← Book details Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 44

Sashe 2

Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri sauri ta cire hijabin jikin ta ta cire uniform din ta ta daura wata towel fara sannan ta saka hijabin ta , ta yi sauri ta fice dakin ta wuce toilet

After some minutes ta shigo cikin dakin
Lokacin har Inaya ta Kamala sallar ta , ta na zaune saman gadon su ta jingina a bayan gadon ta na rike da littafin ta ta na karantawa

Da sallama ta shigo dakin ta na sunkuyar da kai

Ba ta ce da Inaya komai ba ta wuce wajen closet din su , itama ta saka gown irin ta Inaya sai dai ta ta launin Red ce

Bayan ta saka rigar ta dauki hijab ita ma ta saka ta dauki daddumar ta

Inda Inaya ta shinfida ta ta , nan ta shinfida ita ma sannan ta gabatar da sallar ta

Ta na tsaka da sallar ta mama ta shigo dakin ta na sallama

Dago kan ta Inaya ta yi ta na amsa mata sallamar ta

" Yawwa Inaya, dan Allah tasso ki je kiyo min cepane yaran nan sun koma sangayar su " ta na gama fadar haka ta sa kai ta juya

Da sauri Inaya ta diro da ga saman gadon ta na murmushi dan dama na son fita amma ba hali

A hanzarce ta saka hijabin ta, ta saka dan takalmin ta ta fito

A harabar gidan ta isko mama cikin yar runfar da ke bakin kofar dakin ta , ta na zaune saman yar karamar kujera

Gaban ta ta karaso ta tsuguna ta na fadin " gani mama "

Dan murmushi mama ta yi kafin ta ce " to malama an ji za a fita shi ne ki ka tasso da sauri ko "

Sunkuyar da kai ta yi ta na murmushi dan mama ta gano ta

Dubu dayan da ke cikin hannun ta, ta mika mata ta ce " shikenan karbi ki sayo min albassa da timatir na dari biyar biyar ki yi sauri kin ga fa rana ta yi kar ki tsaya wannan shirmen na ki "

Yar dariya ta yi kafin ta ce " mama ni fa ba na tsaya wa shirme kin ga kullum sai na riga Nesrine isowa gida "
Ta na gama fadar haka ta tashi ta nufi hanyar fita gidan

Da kallo mama ta bi ta har ta fita gidan sannan ta ce " kai ni wannan yarinyar Allah ka shirya min ita, a ce ki na girma ki na cin kassa "

Inaya kuma ta na fita gidan ta fara wake waken da ta saba yi
A hankali ta ke tafiyar har ta karaso wajen wata bishiya
Cen ta hango wani datijo zaune kassan inuwar bishiyar ga wasu kananan yara zagaye da shi su na rike da allo su na karatu

Tun da ta hango shi ta saki wani kyawatencen murmushi ta fara takowa da sauri ta tinkaro bishiyar ta na sallama

A hankali ya dago kai ya na amsa mata sallamar ta
Wani dan murmushi ya saki kadan kafin ya ce " Auta me kuma ki ke yi nan "

Riko hanayan ta baya ta yi ta na yar jujuyawa cikin shagwaba ta ce " mama ce ta aike ni cepane "

" shikenan yi sauri ki je, kin ga rana ta yi " ya fada ya na kokarin mike wa tsaye

Jinjina mishi kai kawai ta yi ta na murmushi ta wucewar ta

Ta na barin wajen ya kali yaran ya ce da su " ku ci gaba da karatu ina zuwa "

" Toh malam " su ka fada a tare

A hankali ya ke tafiyar shi ya na sanye da manyan kaya , ka na ganin ka san wannan datijon ya na cike da haiba da mutunci

Ya yi tafiya wajen minti biyar kafin ya iso gidan da Inaya ta fito

Bakin shi da sallama ya shigo cikin gidan

Mama ta na zaune inda Inaya ta baro ta ba ta motsa ba

Ta na ganin shi ta saki murmushi ta ce " sannu da zuwa Abban Abdoul "

Jinjina mata kai ya yi kafin ya ce " Amina ba na ce miki ki bar barin yarin yar nan ta na fita ba "

Sunkuyar da kai mama ta yi kafin ta ce " yi hakouri malam Nesrine ce ta na sallat shi ne na aike ta "

" Amina da sai ki bari ta Kamala, kin fi kowa sanin hatsarin da ke bibiyar Inaya cikin rayuwar ta tun shigowar ta duniya me a ba mu fuskanta ba , a dalilin ta mu ka baro Kaduna saboda barazanar da a ke mana , yanzu in su ka samu labarin mu na nan kin san fa baza mu tsira ba , ni ko makarantar da su ke zuwa dan kin matsa ne na hakura na bar ta, ta na tafiya , ba dan Zayd ya na bibiyar ta ba ban san abun da zai faru da ita ba , dan Allah ki bar barin ta na fita wlh bazan iya jure rashin ta ba " ya fada cikin rauni zuciya

( GA DUKAN ALLAMU AKWAI WANI BOYAYEN AL'AMARI A TATARE DA AHALIN GA 🤔🤔 )

Wasu hawaye ne su ka zubo mata ta cikin zafin zuciya ta ce " yanzu dan Allah malam haka za mu ida rayuwar mu kullum mu na gudu , mi mu ka yi musu da za su ringa bibiyar mu haka , kawai dan ka hana ma d'an su auren Inaya shi ne su ke neman su kashe mana ita, meye laifin ta a cikin wannan abun yarinya karama su na neman su lalata mana rayuwar ta " ta kai karchen kuka na kubce mata

Da sauri ta juya ta koma cikin dakin ta

Ajiyar zuciya Abba ya sauke kafin ya bi bayan ta shi ma ya shiga dakin ya na sallama

Bakin gadon ya isko ta zaune ta na kukan ta

Geffen ta ya je ya zauna ya kai hannu shi bayan ta ya na dan bubugawa ya ce " kiyi hakuri Amina, in sha Allah ba abun da zai faru da ita dan na mallaka ta a hannun wanda zai kulla min da ita fiye da mu "

Dago kai ta yi ta kale shi cikin kuka ta ce " ban gane ba malam, wa ka mallakawa ita kuma me ka ke nufi "

Hannun shi ya kai ya goge hawayen ta sannan ya mike tsaye ya ce " in sha Allah in lokaci ya yi za ki san komai "
Ya na gama fadar haka ya juya ya bar dakin

Ya na fitowa harabar gidan Inaya ta shigo ta na sallama hannun ta rike da leda baka sai murmushi ta ke gwanin ban sha'awa

Ya na ganin ta ya saki murmushi shi ya ce " Auta har kin dawo "

Jinjina mishi kai kawai ta yi ta ci gaba da takawa ta shiga kitchen

Ta na shiga shi ma ya fara takawa ya nufi hanyar fita gidan

Ya na fitowa waje ya isko Zayd ya na tsaye bakin kofar gidan ya jingina da bangon gidan ya na rike da sandar shi ya dan daga kan shi ya na kallon gaban shi

Abba na ganin shi ya saki murmushi ya ce " A Zayd ashe tare ku ke "

Jinjina mishi kai Zayd ya yi sannan ya juya ya fara takawa
Murmushi Abba ya yi ya girgiza kan shi ya bi bayan shi su ka ci gaba da tafiya a tare

Sai da su ka karaso kofar wani gida dan nesa kadan da na Abba su ka tsaya a tare sannan Abba ya kale shi ya ce " Zayd za ka zo cin abincin da dadare dai ko na ga jiya ba ka zo ba "

Girgiza mishi kai kawai ba ta tare da ya ce komai ba

Dan murmushi Abba ya yi kafin ya ce " haba Zayd wai in ka na tare da ni din ma sai ka yi min kurmancin na ka "

Dan karamin murmushi geffen fuska ya yi kafin ya yi magana cikin wata zazzakar murya cike da nitsuwa ya ce " uncle ba na jin dadin maganar ne , so ku bar matsa min ina magana please " ya fada cikin wata kwarbabiyar haoussa kamar wanda ke koyo

( WAIT ! WAIT ! WAIT ! BAN GANE BA KENAN DAMA BA KURMA BA NE KO YA NE WANNAN ZANCEN YAKE 😳😳😳😳😳 )

Jinjina kan shi Abba ya yi kafin ya ce " ba komai, amma fa mu na jiran ka yau kar ka zauna ba ka zo ba " ya na gama fadar haka ya yi gaba ya ci gaba da tafiyar shi

Ya na fara tafiya shi ma Zayd ya juya ya nufi kofar gidan ya na sa hannu shi cikin aljihu

Sai da ya karaso kofar gidan ya tsaya ya ciro wasu keys da ga cikin aljihun shi ya bude kofar sannan ya shiga ya na medo kofar

Gida ne mai kyau dai'dai me hali amma fa ya fi na Abba Girma da kyau

A hankali ya ke takowa ya nufi terrace din gaban shi ya Haye
Nan ma ya sa key ya bude kofar shiga falon

Masha Allah duk da falon karami ne amma ya hadu , an saka mike wasu sofas red colour , buyi two seaters, daya three seater sai guda one seater , a tsakiyar su kuma wata yar karamar table ce ta glass sai wasu remote da ke saman ta

Da ka shigo bangaran dama ka na fuskantar wata yar karamar dining room mai dauke da dining table karama mai kujeru guda hudu
Sai wata yar drawer da ke karshen dining room din ta na dauke da kayan breakfast kamar su madara sugar coffee da sauren su

Bangaran hagu kuma wata door ce wadda za ta sada ka kitchen din

Bayan sofa mai three seater wani corridor ne mai dauke da wasu door guda biyu wanda ina kwaytata zaton bedroom ne

Bai tsaya bin ta falon ba ya wuce kai tsaye corridor din

Door ta karshe ya nufa ya kama handle din kofar ya murda ya shiga ciki ya rufo kofar
Chapter 2 · 0% Book details