Sashe 5
Exile Princess Love And Power Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ta bar wajen ya na kallon ta har ta kure wa kallon shi sannan ya dawo da kallon shi kan hafiz ya ce " bro wacece wacen yarinyar ta hadu fa, she look so innocent "
Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san in Moctar ya lakewa Inaya ta shi ga uku cikin college din nan dan sai ya azabtar da ita shi ma ba karamin mugu ba ne ga son mata
Ta yi nisa cikin tunanin ta sai ji ta yi an daura hannu saman cinyar ta
A razane ta dawo cikin hayacin ta, ta na kallon hannun hafiz da ke saman cinyar ta
" lfy baby ina tambayar ki kin yi shiru " ya fada ya na leko face din ta
" minene ? " ta fada cen kassan makoshi
Dan murmushi yayi kafin ya ce " who is she , ko sister din ki ce "
Da sauri ta ce " a'a kawai saman hanya na hadu da ita "
" okay meye sunnan ta " ya tambayeta ya na tsare ta da ido
Wasu yawu ta hadiye kafin ta ce " ban sani ba "
Tass ta ji saukar mari a face din ta
Da sauri ta kai hannu ta saman kumatun ta ta na dafe wajen wasu hawaye na zubo mata
Mike wa tsaye ya yi cikin bacin rai ya daga mata murya ya ce " ni za ki raina wa hankali ke har kin isa ki min karya "
Ya na gama fadar haka ya kai hannu ya shake ta ya hada kan ta da bishiyar cikin tsawa ya ce " meye sunnan ta na ce miki "
Cikin kuka ta ce mishi " Maryam sunnan ta Maryam " da kyair kalmar ta karshe ta fito dan ba karamar shaga ya yi mata ba
Ganin ya na neman ya kashe ta ya sa Moctar kai hannun shi ya dafa kafadar shi ya ce " bro sake ta kar ta mutu "
Da sauri ya janye hannun shi da ga wuyan ta , ya ja baya kadan kafin ya ce " nan gaba ki san irin amsar da za ki ba ni in na tambaye ki " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen
Bin bayan shi Moctar ya yi su ka bar wajen
Su na barin wajen ta fadi kassa ta konta ta na sauke kuka mai cin rai
Sai da ta share wajen good 30 minutes ta na kukan sannan ta mike a hankali ta na jan kafa ta nufi toilet din mata ta wanke face din ta sannan ta dawo ta dauki school bag din ta ta tafi class
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 3 ❤🔥
After some hours
Tafiya su ke saman titi a jere , Nesrine ta yi nisa cikin tunanin ta , ita kuma Inaya sai wassan nin ta ta ke kamar karamar yarinya
Su na tsaka da tafiyar su wata mota fara kirar Mercedes ta tsaya a gaban su ta tare musu hanyar wuce
Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san ko wanene
Inaya kuma ta yi tsaye ta na kallon motar dan ita ba ta san ko su waye ba
Su na tsaye a hakan su ka ga an bude kofofin gaban na motar Hafiz da Moctar su ka fito
Gaban su ka zo su tsaye sannan Moctar ya ce " yan mata ku zo mu rage muku hanya mana "
Dan murmushi Inaya ta yi sannan ta riko hannun Nesrine ta ce " mun gode amma mun iso gidan ai " ta kai karshen ta na rabawa ta geffen su za ta wuce
Da sauri Moctar ya sha gaban su ya ce " haba yan mata taimako ne fa "
" babu komai mun gode gidan mu fa cen karshen layin ne , ka ga kuma ba ni son Abban mu ya kan ki zai mana fada "
Ba ta gama rufe bakin ta ba ta tsinci Muryar Hafiz ya na fadin " ke Nesi wuce cikin motar nan na kai ku gida "
Wasu yawu Nesrine ta hadiye ta na tsoron ta shiga motar in malam ya gan ta zai yi mata fada, in kuma ta ki ta san halin Hafiz yanzu zai yi mata Dukan mutuwa kuma ba izinin ramawa, kawai sai ta tsaya ta na faman muzurai
Ta yi nisa cikin tunanin ta sai tsintar Muryar Abdoul su ka yi ya na fadin " Nesrine me ku ke yi a nan ? "
A razane ta juyo ta na kallon shi zuciya na duka uku uku
Ya ko tsare da wadanan dara daren idanun shi
" yaya Abdoul dama classmate din su Nesrine ne su ka ce wai su rage mana hanya shi ne na ce musu mun ma iso gida amma su ka ki yarda " Inaya ta fada babu ko tsoro
" shikenan ba komai wuce ko tafi gida yanzu "
Tun bai rufe bakin shi ba Nesrine ta kamo hannun Inaya ta raba ta geffen Moctar da sauri ta bar wajen
Su na barin wajen Abdoul ya juyawar shi shi ma ya yi tafiyar shi su ka bar Hafiz da Moctar tsaye a wajen
Bayan Abdoul ya bar wajen Moctar ya kali Hafiz da ke ta hura hanci ya ce " kai dan malam rage wannan fushin na ka, ga shi yanzu sun tafiyar su ba tare da mun ga gidan su ba "
Dan tsaki Hafiz ya ja sannan ya juya ya fara takawa ya na fadin " ai mun hadu school "
" kai malam kar ka manta ba college din ba mu ke , yawwan zuwan mu cen ya janyo mana matsala "
Geffen driver Hafiz ya bude ya shiga
Ya na ganin ya shiga motar shi ma ya bude geffen mai zaman banza ya shiga
Bayan ya shiga Hafiz ya tada motar su ka bar wajen da mugun gudu
Duk abun da ya faru a kan idon Zayd , dan ya na biye da su Inaya amma su ba su gan shi ba , ya na shirin ya je ya yi ma su Hafiz Dukan tsiya ya ga Abdoul ya shawo kwanar ya nufi su Inaya kawai sai ya yi tsayiwar shi sai da ya ga tafiyar su sannan ya juya ya kama hanyar komawa gidan shi
Bangaran Inaya kuma , sai da su ka isa cikin gidan babu wanda ta ce da yar uwarta wani abu
Sai da suka shiga cikin bedroom din su sannan Inaya ta kwace hannun ta da karfi ta dan ja baya ta na kallon Nesrine ta ce " wai me ya same ki Nesrine kin ga yadda saurayin cen ya yi miki tsawa kuma ki ka kassa ce mishi wani abu "
Cire hijabin ta Nesrine ta yi ta ajiye saman sannan ta zauna geffen gadon ta dago kai ta kali Inaya ta ce " Inaya ke karama ce baza ki gane ba amma wlh ki raba hanya da samarin nan ko cikin school in ki ka gan su ki tsere ki buya dan wlh ba mutanan kirki ba ne " ta na gama fadar haka ta tashi ta fice da ga dakin
Inaya dai ta na tsaye ta na kallon ta har ta ida maganar ta ta tashi ta bar dakin ba ta ce mata komai ba
Nesrine kuma bayan ta fita kai tsaye toilet ta shiga
Maimakon ta yi wanka sai ta jingina a jikin bangon toilet din ta aza kuka
Cikin kukan nata ta ke fadin " ya Allah na roke ka raba ni da Hafiz , ya Allah ko ba ka raba ni da shi ba kar ka bari ya kusan ci yar uwata , ban San me na yi mishi a duniya ba ya ke neman ya cutar da ni , na shiga uku ni Nesrine , RAMATOU kin cuce ni kin hada ni da bala'i da na sani bazan taba yarda da abotar ki ba, Allah ya isa tsakani na da ke "
Haka ta yi ta dimimuwan ta har ta gaji ta yi shiru sannan ta yi wanka ta fito ta koma bedroom din su
Ta na shiga ta tarda Inaya har ta yi barci dan gajiya
Misalin karfe 5 na yamma
Inaya
Zaune ta ke bakin kofar gidan su saman wasu duwatsu ta na faman wassa ita kadai kamar karamar yarinya
Tun da ga nesa ya hango ta zaune ta cikin bakin glass din shi
Ya na tare shi da Moussa, ya na sanye da wandon jeans baki da t-shirt dark blue , shi kuma Moussa jallabiya ce fara ya ke sanye da
Lokacin da Moussa ya gan ta ya saki murmushi ya kali Zayd ya ce " Amir ga fa babyn ka cen ta na wassa "
" ina ga yarinyar nan ta na da matsala a kwakwolwar ta " ya fada mishi cen kassa kassa ta yadda shi da Moussa kawai su ka ji abun da ya fada
Jinjina mishi kai Moussa ya yi dan ya lura yanayin ta bai yi kama da masu cikakiyar lafya ba a shekarun ta
Haka su ka ci gaba da tafiyar su har su ka karaso inda ta ke zaune su ka yi mata sallama
A hankali ta dago kan ta, ta na amsa musu sallamar su kafin ta ce " ina wuni yaya Moussa "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " lafya lau babyn malam , ko dai in ce babyn Zayd "
Dan zaro idanu ta yi ta na kallon Moussa sannan ta kali Zayd da ya tsareta da ido
Turo dan bakin nan nata ta yi gaba ta shagwabe fuska sannan ta ce " a'a ni babyn malam ce ni na ma tafiya ta wajen Abba " ta kai karshen ta na mikewa ta fara tafiya
Da sauri Moussa ya ce " to tsaya mu raka ki mu ma cen za mu je "
Da sauri Zayd ya kale shi dan ya lura Moussa na neman ya kwabo mishi ruwa
Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san in Moctar ya lakewa Inaya ta shi ga uku cikin college din nan dan sai ya azabtar da ita shi ma ba karamin mugu ba ne ga son mata
Ta yi nisa cikin tunanin ta sai ji ta yi an daura hannu saman cinyar ta
A razane ta dawo cikin hayacin ta, ta na kallon hannun hafiz da ke saman cinyar ta
" lfy baby ina tambayar ki kin yi shiru " ya fada ya na leko face din ta
" minene ? " ta fada cen kassan makoshi
Dan murmushi yayi kafin ya ce " who is she , ko sister din ki ce "
Da sauri ta ce " a'a kawai saman hanya na hadu da ita "
" okay meye sunnan ta " ya tambayeta ya na tsare ta da ido
Wasu yawu ta hadiye kafin ta ce " ban sani ba "
Tass ta ji saukar mari a face din ta
Da sauri ta kai hannu ta saman kumatun ta ta na dafe wajen wasu hawaye na zubo mata
Mike wa tsaye ya yi cikin bacin rai ya daga mata murya ya ce " ni za ki raina wa hankali ke har kin isa ki min karya "
Ya na gama fadar haka ya kai hannu ya shake ta ya hada kan ta da bishiyar cikin tsawa ya ce " meye sunnan ta na ce miki "
Cikin kuka ta ce mishi " Maryam sunnan ta Maryam " da kyair kalmar ta karshe ta fito dan ba karamar shaga ya yi mata ba
Ganin ya na neman ya kashe ta ya sa Moctar kai hannun shi ya dafa kafadar shi ya ce " bro sake ta kar ta mutu "
Da sauri ya janye hannun shi da ga wuyan ta , ya ja baya kadan kafin ya ce " nan gaba ki san irin amsar da za ki ba ni in na tambaye ki " ya na gama fadar haka ya juya ya bar wajen
Bin bayan shi Moctar ya yi su ka bar wajen
Su na barin wajen ta fadi kassa ta konta ta na sauke kuka mai cin rai
Sai da ta share wajen good 30 minutes ta na kukan sannan ta mike a hankali ta na jan kafa ta nufi toilet din mata ta wanke face din ta sannan ta dawo ta dauki school bag din ta ta tafi class
❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤
(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥
( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )
STORY & WRITTEN BY : ANISH
Marubuciyar littafin
TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i
♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡
PAGE 3 ❤🔥
After some hours
Tafiya su ke saman titi a jere , Nesrine ta yi nisa cikin tunanin ta , ita kuma Inaya sai wassan nin ta ta ke kamar karamar yarinya
Su na tsaka da tafiyar su wata mota fara kirar Mercedes ta tsaya a gaban su ta tare musu hanyar wuce
Dum Nesrine ta ji gaban ta ya fadi dan ta san ko wanene
Inaya kuma ta yi tsaye ta na kallon motar dan ita ba ta san ko su waye ba
Su na tsaye a hakan su ka ga an bude kofofin gaban na motar Hafiz da Moctar su ka fito
Gaban su ka zo su tsaye sannan Moctar ya ce " yan mata ku zo mu rage muku hanya mana "
Dan murmushi Inaya ta yi sannan ta riko hannun Nesrine ta ce " mun gode amma mun iso gidan ai " ta kai karshen ta na rabawa ta geffen su za ta wuce
Da sauri Moctar ya sha gaban su ya ce " haba yan mata taimako ne fa "
" babu komai mun gode gidan mu fa cen karshen layin ne , ka ga kuma ba ni son Abban mu ya kan ki zai mana fada "
Ba ta gama rufe bakin ta ba ta tsinci Muryar Hafiz ya na fadin " ke Nesi wuce cikin motar nan na kai ku gida "
Wasu yawu Nesrine ta hadiye ta na tsoron ta shiga motar in malam ya gan ta zai yi mata fada, in kuma ta ki ta san halin Hafiz yanzu zai yi mata Dukan mutuwa kuma ba izinin ramawa, kawai sai ta tsaya ta na faman muzurai
Ta yi nisa cikin tunanin ta sai tsintar Muryar Abdoul su ka yi ya na fadin " Nesrine me ku ke yi a nan ? "
A razane ta juyo ta na kallon shi zuciya na duka uku uku
Ya ko tsare da wadanan dara daren idanun shi
" yaya Abdoul dama classmate din su Nesrine ne su ka ce wai su rage mana hanya shi ne na ce musu mun ma iso gida amma su ka ki yarda " Inaya ta fada babu ko tsoro
" shikenan ba komai wuce ko tafi gida yanzu "
Tun bai rufe bakin shi ba Nesrine ta kamo hannun Inaya ta raba ta geffen Moctar da sauri ta bar wajen
Su na barin wajen Abdoul ya juyawar shi shi ma ya yi tafiyar shi su ka bar Hafiz da Moctar tsaye a wajen
Bayan Abdoul ya bar wajen Moctar ya kali Hafiz da ke ta hura hanci ya ce " kai dan malam rage wannan fushin na ka, ga shi yanzu sun tafiyar su ba tare da mun ga gidan su ba "
Dan tsaki Hafiz ya ja sannan ya juya ya fara takawa ya na fadin " ai mun hadu school "
" kai malam kar ka manta ba college din ba mu ke , yawwan zuwan mu cen ya janyo mana matsala "
Geffen driver Hafiz ya bude ya shiga
Ya na ganin ya shiga motar shi ma ya bude geffen mai zaman banza ya shiga
Bayan ya shiga Hafiz ya tada motar su ka bar wajen da mugun gudu
Duk abun da ya faru a kan idon Zayd , dan ya na biye da su Inaya amma su ba su gan shi ba , ya na shirin ya je ya yi ma su Hafiz Dukan tsiya ya ga Abdoul ya shawo kwanar ya nufi su Inaya kawai sai ya yi tsayiwar shi sai da ya ga tafiyar su sannan ya juya ya kama hanyar komawa gidan shi
Bangaran Inaya kuma , sai da su ka isa cikin gidan babu wanda ta ce da yar uwarta wani abu
Sai da suka shiga cikin bedroom din su sannan Inaya ta kwace hannun ta da karfi ta dan ja baya ta na kallon Nesrine ta ce " wai me ya same ki Nesrine kin ga yadda saurayin cen ya yi miki tsawa kuma ki ka kassa ce mishi wani abu "
Cire hijabin ta Nesrine ta yi ta ajiye saman sannan ta zauna geffen gadon ta dago kai ta kali Inaya ta ce " Inaya ke karama ce baza ki gane ba amma wlh ki raba hanya da samarin nan ko cikin school in ki ka gan su ki tsere ki buya dan wlh ba mutanan kirki ba ne " ta na gama fadar haka ta tashi ta fice da ga dakin
Inaya dai ta na tsaye ta na kallon ta har ta ida maganar ta ta tashi ta bar dakin ba ta ce mata komai ba
Nesrine kuma bayan ta fita kai tsaye toilet ta shiga
Maimakon ta yi wanka sai ta jingina a jikin bangon toilet din ta aza kuka
Cikin kukan nata ta ke fadin " ya Allah na roke ka raba ni da Hafiz , ya Allah ko ba ka raba ni da shi ba kar ka bari ya kusan ci yar uwata , ban San me na yi mishi a duniya ba ya ke neman ya cutar da ni , na shiga uku ni Nesrine , RAMATOU kin cuce ni kin hada ni da bala'i da na sani bazan taba yarda da abotar ki ba, Allah ya isa tsakani na da ke "
Haka ta yi ta dimimuwan ta har ta gaji ta yi shiru sannan ta yi wanka ta fito ta koma bedroom din su
Ta na shiga ta tarda Inaya har ta yi barci dan gajiya
Misalin karfe 5 na yamma
Inaya
Zaune ta ke bakin kofar gidan su saman wasu duwatsu ta na faman wassa ita kadai kamar karamar yarinya
Tun da ga nesa ya hango ta zaune ta cikin bakin glass din shi
Ya na tare shi da Moussa, ya na sanye da wandon jeans baki da t-shirt dark blue , shi kuma Moussa jallabiya ce fara ya ke sanye da
Lokacin da Moussa ya gan ta ya saki murmushi ya kali Zayd ya ce " Amir ga fa babyn ka cen ta na wassa "
" ina ga yarinyar nan ta na da matsala a kwakwolwar ta " ya fada mishi cen kassa kassa ta yadda shi da Moussa kawai su ka ji abun da ya fada
Jinjina mishi kai Moussa ya yi dan ya lura yanayin ta bai yi kama da masu cikakiyar lafya ba a shekarun ta
Haka su ka ci gaba da tafiyar su har su ka karaso inda ta ke zaune su ka yi mata sallama
A hankali ta dago kan ta, ta na amsa musu sallamar su kafin ta ce " ina wuni yaya Moussa "
Dan murmushi Moussa ya yi kafin ya ce " lafya lau babyn malam , ko dai in ce babyn Zayd "
Dan zaro idanu ta yi ta na kallon Moussa sannan ta kali Zayd da ya tsareta da ido
Turo dan bakin nan nata ta yi gaba ta shagwabe fuska sannan ta ce " a'a ni babyn malam ce ni na ma tafiya ta wajen Abba " ta kai karshen ta na mikewa ta fara tafiya
Da sauri Moussa ya ce " to tsaya mu raka ki mu ma cen za mu je "
Da sauri Zayd ya kale shi dan ya lura Moussa na neman ya kwabo mishi ruwa