Sashe 9
Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel · about 8 min read
ya na kara nufo motar sautin kukan na karuwa
A hankali ya fara zagayen motar har ya iso inda ta ke
Ta na zaune ta cusa kan ta tsakanin cinyoyin ta sai kuka ta ke kamar ba gobe
A hankali ya tako ya zo geffen ta ya zauna shi ma sannan ya kai hannu ya dafa kafadar ta , Moussa kuma ya na tsaye gaban su
A hankali ta dago kan ta cikin kukan nata fuskar ta duk ta yi jaga'jaga da hawaye
Ta na daura ido saman shi ta ji wani kukan ya zo mata
Da hannu ya mata allamun " minene ki na kuka ? "
TO A NAN ZAN DASSA AYA SAI MUN HADU GOBE✌✌✌✌
KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN ANISH ❤
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 6 ❤🔥
Da hannu ya mata allamun " minene ki na kuka haka ? "
Cikin wata disashashiyar murya ta ce " yaya Zayd wai Abba ya yi min aure "
Da sauri Moussa ya ce " to mine matsalar ba ki na son wadan a ka aura miki ba "
Medo da kallon ta ta yi kan Moussa cikin kukan ta ce " yaya Moussa ni fa ina da wanda na ke so , kuma ni ban ma san wanda Abba ya aura min , ni ko ma wanene ba na son shi , dan Allah yaya Moussa ka je ka same shi ka ce ya raba auren nan wlh ba ni son shi " ta kai karshen ta na meda kan tsakanin cinyoyin ta
Dan satar kallon Zayd ya yi kafin ya ce " shikenan babyn malam , yanzu fada min wa ne wannan wanda ki ke so "
Da sauri ta dago kai ta ce " yaya z........." kut maganar ta yanke ta zaro idanu ta na kallon Moussa
Shi dai Zayd ya na zaune ya zuba mata ido ya na jiran ya ji sauran maganar in da gaske akwai wanda su ke soyayya to ya dauki niyar zai sake ta ya aura mata wanda ta ke so
Ganin ta yi shiru ta tsaya sai kallon Moussa ta ke sai ya kai dan yatsun shi saitin face din ta ya kyasta mata
Sai da ta dan razane sannan ta medo da kallon ta kan shi
Tambayar ta ya yi minene
Girgiza mishi kawai sannan ta meda shi tsakanin cinyoyin ta amma ba kuka ta ke ba wannan karan
Kallon Moussa ya yi sannan ya daga mishi gera guda
Jinjina mishi kai Moussa ya yi sannan ya sunkuyo gaban ta ya ce " shikenan yanzu tashi mu koma gida ko "
Ba tare da ta dago kai ba ta ce " ni wlh ba inda zan je "
Ya na shirin magana Zayd ya daga mishi hannu ya na girgiza mishi kai
Mikewa tsaye moussa ya yi ya dan ja baya kadan
Shi ma Zayd mike wa tsaye ya yi sannan ya fara takawa ya bar gidan
Ta na jin ya fara takawa ta dago kai a hankali ta na kallon shi ta wutsiyar ido
Sai da ta ga ya fita gidan sannan ta sake sakin wani sabon kukan
Juyawa Moussa ya yi zai bar wajen sai ya dawo ya ce mata " tashi ki shiga cikin gidan tun da baza ki koma gida ba "
Ya na gama fadar haka ya sa kai ya fice shi ma
Cen ya hango Zayd har ya yi nisa da tafiyar shi
Da sauri ya fara takawa har ya kamo shi dai'dai ya karaso kofar gidan su Inaya
Su na karasowa wajen Abdoul da malam su ka fito da sauri kamar sun ga wani abun gudu
Da sauri Moussa ya ce " Abdoul ina za ku je haka da sauri wani abu ya faru "
Abdoul na shirin magana malam ya riga shi cewa " Inaya ce ba ta cikin gidan nan ban San inda ta yi ba "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " ku kontar da hankalin ku , yanzu nan mu ka baro ta gidan mu, kar ku damu ba abun da ya same ta "
Ajiyar zuciya malam da Abdoul su ka sauke a tare
" uncle kun san da yarinyar nan ta na da wanda ta ke so " su ka tsinci Muryar Zayd ya na fada
Kallon juna Abdoul da malam su ka yi kafin su kali Zayd har su na hada baki wajen cewa " ita da kanta ta fada maka hakan ? "
Jinjina musu kai ya yi bai ce komai ba
Dan murmushi malam ya yi sannan ya ce " yo ai wannan ba matsala ba ce dan..... "
Da sauri Zayd ya katse shi da cewa " no uncle tun da ta na da wanda ta ke ni zan nemo shi in aura mata shi da kai na , baza ta ji dadin zama da mutuman da ba ta so , a karancin shekarun nan na ta bai kama ta ta shiga cikin kunci ba , dama ni ta yi min karama sosai " bai jira amsar malam ba ya juya ya bar wajen
Sai da ya bar wajen sannan malam ya kali Moussa ya ce " wai maganar me ya ke yi ne haka ? "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " wai zai saki babyn malam tun da ta ce ta na da wanda ta ke so , ku kyale shi yayi ta neman kan shi , zan koma gida sai da safe " ya juya ya bar wajen
Da sauri Abdoul ya yi shirin bin bayan shi, amma malam ya riko hannun shi ya ce " nassan auta ce za ka je daukowa kyale ta, sa safe sai mu je a tare "
Jinjina mishi kai Abdoul ya yi sannan ya juya ya koma cikin gidan malam ya bi bayan shi
Da sallama su ka shigo cikin gidan
Da sauri Nesrine da ke konce ta tada kai da cinyar mama ta na kuka, ta tasso ta tarbo malam cikin kukan ta ke cewa " Abba ina Inaya ta yi ne "
Dan murmushi yayi kafin ya ce " kontar da hankalin ki, ta na gidan mijin ta "
Dan zaro idanu ta yi ta na maimaita kalmar miji cikin ranta
Ta geffen ta malam ya raba ya wuce ya karaso inda mama ke zaune shi ma ya zauna
Shi kuma Abdoul ya wuce bedroom din shi
Ya na zama Nesrine ta juyo da sauri ta nufo malam ta zo gaban shi ta tsaya ta ce " Abba wane mijin kuma, Abba Inaya fa shekarun ta 15 ina ta kai aure ko period ba ta fara ba " duk cikin kukan ta ke mishi wannan maganar ta ma manta da mahaifin ta ta ke magana
Malam na shirin magana mama ta riga shi cewa " yanzu dan Allah malam ina Inaya ta isa aure me ma ta sani a kai , ka hada ta da wanda ba mu san shi ba , wanda ba son shi ta ke ba yanzu in ya je ya cutar mana da ita da wane za muji malam bibiyar da ake mana ko wannan " ta kai karshen ta na sakin kuka
Da sauri Nesrine ta karaso wajen ta ta Zube saman guyiwowin ta ta rungume mama ita ma ta na sakin kuka
" yanzu Amina ya ki ke son na yi kin fi son na saka ido wancen yaron ya gano inda muke ya zo ya dauke mana ita, kuma na fada miki auren ya yi wajen shekara biyu yanzu , kuma ta na son mijin na ta dan ni da kai na na tambaye ta in ta na son shi , ku yanzu a tunanin ku in Sudais ya gano inda muke ba sai ta fi shiga cikin matsa la ba dan Allah ku kontar da hankalin ba abun da zai faru da ita " ya kai karshen ya na kai hannun shi saman kafadar mama
A hankali mama ta dago da ga jikin Nesrine ta kali malam ta ce " shikenan na ji abun ka fada amma ba ka fada min wanene wanda ka aura mata "
Jinjina kan shi ya yi kadan sannan ya ce " ba kowa ba ne face Zayd "
A dubu dari Nesrine ta mike tsaye ta na fadin " Zayd ???? " da karfi ta na zaro idanu, yanzu mutumin da ko hanya ba ta fatan ta hada su wai shi ne mijin kanwar ta, mutumin da ko gani ba ya yi kamm akwai ta
" e Zayd , wanda ke zowa gidan nan wanda ku ke ma kallon makaho da kurma shi din dai " malam ya fada ya na kallon ta
Cikin bacin rai mama ta ce " haba malam, wannan makaho ta ya zai iya kare mana yarinyar mu , ko shi ta kan shi ya ke , ya zai kula da ita, inda ma abokin shi Moussa ne da sauki amma Zayd ? "
Mikewa tsaye malam ya yi cikin bacin rai ya ce " bara ku ji aure dai an riga da an aura ku ba bazai sake ta ba in kun ga dama ku karbe shi in kun ki ku ta matsewa "
Ya na gama fadar haka ya kama hanyar dakin shi ya shige ya bar su nan tsaye
Juya wa ita ma Nesrine ta yi ta koma dakin ta da gudu ta na sakin sabon kuka
Ita ma mama ta juya ta koma dakin ta zuciya ba dadi
Duk abun da su ke Abdoul na jin su amma ya yi banza da su ya yi konciyar shi
Zayd
Bayan ya koma gida kai tsaye bedroom din shi ya wuce, ga Dukan allamu ya manta da Inaya da ke cikin gidan
Shi ma Moussa ya na shigo wa ya wuce kai tsaye cikin falo
A tunanin shi ta na nan amma da ya shigo ya ga ba kowa a cikin falon
Da sauri ya juya ya fita falon ya koma wajen da su ka baro ta
A hankali ya fara zagayen motar har ya iso inda ta ke
Ta na zaune ta cusa kan ta tsakanin cinyoyin ta sai kuka ta ke kamar ba gobe
A hankali ya tako ya zo geffen ta ya zauna shi ma sannan ya kai hannu ya dafa kafadar ta , Moussa kuma ya na tsaye gaban su
A hankali ta dago kan ta cikin kukan nata fuskar ta duk ta yi jaga'jaga da hawaye
Ta na daura ido saman shi ta ji wani kukan ya zo mata
Da hannu ya mata allamun " minene ki na kuka ? "
TO A NAN ZAN DASSA AYA SAI MUN HADU GOBE✌✌✌✌
KAR KU MANTA KU NA TARE DA ALKALAMIN ANISH ❤
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 6 ❤🔥
Da hannu ya mata allamun " minene ki na kuka haka ? "
Cikin wata disashashiyar murya ta ce " yaya Zayd wai Abba ya yi min aure "
Da sauri Moussa ya ce " to mine matsalar ba ki na son wadan a ka aura miki ba "
Medo da kallon ta ta yi kan Moussa cikin kukan ta ce " yaya Moussa ni fa ina da wanda na ke so , kuma ni ban ma san wanda Abba ya aura min , ni ko ma wanene ba na son shi , dan Allah yaya Moussa ka je ka same shi ka ce ya raba auren nan wlh ba ni son shi " ta kai karshen ta na meda kan tsakanin cinyoyin ta
Dan satar kallon Zayd ya yi kafin ya ce " shikenan babyn malam , yanzu fada min wa ne wannan wanda ki ke so "
Da sauri ta dago kai ta ce " yaya z........." kut maganar ta yanke ta zaro idanu ta na kallon Moussa
Shi dai Zayd ya na zaune ya zuba mata ido ya na jiran ya ji sauran maganar in da gaske akwai wanda su ke soyayya to ya dauki niyar zai sake ta ya aura mata wanda ta ke so
Ganin ta yi shiru ta tsaya sai kallon Moussa ta ke sai ya kai dan yatsun shi saitin face din ta ya kyasta mata
Sai da ta dan razane sannan ta medo da kallon ta kan shi
Tambayar ta ya yi minene
Girgiza mishi kawai sannan ta meda shi tsakanin cinyoyin ta amma ba kuka ta ke ba wannan karan
Kallon Moussa ya yi sannan ya daga mishi gera guda
Jinjina mishi kai Moussa ya yi sannan ya sunkuyo gaban ta ya ce " shikenan yanzu tashi mu koma gida ko "
Ba tare da ta dago kai ba ta ce " ni wlh ba inda zan je "
Ya na shirin magana Zayd ya daga mishi hannu ya na girgiza mishi kai
Mikewa tsaye moussa ya yi ya dan ja baya kadan
Shi ma Zayd mike wa tsaye ya yi sannan ya fara takawa ya bar gidan
Ta na jin ya fara takawa ta dago kai a hankali ta na kallon shi ta wutsiyar ido
Sai da ta ga ya fita gidan sannan ta sake sakin wani sabon kukan
Juyawa Moussa ya yi zai bar wajen sai ya dawo ya ce mata " tashi ki shiga cikin gidan tun da baza ki koma gida ba "
Ya na gama fadar haka ya sa kai ya fice shi ma
Cen ya hango Zayd har ya yi nisa da tafiyar shi
Da sauri ya fara takawa har ya kamo shi dai'dai ya karaso kofar gidan su Inaya
Su na karasowa wajen Abdoul da malam su ka fito da sauri kamar sun ga wani abun gudu
Da sauri Moussa ya ce " Abdoul ina za ku je haka da sauri wani abu ya faru "
Abdoul na shirin magana malam ya riga shi cewa " Inaya ce ba ta cikin gidan nan ban San inda ta yi ba "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " ku kontar da hankalin ku , yanzu nan mu ka baro ta gidan mu, kar ku damu ba abun da ya same ta "
Ajiyar zuciya malam da Abdoul su ka sauke a tare
" uncle kun san da yarinyar nan ta na da wanda ta ke so " su ka tsinci Muryar Zayd ya na fada
Kallon juna Abdoul da malam su ka yi kafin su kali Zayd har su na hada baki wajen cewa " ita da kanta ta fada maka hakan ? "
Jinjina musu kai ya yi bai ce komai ba
Dan murmushi malam ya yi sannan ya ce " yo ai wannan ba matsala ba ce dan..... "
Da sauri Zayd ya katse shi da cewa " no uncle tun da ta na da wanda ta ke ni zan nemo shi in aura mata shi da kai na , baza ta ji dadin zama da mutuman da ba ta so , a karancin shekarun nan na ta bai kama ta ta shiga cikin kunci ba , dama ni ta yi min karama sosai " bai jira amsar malam ba ya juya ya bar wajen
Sai da ya bar wajen sannan malam ya kali Moussa ya ce " wai maganar me ya ke yi ne haka ? "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " wai zai saki babyn malam tun da ta ce ta na da wanda ta ke so , ku kyale shi yayi ta neman kan shi , zan koma gida sai da safe " ya juya ya bar wajen
Da sauri Abdoul ya yi shirin bin bayan shi, amma malam ya riko hannun shi ya ce " nassan auta ce za ka je daukowa kyale ta, sa safe sai mu je a tare "
Jinjina mishi kai Abdoul ya yi sannan ya juya ya koma cikin gidan malam ya bi bayan shi
Da sallama su ka shigo cikin gidan
Da sauri Nesrine da ke konce ta tada kai da cinyar mama ta na kuka, ta tasso ta tarbo malam cikin kukan ta ke cewa " Abba ina Inaya ta yi ne "
Dan murmushi yayi kafin ya ce " kontar da hankalin ki, ta na gidan mijin ta "
Dan zaro idanu ta yi ta na maimaita kalmar miji cikin ranta
Ta geffen ta malam ya raba ya wuce ya karaso inda mama ke zaune shi ma ya zauna
Shi kuma Abdoul ya wuce bedroom din shi
Ya na zama Nesrine ta juyo da sauri ta nufo malam ta zo gaban shi ta tsaya ta ce " Abba wane mijin kuma, Abba Inaya fa shekarun ta 15 ina ta kai aure ko period ba ta fara ba " duk cikin kukan ta ke mishi wannan maganar ta ma manta da mahaifin ta ta ke magana
Malam na shirin magana mama ta riga shi cewa " yanzu dan Allah malam ina Inaya ta isa aure me ma ta sani a kai , ka hada ta da wanda ba mu san shi ba , wanda ba son shi ta ke ba yanzu in ya je ya cutar mana da ita da wane za muji malam bibiyar da ake mana ko wannan " ta kai karshen ta na sakin kuka
Da sauri Nesrine ta karaso wajen ta ta Zube saman guyiwowin ta ta rungume mama ita ma ta na sakin kuka
" yanzu Amina ya ki ke son na yi kin fi son na saka ido wancen yaron ya gano inda muke ya zo ya dauke mana ita, kuma na fada miki auren ya yi wajen shekara biyu yanzu , kuma ta na son mijin na ta dan ni da kai na na tambaye ta in ta na son shi , ku yanzu a tunanin ku in Sudais ya gano inda muke ba sai ta fi shiga cikin matsa la ba dan Allah ku kontar da hankalin ba abun da zai faru da ita " ya kai karshen ya na kai hannun shi saman kafadar mama
A hankali mama ta dago da ga jikin Nesrine ta kali malam ta ce " shikenan na ji abun ka fada amma ba ka fada min wanene wanda ka aura mata "
Jinjina kan shi ya yi kadan sannan ya ce " ba kowa ba ne face Zayd "
A dubu dari Nesrine ta mike tsaye ta na fadin " Zayd ???? " da karfi ta na zaro idanu, yanzu mutumin da ko hanya ba ta fatan ta hada su wai shi ne mijin kanwar ta, mutumin da ko gani ba ya yi kamm akwai ta
" e Zayd , wanda ke zowa gidan nan wanda ku ke ma kallon makaho da kurma shi din dai " malam ya fada ya na kallon ta
Cikin bacin rai mama ta ce " haba malam, wannan makaho ta ya zai iya kare mana yarinyar mu , ko shi ta kan shi ya ke , ya zai kula da ita, inda ma abokin shi Moussa ne da sauki amma Zayd ? "
Mikewa tsaye malam ya yi cikin bacin rai ya ce " bara ku ji aure dai an riga da an aura ku ba bazai sake ta ba in kun ga dama ku karbe shi in kun ki ku ta matsewa "
Ya na gama fadar haka ya kama hanyar dakin shi ya shige ya bar su nan tsaye
Juya wa ita ma Nesrine ta yi ta koma dakin ta da gudu ta na sakin sabon kuka
Ita ma mama ta juya ta koma dakin ta zuciya ba dadi
Duk abun da su ke Abdoul na jin su amma ya yi banza da su ya yi konciyar shi
Zayd
Bayan ya koma gida kai tsaye bedroom din shi ya wuce, ga Dukan allamu ya manta da Inaya da ke cikin gidan
Shi ma Moussa ya na shigo wa ya wuce kai tsaye cikin falo
A tunanin shi ta na nan amma da ya shigo ya ga ba kowa a cikin falon
Da sauri ya juya ya fita falon ya koma wajen da su ka baro ta