← Book details Dahuwar Kaho Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 70 OF 81

Sashe 70

Dahuwar Kaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mai Yasin da ke gefe ya zuba wa Salame da kuka idanu yana lashe baki, saboda fara ce tas kamar Yaya Inu sai dai 'yar ƙibar mahaifiyarta da ta ɗauko.
'Yanzu wannan danƙwaleliyar aka saki, ai kuwa wannan mijin nata an yi sakarai.'
Malam ya furta a cikin ransa.

"To tsohon munafuki, ai babu kuɗin kowa a cikin auren da nake yi, kuma babu ƙaton da yake ciyar mini da su idan sun dawo gida. Ke shige gida muje." Yaya Inu ya ƙarasa maganar yana tasa ƙeyar Salame shi ma ya shige ciki, daga haka kowa ya watse.

CIKIN DARE

Tun da Mai Yasin ya ci karo da Salame ya kasa zaune ya kasa tsaye, haka kawai ya ji wani abu yana fisgarsa a kanta. Duk da tana yanayin kama da Laraba amma ta fi Labara zama cikakkiyar mace 'yar duma-duma kamar yadda yake muradi, Inno da ke gefensa ta miƙe za ta yi masa sallama ta ce.
"To Malam ni zan wuce ɗaki ko akwai abin da kake buƙata a yanzu?"
Wani munin Inno ya gani saboda yadda Salame ta mamaye zuciyarsa, haushinta ya kama shi don haka ya É—an yi tsaki a hankali ya ce.
"Babu komai za ki iya tafiya!"
Inno ta yi mamakin yanayin furucin da ya yi mata, ganin haka ya sa Mai Yasin ya wayance da cewa.

"Raina ne duk a ɓace wallahi, a ce ka saki mace da tsohon ciki wannan ai hauka ne."
A fili Inno ta saki ajiyar zuciya cikin jin daÉ—i, don yadda Mai Yasin yake nuna wa zuri'arta kulawa abin yana burge ta.

"Lamarin babu daÉ—i dai sam malam, ni bari na wuce sai da safe."

Mai Yasin ya amsa mata yana alla-alla ta fice, shi kaɗai ya dinga zarya a ɗaki yana tunanin yadda zai ɓullowa halin da yake ciki. Wata dabara ce ta faɗo masa ya saki murmushi mai sauti, kamar wanda aka yi wa dole haka Mai Yasin ya zauna tunkur har ƙarfe biyun dare ta cika. Daga shi sai gajeren wando ya zare sakatar ƙofa ya nufi sashen Yaya Inu, wannan ne zuwansa na farko sashen don haka cikin sanɗa ya kama gajeriyar katangar ya dira. Sakatar ƙofar ya zare ya bar ƙofar a buɗe saboda koda rana ta ƙwace masa ba zai sha wahalar guduwa ba.

Da yake da ɗan hasken farin wata, cikin sanɗa ya dinga bin ɗakuna yana leƙe, sai dai idan ya zura kai ba ya iya hango komai ta ciki. A haka har ya nufi ɗakin da Yaya Inu yake kwance ya shiga, domin jikinsa ya ba shi a nan Salame take a kwance. Tun dag bakin ƙofa Mai Yasin ya kwanta ya fara jan jiki a hankali, don kada a ji motsinsa a haka har ya haye kan katifar da Yaya Inu yake kwance.
Cikin bacci Yaya Inu ya ji ana shafa masa jiki, da É—an magagin bacci ya ce.

"Hansatu ce!"
Jin muryar Yaya Inu ya sa ƙirjin Mai Yasin ya buga da ƙarfi, amma don kar ya yi saurin gano shi sai ya ce.
"Ummm."
Tsaki Yaya Inu ya yi ya ce, "Ke dai kin cika jabara Hansatu, don masifa na ce miki zazzaɓi ne a jikina amma saboda ƙalata sai kin zo kin tsotse ragowar ruwan jikina."
Mai Yasin ya yi shiru ya cigaba da kai hannun yana laluben Yaya Inu, shiru Yaya Inu ya yi yana mamakin yadda Hansatu ta iya irin waɗannan abubuwan don bai taɓa jin haka daga gare ta ba. Don haka sai abin ya birge shi duk da yana jin zazzaɓin jikinsa, ya shiga mayarwa da Mai Yasin martani yana faɗin.

"Ke dai Hansatu wannan jarabar Allah Ya yaye miki, duk halin da mutum yake ciki ba za ki..."
Maganar Yaya Inu ta maƙale, ƙirjinsa ya buga da ƙarfi jin ya shafo gashin baki da gemu buzu-buzu, sai kuma ya kai hannu ya shafo kai ya ji wayam babu gashi sai ma wani sulɓi da ya ji kan yana yi kamar bayan sulba. Mai Yasin kusan mutuwar tsaye ya yi, Yaya Inu ya yi kukan kura ya ce.
"Ƙundun uba, jama'a kwarto a ɗakina zai haike mini."

A yi mini afuwa da rashin update kwana biyu, na shiga rububi amma yanzu na dawo free.

07062062624
Ummou Aslam Bint Adam
[01/01, 17:08] Ameera Adam: *GIDAN LIKITOCI*

©®AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITERS ASSO...*

Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.

*MARUBUCIYAR:*
MARWAN
JARIRI
ASEELA
BAƘAR DAULA
AN YA BAIWA CE?
ƊAN BA ƘARA...
SHU'UMAR MASARAUTA
DUBU JIKAR MAI CARBI
UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA
YAWON SALLAR HAJIYA IYA
ZAUJATU JINNUL-ASHIQ
SANADIN RAGON LAYYA

https://youtube.com/@ameerahaadam9365?si=xyR-pHK5EjkLjQnd

Don Allah duk wanda ya ci karo da wannan page ɗin, ya taimaka ya yi mana Subscribe a youtube channel ɗinmu.👆🏻👆🏻👆🏻

SHAFI NA TARA

A madadin Mai Yasin ya saki Yaya Inu ya yi ta kansa, sai ma ya sake ƙanƙame shi ta baya ya maƙale murya cikin ƙarfin hali ya ce.

"Haba Mai gida me kake son mayar da ni?"

Sororo Yaya Inu ya yi jin abin da Mai Yasin ya faɗa, sai ya fara zargin ko dai shi ne bai shafo daidai ba, ko kuma hannuwansa ne suke yi masa gizo. Don haka ya sake lalubo Mai Yasin ya ji ƙasunbarsa ta masa ƙabe-ƙabe, ya shafa gefen cinyarsa ya ji gajeren wando. A zafafe cikin zafin nama, ya kai masa naushi a fuska yana faɗin, "Mai gidan ubanka, ɗan iskan kwarto. Jama'a a kawo ɗauki." Ganin da gaske asirin Mai Yasin yana shirin tonuwa, ya sa shi fita a guje; shi ma Yaya Inu ya rufa masa baya. Sai da suka je tsakar gida Yaya Inu ya fisgo gajeren wandon Mai yasin, saboda babu riga a jikinsa idan ba haka ya yi ba zai iya kama shi har ya cim masa ba. Ganin dumu-dumu ya shiga hannu sai Mai Yasin ya zage iya ƙarfinsa ya barke wandon ya rabe biyu, ya fita a guje saboda tashin hankali a tsammaninsa sashen Inno ya nufa. Ba tare da ya ankara ba, ya haye katangar sashen Labaran ya dira. Cikin ɗakin ya faɗa a guje jikinsa har karkarwa yake yi, yana jin sa a kan katifa ya ja bargo ya rufa gumi yana keto masa.

Labaran ne ya fito daga zagayen wurin da suke tsugunno, sai da ya ajiye butar a ƙofar ɗaki sannan ya shiga ya buɗe randa ya sha ruwa, ya ƙarasa gefen gadon Rahinatu.
Murmushi ya saki a fili ganin mutum ya gangaro wurin kwanciyarsa, a tsammaninsa Rahinatu ce. Cike da shauƙin soyayya ya furta.
"Rahinatuwa kenan! Bari na gyara ki da kaina, don kada na katse miki bacci mai daɗi." Ya ƙarasa maganar cikin tattausan lafazi mai haɗe da soyayya, sannan ya saka hannu ya gyara hannun Mai Yasin da gumi ya gama wanke shi, ya yi mamaki sosai da ya ji hannun kamar ba na Rahina ba saboda ita mace ce mai ƙiba sosai. Da yake ɗakin babu haske sai ya bar abin a ransa ya raɓa ta gefe ya kwanta, sauke hannunsa da zai yi a gefen Rahinatu ya ji ana karkarwa ga gumi ya jiƙe shi. Ƙirjinsa ne ya buga da ƙarfi, a sanyaye ya ce.

"Rahinatu lafiya kuwa? Me yake damunki na ji kamar kina rawar É—ari "

Daga can gaban Mai Yasin, Rahina ta É—ago tana É—an yanutsa fuska ta ce, "Baby lafiya kake magana da tsohon daren nan?"
Da sauri Labaran ya zaro ido waje, saboda Mai Yasin a tsakiyarsu yake. Labaran shiru ya yi ya sake saɗaɗa hannu ta cikin bargo ya shafo ƙafar Mai Yasin ya ji, don ya tabbatar da ba aljani ne ya jawo masa hari ba. Saboda a fitar da ya yi fitsari a tsammaninsa indai ba aljani ba, babu wanda zai shigo masa ba tare da ya ji ƙarar buɗe ƙofa.
Ƙafar Mai yasin ya shafo ya ji 'yan yatsu irin na shi saɓanin kofato da ya yi tsammani, sai ya kai hannu ya shafo kansa. Mai Yasin ya maƙale murya ya ce, "Masoyi kada ka yarda da ita ni ce ainihin matarka."

Ware ido Rahinatu ta yi don sai a lokacin ta lura da mutum a kusa da ita, jin furucin Mai Yasin ya sa Labaran ya shafo ƙasunbarsa, ya lalubo ƙirjinsa sai ya ji shi wayam.

"Kai la'ananne sai na kashe ka, garsamemen ƙato a gefen Rahinatuna! weeeeeeeeee huuuuuuu."
Labaran ya furta a haukace haɗe da yin gurnanin da ya razana Mai Yasin, hakan ya sa ya bankaɗe bargo ya fita da gudu Labaran ya rufa masa baya. Cikin shammata Mai Yasin ya juyo ya yi masa mahangurɓa a fuska, cikin tsananin jin azaba ya zube a wurin. Rahinatu ta fito tana ihu da kururuwa, a haka Mai Yasin ya samu ya cire sakata ya fice. Ya fita kenan Yaya Inu ya sako kai cikin sashen Labaran, ya shiga wuri-wuri hannunsa ɗauke da barandami da kokara.
A haukace Labaran ya fisge daga hannun Rahinatu ya cakumi wuyan Yaya Inu yana faɗin, "Wallahi yau ko ni ko kai a gidan nan, tun da ka nemi gwada mini kwartanci." Yana faɗin haka ya kai wa Yaya Inu naushi a baki, jin zafin haka ya sa Yaya Inu ya watsar da kokarar hannunsa ya falla wa Labaran mari, nan take suka shiga kiciniya Rahinatu ban da ihu babu abin da take yi. Kafin wani lokaci tuni iyalan Yaya Inu sun cika sashen Labaran, da ƙyar aka raba su kowannensu yana mayar da numfashi.

"Kai Labaran idan ka bari na riƙe ka wallahi sai na sumar da kai, shashasha wanda bai san ciwon kansa ba."
Yaya Inu ya yi furucin yana buga tsalle, kamar zai ƙwace daga hannun su Bashar. Labaran ya ji wani takaici ya lulluɓe shi, don gani yake Yaya Inu ya gama cin tuwo a kansa, saboda maganar da yake yi masa kamar an dake shi ne kuma aka hana shi kuka. Ya zabura a hassale ya ce.
Chapter 70 · 0% Book details