus me yawa bak'a Sega zeee d'au skin inta me kalar choculate ta haskaka.
    Haka ta feshe ta ta perfume sai ga zee Tamkar flower Tai kyau sai kallon mirrow take tana murmushi "mum dama Nima ina da kyau".?
  "Sosaima Zee ai sema kin Dena fad'a kyanki zai dad'a fitowa"  Tsalle ta daka "ai mum na kusa Daina wa" dariya mum Tai to Allah yasa".
    Agogo ta kalla taga 4:15 da gudu ta fita ta sako takalmin ta da wani mayafi shima dai-dai shekarun ta tsayawa Tai "mum na tafi "
   "Zee kar naji kar na gani ".

************
Ahankali Zee ke tafiya don kar ta fad'I har yanga ake dosar gidan su Anee Tai taga motoci birjik K'ara sauri Tai jikin ta na rawa .wasu manyan 'yan Mata ne atsaye ganin yanda Zee ke tafiya yasa suka sa laugh Wata tace " ga yarinyar can se yanga take kuma masha Allah me kyau da ita, harara Zee ta buga musu dai -dai,shiga gidan taga munay.nan suka tsaya .

Zee tace" wai  a ina za ai ne "?munay tace" a wani big house za ai  kusa da gidan Antyn su Anee ke kings gidan tab ya had'u "Zee ta yatsine fuska "to,mu a ina zamu "? munay tace" bakya ganin motoci ai aciki zamu shiga".
   Ganin an fara shiga su zeee suka doshi Wata dalleliyar mota garin sauri Zee ta buge wani bata Sani ba  jiyawa Tai sukai Ido Hud'u da wani matashin saurayi da sauri  Ta k'arasa suka bud'e motar zasu shiga manyan 'yan Matan nan suka tsai dasu.
    "Ku yaran nan ina zaku shiga? kuje ga bus can nan yara ke shiga" zeee ta tab'e baki tace to" dame kuka fimu "Wata tace zan mauje ki kina kwaila kina cusa kai".
"Zee tace malama duk girmanki ba tsoronki zanji ba ta far-fara idon ta
  Dariya suka sa Zee taja hannun munay suka doshi Wata mota waddama tafi d'ayar kyau bud'ewa  sukai suka zaman su .......ku dakace ni plsss.

*©Queen meemi**
[9:24pm, 01/11/2016] meemi basheer: . . . . . . *ZEENATU by Queen meemi page11*

♠.          ♠.          ♠.          ♠.           ♠.             ♠
♠.               ♠.             ♠
               *®NWA*
*dedicated to bena &Lubie*
  *[18sep 2016]*

Zaman su keda wuya suka hau magana zaune yake a driver sit yana kallonsu ta mudubi sai murmushi yake yana kallon Zee dake juya idanuwa wai ala dole Tai kyau ,haka kawai tun sa'ilin da ya ganta yake son kallon ta.
Chapter 4 · 0% Book details