← Book details Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 44

Sashe 8

Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jim kadan ta fito rike da wani dan basket a hannun ta, ta fita gidan, a lokacin har malam ya shiga dakin shi

A hankali ta ke tafiya saman hanya ta na kallon kassa kamar mai tunanin wani abu

Sai da ta karaso kofar gidan sannan ta dago kai, ta kai hannu ta tura kofar ta shiga ta na sallama

Wannan karan farko da ta shigo gidan shi ,
Ta sha ruwan mamaki ganin yanayin gidan, har da wata mota fara ta tambayi kanta ta ina motar ta shigo , in ta shigo ai fitar ba za ta yi wuya ba kuma ita kofa daya ta gani kuma karama ce

A hankali ta ci gaba da takawa har ta isa terrace din gaban ta

Ta kai hannu ta bubuga kofar, sau daya
Shiru ba a bude ba sai ta sake bugawa karo na biyu

Wannan karan bai fi one minute ba ta ga kofar ta bude
Sai ga Moussa ya na tsaye rike da kofar ya na sanye da wando three cuter da t-shirt ya na shan iska

Sallama ta yi mishi ta gaishe da shi cikin fara'a sannan ta mika mishi basket din hannun ta ta ce ga abincin su in ji malam

Dan murmushi yayi kafin ya dan ja gefe kadan ya ce " bismillah shigo mana dama yunwa na ke ji idan mun ida sai ki koma da basket din ko "

Jinjina mishi kai ta yi ta na murmushi kafin ta sa kafa ta shiga falon ta na sallama

Ya na zaune saman sofa da ke fuskantar kofar shigowa, ya na sanye da jallabiya fara mai kananan hannu, ya na sanye da wadanan glass din na shi baki, ya jinjina a bayan sofar ya daga kai sama ya lumshe idanu duk da su na cikin glass

Ya ji sallamar ta amma ko motsi bai yi bare ya amsa mata

A hankali ta karaso cikin falon ta na bin shi da kallo gaskia ya yi mata kyau

Ta na cikin dube duben ta ta tsinci Muryar moussa ya na fadin " ko kin dawo nan da zama "

Girgiza mishi kai ta yi ta na murmushi sannan ta karasa ta ajiye basket din hannun ta saman table ta ce " ina wuni yaya Zayd "

Shiru bai amsa mata ba ko motsi bai yi ba

Da sauri Moussa ya ce " barci ya ke " dan ya kare dan uwan shi

Murmushi ta yi sannan ta koma bakin sofar da ke wajen kofar shigowa ta zauna kassa saman carpet

Karasowa Moussa ya yi ya zauna saman sofar da Zayd ke zaune, ya kai hannu ya janyo table din gaban shi ya kai hannu ya ciro kwanonin da ke ciki da plate guda ya fara serving din kan shi ya fara ci ya na yi mata hira ta na amsa mishi a kai a kai

Duk abun da su ke Zayd na sauraron su dan ba barci ya ke ba kawai dai ya lumshe idanun shi

Sai da ya Kamala cin abincin tass ya cinye komai sannan ya meda kayan cikin basket ya tashi ya je dining room ya bude fridge ya dauko gorar ruwa guda sannan ya dawo inda ya tashi ya zauna ya bude ya sha ruwan

Sai da ya ida sannan ya koma ya jingina a bayan sofar ya lumshe idanun ya bude a hankali ya kali Inaya ya ce " Gaskia abincin nan ya yi dadi "

Shiru ta yi ta kurewa waje guda ido babu ko kiftawa

" Inaya tunanin mi ki ke " ya tambayeta ya na kallon ta

Nan ma shiru ba ta motsa ba

Tasowa ya yi da ga jikin sofar ya kai hannu ya dan bubuga cinyar Zayd

A hankali ya ware idanun shi ya taso da jikin sofar shi ma ya kali Moussa

" duba ka ga, ko tunani me ta ke ? " Moussa ya fada ya na nuna mishi Inaya

A hankali ya juyo kan shi ya kale ta

Ta yi zugum waje guda kamar wadda ta suma

Mikewa tsaye ya yi ya koma saman sofar da ke bayan ta ya zauna ya kai hannun shi ya dafa kafadar ta

A razane ta dawo cikin hayacin ta , ta na sakin kara ta kai hannayan ta ta toshe kunnuwan ta ta na fadin " Ku kyale ni , ku kyale , kar ku tabani , wayo Abba na, aaaaaaaaaaaa "

A rude ya sauko kassa ya riko ta da hannayan shi biyu, shi ma Moussa da sauri ya tasso ya koma gaban ta ya tsuguna ya na fadin " Inaya lafya me ya faru "

Ina sam ba ta jin shi ta toshe kunnuwan ta

Da karfi Zayd ya sa hannayan shi duka biyu ya riko nata ya yanye su da karfi ya sauke su kassa ya kali Moussa

Jinjina kan shi Moussa ya yi sannan ya karanto ayatul kursi'u dan a tunanin shi aljanu ne gare ta

Kamar da gaske ya na fara karanta, ta fara nitsuwa ta na kallon shi ta na sauke ajiyar zuciya a hankali ta lumshe idanun ta ta fada jikin Zayd

Sai da ya karanta ajatul kursi sau biyar sannan ya bari ya kali Zayd ya ce " Amir ba dai aljanu ne da ita ba ? "

Girgiza mishi kai Zayd ya yi ba tare da ya ce komai ba ya na rungume da ita
Ya na jin ta sauke ajiyar zuciya ta ke a jere idanu a lumshe

Sai da ta ji ta nitsu sannan ta bude idanun ta, ta mike da ga jikin Zayd ta na kallon Moussa

Dan murmushi ta saki kafin ta mike tsaye ta ce " yaya Moussa zan koma gida "

" shikenan muje na raka ki " ya fada ya na mikewa tsaye ya dauki basket din saman table ya riko hannun ta ya ce mu tafi

Ba musu ta bi bayan shi su ka bar falon

Shi ma Zayd mike wa ya yi ya bi bayan su a hankali dan nesa kadan da su

Sai da su ka iso bakin kofar gidan sannan ya saki hannun ta ya mika mata basket din ta ya ce ta shiga

Karbar basket din ta yi sannan ta ce mishi sai an jima ta shige gidan su

Har ya juya zai bar wajen
Cak ya tsaya ya na kallon Zayd da ke tsaye bayan shi cike da mamaki " yaushe ya biyo mu kuma ? " ya tambayi kanshi

Ya na shirin magana ya riga shi cewa " shiga ka yi min magana da uncle "

Ba musu ya juya ya shiga gidan ya na sallama shi kuma ya tsaya nan ya na jiran su

Jim kadan Moussa ya fito , malam na bayan shi

Sallama malam ya yi mishi sannan ya bashi su ka yi musbaha

Sai da su ka gaisa sannan Zayd ya ce " Uncle ina son muyi wata magana "

" ina sauraron ka, mi ka ke son muyi magana a kai ? " Malam ya fada ya na tsare shi da ido

Ajiyar zuciya Zayd ya yi kafin ya ce " uncle ina son in san dalilin da ka aura min yarinyar nan "

Nan take yanayin face din malam ta sauya ya rasa amsar da zai ba shi
Ga kuma Zayd ya tsare shi da ido

Wasu yawu malam ya hadiye kafin ya ce " Zayd ba zan iya fada maka ba a yanzu ka gane lokacin in ya yi za ka gane komai "

" shikenan next week zan zo na dauki matata zan gano abun da ake boye min da kai na " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen ya na taku cike da izza
(TO FA NA MULKIN SUN FARA TASHI 🤣🥀 )

Ba karamin kwarjini ya yi ma malam ba kawai ya tsaya ya na kallon shi ya rasa me zai ce

Kallon shi Moussa ya yi sannan ya ce mishi " malam zan tafi " sannan ya juya ya fara takawa

Jinjina kan shi malam ya yi sannan ya fara takawa dama ya fito zai je mosque ya ji sallamar Moussa

Bayan sallar isha

Inaya

A hankali ta ke fitowa da ke fitowa da ga cikin dakin su
Ta na sanye da gown pink colour mara nauyi da hijab pink shi ma zuwa guyiwa

A hankali ta ke takowa cike da nitsuwa ta ke takowa ta nufi kitchen
Har ta kai kofar kitchen ta jiyo mama na magana sama sama

A hankali ta juyo ta nufi kofar dakin mama dan a tunanin ta ita ka dai ce ko da ita ta ke magana ba ta ji da kyau ba

Har kai kofar dakin ta bude baki za ta yi sallama ta ji Muryar malam ya na fadin " abun da ki ka ji Amina, auta dai na aurar da ita tun shekara biyu da su ka wuce kuma yanzu mijin ta ya ce ya na son ta koma gidan shi "

Dumm ta ji gaban ya buga da karfi nan take idanun ta su ka kawo ruwa da gudu ta juya ta bar wajen

Maimakon ta koma bedroom din su , sai ta bar gidan baki daya

Gudu ta ke da iya karfin ido a rufe
Da karfi ta bangaje kofar gidan shi ta shiga ta nufi wajen motar da ke cikin gidan ta buya a baya ta Zube saman guyiwowin ta ta aza kuka da karfi

Ba ta fi ten minutes da shigowar ta wajen Moussa da Zayd su ka fito da ga cikin falon
Su na sanye da jeans baki da t-shirt amma ta Zayd fara ce ta Moussa kuma blue

Su na tsaka da tafiyar su su ka jiyo kukan mutun
Cak su ka tsaya a tare su na kallon juna su na zaro idanu

A hankali su ka fara bin wajen da kallo ba su ga kowa ba
Cen Moussa ya ce " ko dai aljanu ne ke wannan kukan ? "

Girgiza mishi kai Zayd ya yi kafin ya fara takawa a hankali ya nufi motar shi
( WATA SABUA MAKAHO DA TUKA MOTA 🤣✌)
Chapter 8 · 0% Book details