Sashe 9
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 27, 28
& 29
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Goggo tana zara idanu ta mike
da sauri ta dauko sabuwar
tabarma daga daki ta shimfida
mashi, ya zauna, ya gaishe da
ita cikin ladabi, ta ansa bakin
ta na kyarma, tace "ni fa har
yanzu ban dau haske ba, daga
ina kazo ne samari?" Ya saki
lallausan murmushi, sannan
yace "Sunana Nawap, dan
asalin garin kaduna ne ni,
yanayin aiki na ne ya kawo ni
Bauchi state, daga nan kuma
aka turo ni wannan gari" goggo
tace "Ayyya, to wannan tulin
kayan fa na menene?" Ya kara
murmusawa, yace "naki ne Haj.
Goggo" goggo ta zaro ido ta
dafe kirji, tace "wannan uban
kaya haka? To wai kai a ena ka
sanni ma?" Nawap cikin
zuciyar shi daria kawai yake,
ya san hakon shi ya kusan
cimma ruwa kasancewar
yanayin da goggo ta shiga, ya
san dama baza ta rasa son
abin dunia ba. Yace "ina zaune
da mahaifiya ta, ina kuma da
kanwa kwaya daya, amma tayi
aure, to mu kan samu masu
aiki da dama, sai dai da yawan
su basu zama sai su gudu,
saboda aikin gidan yana da
yawa. To jiya sai naga wata
yarinya da katon baho na ruwa
ta shigo gidan nan, hakan ya
tabbatar mun da zata iya ko
wane irin aikin wahala, shi
yasa nace bara nazo naji ta
bakin ki, ko zaki taimaka ki
bani ita? Ke kuma ina turo miki
da kudin aikin nata a ko wane
karshen wata" goggo ta gyara
zaman dankwalin ta, tace "ba
dai wannan tambadaddiyar
yarinyar kake nufi ba?" Yace
"wa kenan?" Tace "Deedo
mana, tsintacciyar mage,
shegia mai mugun hali" har
cikin zuciyan Nawap baya jin
dadin zagin da goggo take ma
marainiyar yarinyar nan, haka
dai ya daure yace "ina ga ita
din ce, ban dai san sunan ta
ba" goggo ta dan matso da
kanta dab dashi, kamar wani
zaiji abinda zata ce, a hankali
tace "nawa zaka na biya na duk
wata idan na baka ita?" A
takaice, yace "naira dubu
hamsin" dan tsabar tsorata har
sai da goggo ta hantsila baya
daga kan yar kujerar tsugunnin
da take kai, tace "dubu
hansin?" Ya gintse dariyar shi
yace "ko sunyi kadan ne
goggo?" Tace "haba ina fa, ai
ban taba kama ko rabin su ba,
bari tsinanniyar tazo, ko zata
mutu sai ta bika, kuma ko
wahala zata kashe ta, kar ta
sake ta dawo mun gidan nan,
kai ni in ka tafi da ita ma ko
ganin gida kar ta sake tazo"
Nawap kallon ikon Allah kawai
yake, tare da tsantsarar rashin
imani na matar nan, ya
muskuta, yace "ena yarinyar
take ne?" Tace "ta tafi
makaranta, ai tana dawowa ba
abinda za a jira wucewa kawai
zakuyi, daman ba wata kwalwar
fahimtar karatun ne da ita ba,
haka nan dai take zuwa
makarantar" Nawap yace "bari
dai muji ta bakin ta ko goggo"
goggo tace "in dai ta bakin
wannan shegiyar zamu tsaya ji
ai ba yarda zata yi ta bika ba,
dan haka kawai ba sai an mata
wani bayani ba" Nawap wani
irin kallo mai tattare da tsana
yake watsa ma goggo, yanzu
shi inda ace ba manufar alkairi
gare shi akan yarinyar ba, da
haka zata dauke ta ta bashi, ba
tare da tunanin shi din ko
wanene ba. A zuciyar shi yayi
Allah wadaran hali irin na
wannan matar, ya kuma yi mata
addu'ar Allah ya sa ta
dandanin kuncin rayuwa koda
rabin wanda Deedo ta dandana
ne.
Sai da ya tattaro natsuwar shi,
sannan ya saki murmushin
yake, yace "to shikenan goggo,
bara na dan zaga cikin gari zan
dawo zuwa anjima" yasa hannu
a aljihu ya ciro bandir na yan
500 ya mika mata, goggo
hannu na bari, tayi saurin
warcewa, sai da ta adana su
cikin zanin ta, sannan tace
"bayan wannan kantin guda
daka kwaso, abin kuma har da
wahala" yana tsaye yana kallon
karfin hali da munafurci irin na
goggo, ya girgiza kanshi, yayi
murmushi, yace "wannan ai
kadan ne goggo, kar ki damu"
ta wangale bakin ta, tace "to
shikenan Nawab, sai ka dawo
din" yadda ta kira sunan nashi
yasa ya kasa gintse dariyar
shi, dan haka ya dan dara,
sannan ya wuce ya fita.
Yana fita skool din su Deedo
ya zarce, direct office din
principal ya nufa, bayan sun
gaisa yake tambayar "Dr. Kaine
a garin namu" Nawap ya shafi
kyakkyawan sajen shi da ya
kwanta luf saman fuskar shi,
yace "wlh fa, ya students?"
Yace "Lafia fa" nan suka cigaba
da fira, inda yawancin firan
nasu duk akan tabarbarewar
ilimin yaran karkara ne, nan ya
samu labarin su Deedo suna
zana waec ne, wadda zasu
gama sati mai zuwa, sannan
kuma su fara neco. A haka yai
ma principal din sallama,
sannan ya fito.
A kofar gidan goggo ya tarar
da Deedo tare da hally, tana
mika mata magani da ta ciro
daga jakar ta, tace "wlh Deedo
ki natsu, yanzu kinyi girman da
za ace kin wuce duka, har ana
kumbura miki baki, wlh idan
nice ke tuni zan ture goggon
gefe, sai dai ko mai zai faru ya
faru" Deedo ta murmusa tace
"hally ke dai ki gode ma Allah
da yasa iyayen ki suna raye,
amma baki san menene
maraici ba, ni ina naga karfin
halin da zan iya taba koda
yatsan goggo ballantana kuma
in samu halin ture ta, ke dai ki
taya ni da addu'a kawai har
Allah ya kawo karshen zamana
a gidan nan" hally tace "Allah
ya taimaka, bara na wuce" suka
juyo a tare, nan suka ga Nawap
jingine jikin mota, fuskan ba
yabo ba fallasa, duk suka duka
suka gaishe shi, sannan suka
yi gaba ta dan taka ma hally,
nan take fada mata yadda suka
yi jiya, hally tace "Allah yasa ya
zamo silar fitar ki daga kangin
da kike ciki" Deedo tace
"kaman ya? Ke ni ko ganin shi
bana son yi wlh" hally tace "Ke
dai yanzu je kiji da wacce yazo
tukunna" sukai sallama ta wuce
ita kuma ta dawo, amma bata
ganshi ba dan haka tayi saurin
shigewa cikin gidan, nan ta jiyo
muryar goggo tana cewa "kaga
gantalalliyar yarinyar nan har
yanzu bata iso ba" jiki ba kwari
tayi sallama cikin gidan ta
shiga, ganin shi tayi zaune
saman tabarma, dan da nan ta
shiga tashin hankali, tasan yau
karyar ta ta kare, Allah ne
kawai zai raba ta da goggo da
bala'in ta..
Dakyar ta karaso cikin gidan, a
dai dai lokacin kuma goggo ta
fito daga daki inda suke shiga
da kayan da Nawap ya kawo
masu. Harara ta watsa mata,
sannan tace "ke dai Allah
wadaran hali irin naki, shegiyar
'ya gantalalliya, ina kika je kika
zauna kuma" ta karaso gaban
ta, ta duka tace "kiyi hakuri
goggo wlh ban tsaya ko ina ba"
tasa kafa ta wurgar da ita, tace
"daga yau dai gantalin ki ya
kare, naga gidan uban da zaki
kara yawon iskancin ki, dubi
nan" ta nuna mata Nawap da
yake zaune yana kallon goggo,
Deedo ta dago ta kalle shi,
sannan goggo taci gaba "to da
shi zaku tafi, zaki je can kina
masu aikatau, sauran kuma inji
abinda ba shikenan ba, wlh na
lahira sai ya fiki jin dadi" wani
irin kuka ta saki, duk wanda ya
kalle ta sai ya tausaya mata,
kafar goggo ta rike tana "kiyi
mun rai goggo, ki taimaki
rayuwa ta dan Allah, wlh ban
san shi ba, bazan bi shi ba,
kila ma dan yankan kai ne, wlh
zan yi miki ko mai kike so,
amma kiyi mun rai kada ki
kaini wurin yan yankan kai"
saida goggo ta tattaro karfin ta
gaba daya, sannan ta wancakar
da Deedo, har saida ta bige da
dogon karfe na baranda,
sannan tace "kinsan Allah ko
gawar ki ce sai bawan Allahn
nan ya tafi da ita, kinji dai na
rantse, baki isa ki sani kaffara
ba kuma" tayi hanyar dakin
Deedo da niyyar watso mata
tsummokaran ta, Nawap dake
gefe yana kallon abinda ke
faruwa, cikin kunan zuciya
wanda bai bari goggo ta gane
ba, yace "ehnmm goggo" tayi
saurin dawowa ta duka gaban
shi tace "ya akayi ne Nawabu?"
Saida yaja dogon numfashi,
sannan ya tuna principal din
su Deedo ya fada mashi suna
exams, sannan ya tuno da
ummin shi, at least ya kamata
ya sanar da ita kafin ya kai
mata Deedo, wata dabara ta
fado mashi, ya dan gyara
zama, sannan yace "naga
alamar yarinyar nan tana da
yan matsaloli, ga kuma yanayin
jikin ta ba wani gyaran kirki,
dan haka ina son a aje mun ita
a nan zuwa nan da kamar wata
guda, amma ina so duk wata
wahala da take yi a da ta daina
yin ta, ba don komai ba sai
don idan na kaita can ta samu
karfin yin aiyukan da muke
dasu, irin dibar ruwan nan da
sauran su, in yaso ko kofar
gida kada a rinka barin ta tana
fita, makaranta kawai na
amince taje, wannan shima
wani aiki ne, wanda zan biya
kudin shi yanzu yanzun nan"
goggo da taji maganar kudi,
tayi sauri tace "to ai shikenan
tunda dai kai ka bukaci hakan,
amma dai naso ka tafi da ita
yau din" yace "bakomai, zan
dawo nan da wata 1" yasa
hannun shi aljihu ya kara
kwaso wasu kudin ya mika wa
goggo, sannan ya mike yayi
hanyar zaure, sai da ya kare
ma Deedo kallo tsab, sannan
ya sa kai ya wuce abin shi.
Shehu ne ya rugo daga daki da
sabbin kaya jikin shi, sai da
yasa kafa ya hanbari Deedo
sannan yabi Nawap har kofar
gida yana cewa "Allah ya
kiyaye hanya" Nawap wanda
yake jin haushin su shi da
uwar su, ko kallon shi bai ba,
ya shige motar shi ya tada.
ZUMA… 27, 28
& 29
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Goggo tana zara idanu ta mike
da sauri ta dauko sabuwar
tabarma daga daki ta shimfida
mashi, ya zauna, ya gaishe da
ita cikin ladabi, ta ansa bakin
ta na kyarma, tace "ni fa har
yanzu ban dau haske ba, daga
ina kazo ne samari?" Ya saki
lallausan murmushi, sannan
yace "Sunana Nawap, dan
asalin garin kaduna ne ni,
yanayin aiki na ne ya kawo ni
Bauchi state, daga nan kuma
aka turo ni wannan gari" goggo
tace "Ayyya, to wannan tulin
kayan fa na menene?" Ya kara
murmusawa, yace "naki ne Haj.
Goggo" goggo ta zaro ido ta
dafe kirji, tace "wannan uban
kaya haka? To wai kai a ena ka
sanni ma?" Nawap cikin
zuciyar shi daria kawai yake,
ya san hakon shi ya kusan
cimma ruwa kasancewar
yanayin da goggo ta shiga, ya
san dama baza ta rasa son
abin dunia ba. Yace "ina zaune
da mahaifiya ta, ina kuma da
kanwa kwaya daya, amma tayi
aure, to mu kan samu masu
aiki da dama, sai dai da yawan
su basu zama sai su gudu,
saboda aikin gidan yana da
yawa. To jiya sai naga wata
yarinya da katon baho na ruwa
ta shigo gidan nan, hakan ya
tabbatar mun da zata iya ko
wane irin aikin wahala, shi
yasa nace bara nazo naji ta
bakin ki, ko zaki taimaka ki
bani ita? Ke kuma ina turo miki
da kudin aikin nata a ko wane
karshen wata" goggo ta gyara
zaman dankwalin ta, tace "ba
dai wannan tambadaddiyar
yarinyar kake nufi ba?" Yace
"wa kenan?" Tace "Deedo
mana, tsintacciyar mage,
shegia mai mugun hali" har
cikin zuciyan Nawap baya jin
dadin zagin da goggo take ma
marainiyar yarinyar nan, haka
dai ya daure yace "ina ga ita
din ce, ban dai san sunan ta
ba" goggo ta dan matso da
kanta dab dashi, kamar wani
zaiji abinda zata ce, a hankali
tace "nawa zaka na biya na duk
wata idan na baka ita?" A
takaice, yace "naira dubu
hamsin" dan tsabar tsorata har
sai da goggo ta hantsila baya
daga kan yar kujerar tsugunnin
da take kai, tace "dubu
hansin?" Ya gintse dariyar shi
yace "ko sunyi kadan ne
goggo?" Tace "haba ina fa, ai
ban taba kama ko rabin su ba,
bari tsinanniyar tazo, ko zata
mutu sai ta bika, kuma ko
wahala zata kashe ta, kar ta
sake ta dawo mun gidan nan,
kai ni in ka tafi da ita ma ko
ganin gida kar ta sake tazo"
Nawap kallon ikon Allah kawai
yake, tare da tsantsarar rashin
imani na matar nan, ya
muskuta, yace "ena yarinyar
take ne?" Tace "ta tafi
makaranta, ai tana dawowa ba
abinda za a jira wucewa kawai
zakuyi, daman ba wata kwalwar
fahimtar karatun ne da ita ba,
haka nan dai take zuwa
makarantar" Nawap yace "bari
dai muji ta bakin ta ko goggo"
goggo tace "in dai ta bakin
wannan shegiyar zamu tsaya ji
ai ba yarda zata yi ta bika ba,
dan haka kawai ba sai an mata
wani bayani ba" Nawap wani
irin kallo mai tattare da tsana
yake watsa ma goggo, yanzu
shi inda ace ba manufar alkairi
gare shi akan yarinyar ba, da
haka zata dauke ta ta bashi, ba
tare da tunanin shi din ko
wanene ba. A zuciyar shi yayi
Allah wadaran hali irin na
wannan matar, ya kuma yi mata
addu'ar Allah ya sa ta
dandanin kuncin rayuwa koda
rabin wanda Deedo ta dandana
ne.
Sai da ya tattaro natsuwar shi,
sannan ya saki murmushin
yake, yace "to shikenan goggo,
bara na dan zaga cikin gari zan
dawo zuwa anjima" yasa hannu
a aljihu ya ciro bandir na yan
500 ya mika mata, goggo
hannu na bari, tayi saurin
warcewa, sai da ta adana su
cikin zanin ta, sannan tace
"bayan wannan kantin guda
daka kwaso, abin kuma har da
wahala" yana tsaye yana kallon
karfin hali da munafurci irin na
goggo, ya girgiza kanshi, yayi
murmushi, yace "wannan ai
kadan ne goggo, kar ki damu"
ta wangale bakin ta, tace "to
shikenan Nawab, sai ka dawo
din" yadda ta kira sunan nashi
yasa ya kasa gintse dariyar
shi, dan haka ya dan dara,
sannan ya wuce ya fita.
Yana fita skool din su Deedo
ya zarce, direct office din
principal ya nufa, bayan sun
gaisa yake tambayar "Dr. Kaine
a garin namu" Nawap ya shafi
kyakkyawan sajen shi da ya
kwanta luf saman fuskar shi,
yace "wlh fa, ya students?"
Yace "Lafia fa" nan suka cigaba
da fira, inda yawancin firan
nasu duk akan tabarbarewar
ilimin yaran karkara ne, nan ya
samu labarin su Deedo suna
zana waec ne, wadda zasu
gama sati mai zuwa, sannan
kuma su fara neco. A haka yai
ma principal din sallama,
sannan ya fito.
A kofar gidan goggo ya tarar
da Deedo tare da hally, tana
mika mata magani da ta ciro
daga jakar ta, tace "wlh Deedo
ki natsu, yanzu kinyi girman da
za ace kin wuce duka, har ana
kumbura miki baki, wlh idan
nice ke tuni zan ture goggon
gefe, sai dai ko mai zai faru ya
faru" Deedo ta murmusa tace
"hally ke dai ki gode ma Allah
da yasa iyayen ki suna raye,
amma baki san menene
maraici ba, ni ina naga karfin
halin da zan iya taba koda
yatsan goggo ballantana kuma
in samu halin ture ta, ke dai ki
taya ni da addu'a kawai har
Allah ya kawo karshen zamana
a gidan nan" hally tace "Allah
ya taimaka, bara na wuce" suka
juyo a tare, nan suka ga Nawap
jingine jikin mota, fuskan ba
yabo ba fallasa, duk suka duka
suka gaishe shi, sannan suka
yi gaba ta dan taka ma hally,
nan take fada mata yadda suka
yi jiya, hally tace "Allah yasa ya
zamo silar fitar ki daga kangin
da kike ciki" Deedo tace
"kaman ya? Ke ni ko ganin shi
bana son yi wlh" hally tace "Ke
dai yanzu je kiji da wacce yazo
tukunna" sukai sallama ta wuce
ita kuma ta dawo, amma bata
ganshi ba dan haka tayi saurin
shigewa cikin gidan, nan ta jiyo
muryar goggo tana cewa "kaga
gantalalliyar yarinyar nan har
yanzu bata iso ba" jiki ba kwari
tayi sallama cikin gidan ta
shiga, ganin shi tayi zaune
saman tabarma, dan da nan ta
shiga tashin hankali, tasan yau
karyar ta ta kare, Allah ne
kawai zai raba ta da goggo da
bala'in ta..
Dakyar ta karaso cikin gidan, a
dai dai lokacin kuma goggo ta
fito daga daki inda suke shiga
da kayan da Nawap ya kawo
masu. Harara ta watsa mata,
sannan tace "ke dai Allah
wadaran hali irin naki, shegiyar
'ya gantalalliya, ina kika je kika
zauna kuma" ta karaso gaban
ta, ta duka tace "kiyi hakuri
goggo wlh ban tsaya ko ina ba"
tasa kafa ta wurgar da ita, tace
"daga yau dai gantalin ki ya
kare, naga gidan uban da zaki
kara yawon iskancin ki, dubi
nan" ta nuna mata Nawap da
yake zaune yana kallon goggo,
Deedo ta dago ta kalle shi,
sannan goggo taci gaba "to da
shi zaku tafi, zaki je can kina
masu aikatau, sauran kuma inji
abinda ba shikenan ba, wlh na
lahira sai ya fiki jin dadi" wani
irin kuka ta saki, duk wanda ya
kalle ta sai ya tausaya mata,
kafar goggo ta rike tana "kiyi
mun rai goggo, ki taimaki
rayuwa ta dan Allah, wlh ban
san shi ba, bazan bi shi ba,
kila ma dan yankan kai ne, wlh
zan yi miki ko mai kike so,
amma kiyi mun rai kada ki
kaini wurin yan yankan kai"
saida goggo ta tattaro karfin ta
gaba daya, sannan ta wancakar
da Deedo, har saida ta bige da
dogon karfe na baranda,
sannan tace "kinsan Allah ko
gawar ki ce sai bawan Allahn
nan ya tafi da ita, kinji dai na
rantse, baki isa ki sani kaffara
ba kuma" tayi hanyar dakin
Deedo da niyyar watso mata
tsummokaran ta, Nawap dake
gefe yana kallon abinda ke
faruwa, cikin kunan zuciya
wanda bai bari goggo ta gane
ba, yace "ehnmm goggo" tayi
saurin dawowa ta duka gaban
shi tace "ya akayi ne Nawabu?"
Saida yaja dogon numfashi,
sannan ya tuna principal din
su Deedo ya fada mashi suna
exams, sannan ya tuno da
ummin shi, at least ya kamata
ya sanar da ita kafin ya kai
mata Deedo, wata dabara ta
fado mashi, ya dan gyara
zama, sannan yace "naga
alamar yarinyar nan tana da
yan matsaloli, ga kuma yanayin
jikin ta ba wani gyaran kirki,
dan haka ina son a aje mun ita
a nan zuwa nan da kamar wata
guda, amma ina so duk wata
wahala da take yi a da ta daina
yin ta, ba don komai ba sai
don idan na kaita can ta samu
karfin yin aiyukan da muke
dasu, irin dibar ruwan nan da
sauran su, in yaso ko kofar
gida kada a rinka barin ta tana
fita, makaranta kawai na
amince taje, wannan shima
wani aiki ne, wanda zan biya
kudin shi yanzu yanzun nan"
goggo da taji maganar kudi,
tayi sauri tace "to ai shikenan
tunda dai kai ka bukaci hakan,
amma dai naso ka tafi da ita
yau din" yace "bakomai, zan
dawo nan da wata 1" yasa
hannun shi aljihu ya kara
kwaso wasu kudin ya mika wa
goggo, sannan ya mike yayi
hanyar zaure, sai da ya kare
ma Deedo kallo tsab, sannan
ya sa kai ya wuce abin shi.
Shehu ne ya rugo daga daki da
sabbin kaya jikin shi, sai da
yasa kafa ya hanbari Deedo
sannan yabi Nawap har kofar
gida yana cewa "Allah ya
kiyaye hanya" Nawap wanda
yake jin haushin su shi da
uwar su, ko kallon shi bai ba,
ya shige motar shi ya tada.