← Book details Dahuwar Kaho Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 81

Sashe 43

Dahuwar Kaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Subhanallah! Allah Ya raba lafiya, bari na ƙarasa girki sai na haɗa na wanke da nawa."
Godiya ya yi mata sannan ya koma ɗakin, tun da ya shiga yana son ya tambaye ta abin da za zai girka musu da rana yana shakkar tashinta da ɓacin ranta. Tukunyarta ya buɗe ya ga akwai sauran miya, sai kawai ya ɗora taliya ya dafa musu. Kafin Fauziya ta tashi tuni Kabir ya gama komai, hatta turaren wutar da take sakawa ya saka musu. Ya shiga ɗakin ya same ta a bakin gado a zaune ta tashi, fuskarta ta sauya sosai daga jiya zuwa yau duk ta rame.

"Ga ruwan wanka zan sirka miki sai ki yi wanka."

Kabir ya furta yana satar kallonta, ko kallonsa ba ta yi ba har ya sake maimaita mata.
"Don Allah ka matsa daga gabana Kabir." Da sauri ya fice daga ɗakin, ya shiga banɗaki ya yi wanka. A inda ya bar ta a nan ya same ta, bayan ya shirya ya tambaye ta abin da take buƙata a wannan karon ma banza ta yi da shi. Don haka ya zaro dubu ɗaya ya ajiye mata, bayan ya fita ta bi bayansa da kallon tsana.

Miƙewa ta yi ta ɗauki wata 'yar babbar leda ta ɗebo kaya a drowerta, sai da ta yi wanka ta ɗauki kular abincin su ta zuba, sannan ta saka wata doguwar rigar atamfa ko man kirki ba ta shafa ba. Bakin ƙofar Lawisa ta ƙarasa ta ce.

"Lawisa ga abincin yaran nan da kayan makarantarsu, idan sun dawo don Allah su wuce makaranta."

Lawisa ta karɓa tana faɗin, "Ai na leƙa kina bacci, wai ko abar ce ta zo." Fauziya ta girgiza mata kai ta ce, "Ga wannan mukullin kuma koda babansu zai dawo."

Da mamaki Lawisa ta bi Fauziya da kallo, don ba ta taɓa tafiya unguwa ta ajiye mukulli ta ce a ba wa Kabir ba, amma sai ta haɗiye abin a ranta don tun daren jiya ta fahimci akwai abin da yake damunta saɓanin maganar da ta faɗa mata.
Sallama Fauziya ta yi mata ta fice daga gidan, tana fatan wannan fitar da ta yi daga cikinbaƙin gida ya zame mata ita ce fita ta ƙarshe da za ta yi masa.

+2347062062624
[14/02, 17:27] Ameera Adam: *NAUSHIN WUTA*

©®AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

GARGAÆŠI: Ban amince a sarrafa mini littafi da kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.

SADAUKARWA
Tun daga farko har ƙarshe, na sadaukar da wannan littafin ga duk mahaifiyar da ta kasance uwa; ko mai burin zama uwa a nan gaba. Allah Ya saka wa iyayenmu maza da mata da gidan Aljanna Amin.

SHAFI NA TAKWAS

UWAR GIDA, AMARYA HAR MA DA MAI GIDA KU MATSO KUSA.🥳🥳🥳🥳🥳🥳🥳

Ina kuke matan habiby da Habibin kansa ku matso kusa ga kaya nagani na fada wanda habiby xai saka ki kasa gane shi 😍shin kina neman inda xakisai ma mijinki kyauta ta bazata ? Maza hanxarto musaka labule jallabiya ta gani ta fada da hula mai musulmin kyau wanda xai burge oga 😍 akan farashi daidai da aljihunki kundaisan kyauta tana kara soyayya

Kaima habiby ban barka abaya ba hanxarto gurinmu ka mallaki hula da jallabiya qualitatives via +234 816 916 8731

***

Kabir tun da ya fita daga gidan ba a nutsuwarsa yake ba, kwata-kwata ya rasa me yake yi masa daɗi. Zuciyarsa ce ta shiga wassafa masa laifin abin da ya aikata, har yake jin kamar ya rabu da su Hafsee ya rungumi matarsa ita kaɗai. Ɗaya tsagin na zuciyarsa kuma, ya shiga kwaɗaita masa haɗe da harsaso masa surorin jikin Surayya da Hafsat. Nan take ya ji sam ba zai iya rabuwa da su ba, koda a ce bai auri su duka ba. To tabbas dole zai auri ɗaya, domin zuciyarsa ta jima tana kaɗayin dandalar ni'imar da Allah ya yassare musu. Rashin walwala da sukunun da yake ciki, ya sa mutanen cikin shagon suka lura da shi. Har suke tambaayarsa ko ba shi da lafiya, saboda Kabir mutum ne mai faram-faram yana da sakin fuska sosai. Ganin ya gagara gudanar da aikin da yake yi, yamma liƙs ya yi wa Ogansu sallama ya ce zai koma gida saboda ba ya jin daɗin jikinsa. Lokacin da ya tunkaro gida, kamar ya kira Fauziya a waya ya tambaye ta ko akwai abin da take buƙata ya sayo mata. Sai kawaa ya haƙura, saboda ko sunanta ya tuna gabansa faɗuwa yake yi.

Lokacin da ya ƙarasa gida kusan shida saura, su Na'ima suna jin sallamarsa suka fito daga ɗakin Lawisa da sauri suka rungume shi. Mukulli ta ba wa Fatima ta ce ta kai masa. Kabir turus ya yi a bakin ƙofar ganinta rufe da kwaɗo, kamar yaran sun san tambayar da take cikin zuciyarsa Hidaya ta ce.

"Mami ta je unguwa!"

Gabansa ne ya faɗi, ƙafafuwansa har rawa suke yi saboda tashin hankali. Da ƙyar ya iya saita nutsuwarsa hannunsa yana karkarwa ya buɗe ƙofar ɗakin suka shiga, yana shiga ɗakin ya fara kiran layin Fauziya sai dai tashin farko ya ji an ce masa a kashe take. Kamar zai yi hauka, haka ya fara zagaye ɗakin da sauri-sauri. Wani tunani ya faɗo masa cikin sauri ya sake riƙo hannun yaran, ya kai su ƙofar ɗakin Lawisa ya ce su shiga zai je ya dawo. Rufe ɗakin ya yi ya sake ba wa Lawisa mukullin sannan ya fice daga ɗakin kamar zai tashi sama.

"Ina Fauziya ta tafi? Ko dai ta tafi gidansu ne? Fauziya ba ta taɓa yin yaji ba, ko ƙarata ta kai gidansu? Yanzu haka za su dinga yi mini kallon mutumin banza? Kai Fauziya ba za ta yi mini haka ba, ina da tabbacin ba za ta bankaɗa labulen sirrina ba."

Haka Kabir ya dinga tafiya yana surutai kamar sabon taɓin hankali, domin kafin ya ƙarasa bakin titi gani ya yi hanyar ta ƙara yi masa nisa. A gurguje ya tari adaidaita sahu ya nufi uguwarsu Fauziya, yana zuwa ya samu mahaifinta a ƙofar gida yana sallar magriba. A hargitse ya zube a gabansa yana faɗin, "Baba barka da yamma."

"Baba ya yi masa kallon tsaf ganin ƙafafuwansa duk sun yi butu-butu, da mamaki ya ce. "Barka dai Kabiru, kai ne da doshin magriba haka? Ya Fauziya da yaran?"

Turus! Kabir ya yi ya ɗan sosa kansa, gabansa ya cigaba da faɗuwa saboda fargaba. Amma gudun kada Baba ya gano shi sai ya ce, "Duk lafiyarsu ƙalau, dama wucewa zan yi na ce bari na biyo mu gaisa."

Baba ya saki murmushi ya ce, "To Ma Shaa Allahu, ai jiya mun ga abin alheri. Allah dai ya raya zuri'a." Jiki a sanyaye Kabir ya amsa sannan ya cewa Baba zai wuce.
Haka Kabir ya cigaba da tafiya yana kiran layin Fauziya har lokacin a kashe, gidan ƙawarta Jamila ya je suka gaisa. Ita ma ta wurga masa tambayar Fauziya, don ta yi mamakin ganinsa a ƙofar gidanta. Saboda rabon shi da gidanta, tun tana amarya da suka zo mata shi da Fauziya kusan shekara biyar kenan.

"Kabir ko ƙawar tawa ce ta haihu?"

Jamila ta jefe masa tambaya tana gyara mayafinta.
"Amm dama na ɗauka ta ƙaraso nan ne, da yake ta fita ɗazu ta ce mini idan ba ta yi yamma ba za ta biyo ta nan. To mukullin yana hannunta, kuma akwai ɗinki wata Mai jego da aka zo karɓa daga nesa, ga ɗakin ta rufe shi. Na kuma kira wayarta a kashe." Ita ma Kabir ya zabga mata ƙarya, Jamila ta ce.

"Ai kuwa ba ta biyo ba, ina jin ko kun yi saɓani a hanya tun da magriba ta yi."
Amsa mata Kabir ya yi suka yi sallama.

Tunanin duniya ya shiga yi a kan inda zai je ya lalubo Fauziya, saboda tun da suke duk faɗan da za su yi ba ta taɓa yi masa irin haka ba. Wayarsa ce ya ji ta fara ƙara, da sauri ya ciro ta a tsammaninsa ita ce sai ya ci karo da lambar Surayya. Guntun tsaki ya saki ya ƙi ɗauka, amma sai ta cigaba da kira. A ƙufule Kabir ya ɗauka yana faɗin, "Wai Surayya me ya sa kin fiye naci ne? Idan kika ga ban ɗauka ba ai kin san ina uzuri."
Daga can ɓangaren Surayya ta kwantar da murya ta ce. "Haba sweet..."

"Babu wani sweet, Surayya ba na cikin nutsuwata yanzu haka duniyar ta yi mini zafi."

"Me yake damunka baby? Ko za ka zo na rage maka damuwa?"
Kamad Kabir ya buÉ—e baki ya faÉ—a mata abin da ya faru, sai kuma ya tuna idan ya yi haka kamar ya rusa soyayarsa ne, idan Surayya ta ji labarin hotunan tsiraicin da hafsa ta tura wa Fauziya ne ya sa ta fita daga gidan.

"Wannan ba damuwarki ba ce, family issuesne."

Daga haka ya katse wayar, sai ya sake lalubar layin Fauziya amma a kashe. Gida ya ƙarasa ya laɓe a soro, don kada mutanen gidan su fahimci akwai matsala tsakaninsa da ita.
Ganin har lokacin ba ta dawo ba ya sa Kabir ya nufi gidan Inna domin ya sanar da ita halin da ake ciki, a lokacin da ya shiga gidan har an fara kiraye-kirayen sallar Isha'i.
Yana shiga É—akin Inna ya nemi wuri ya zauna haÉ—e da haÉ—a kai da gwiwa. Inna da ta gama alwala ta shiga É—akin ta ce.
"Kabiru nake gani da daren nan?"

Kabiru ya share ƙwallar idonsa ya ce, "Inna ni ne."

"To ashe Fauziyan ta isar maka da saƙona, amma ba ka samu zuwa ba sai yau. Yau kuma me ka kawo mini, saboda dama garin tuwona ya ƙare."
Inna tana yin gama magana ta ji Kabir yana shasshekar kuka, a ɗan kaikaice ta leƙa fuskarsa ta ce.

"Wai kuka kake yi Kabiru? A cikin yaranka wata ce ta mutu?"

Kabir ya girgiza mata kai, Inna ta sake cewa.
"To Fauziyan ce ta mutu?" A nan ma ya sake girgiza mata kai.
"To uban me ya sa ka kuka tun a farkon daren nan? Ni dai na san rabon da na ga kukanka tun ranar da mahaifinku ya mutu."
Chapter 43 · 0% Book details