Sashe 33
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
BA’A SHAN
ZUMA…
104-106
BA'A SHAN ZUMA… 104
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Deedo wadda tunda aka fara
maganar kanta yake kasa, tana
jin wani sabon canji a jikinta,
domin yanayinta na yau, yasha
ban ban dana kullun. Mik'ewa
tayi ta zuzzuba masu abincin
cikin jin kunyar mugun kallon
da Nawap ya tsare ta dashi.
Bayan sun gama Ummi taga
abin nasu ba mai k'arewa
bane, dan haka ta wuce sama,
inda a zuciyarta take cewa "oh
ni Fatima, yaran zamani sai a
bar su, ko dan kunyar idona
ba'a ji, uhunmm" ta haura
sama, ta haye dan gadonta
tana tunanin yadda zata aurar
da ya'ya har biyu.
Deedo da Nawap wanda
soyayya tasa suka manta ko
sallar isha'i basuyi ba ne suka
ankare da lokaci, yayin da ta
sauke idanunta kan tafkekiyar
agogon bangon dake manne a
palon, k'arfe goma har da minti
ashirin da biyu (10:22pm).
Mik'ewa tayi ba wai dan ta so
ba, ta kalli Nawap wanda ya
marairaice fuska kaman zai
saki hawaye yana mata kallon
ban gaji da ganin ki ba. Alama
ta mashi da ido, abin nufin ya
kalla agogo. Wadda ke daure a
hannunsa ya duba, bai ma san
lokaci ya ja haka ba, dan haka
ya dan wara idanunsa, sannan
ya mike, hannuwansa duk
biyun cikin aljihu, ya kalli
Deedo yace "it's ok yan mata
na, ki shiga ciki, I'll call kafin ki
bacci"
Murmushin itama ta sakan
mashi, sannan ta juya tana
tafiya, sai da ta hau stairs din,
kafin ta juyo tace "don't keep
me waiting plz" cikin shagwaba
mai narkar da zuciya tayi
maganar, dan haka Nawap ya
sandare a wurin, ya kasa
motsa koda yatsan k'afarshi,
har ta haye tana mai dariya.
Girgiza kansa yayi, sannan
ya juya ya wuce side dinsa,
inda a zuciyarsa yake cewa
"tabbas ka so a so ka ma wani
babban abu ne mai tattare da
farin ciki a duniyar masoya"
* ***—-******
Soyayyar Nawap da Deedonsa
soyayya ce wadda suka
shimfid'a a kan gaskiya da
amana, soyayya mai cike da
so, tattali, da kuma kula da
junansu, wanda hakan ya basu
damar sanar da magabatansu
domin cika burin masoya.
A ranar yau, wadda tayi dai
dai da juma'a ishirin da ukku
ga watan ifirilu (23 Apr,) aka
sanya ranar auren Deedo da
Nawap dinta, wata ukku cif cif,
wanda ya kama sati daya dai
dai gama jarabawarta ta aji
hud'u (400L). Bayyana farin
cikin da masoyan suke ciki,
b'ata baki ne, domin ko suna
cikin tsananin farin cikin da ni
Lubiee ba zan iya fasalta shi
ba, lokaci kawai muke jira mu
sakata mu wala, sannan kuma
mu 6arje guminmu.
BA'A SHAN ZUMA… 105
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
BAYAN WANI LOKACI
A gajiye liss ta shigo gidan, ta
zube akan kujera tana kwala
kiran Saude wadda ta rugo da
dan saurinta tana cewa "sannu
da zuwa uwar dakina, ya
jarabawar?" Idonta a lumshe
tace "Alhamdulillah, taimaka
mun da abu mai sanyi, baki ji
ranar da na kwaso ba" "to, to
bari inzo" Saude ta fada,
sannan ta mik'e ta koma
kitchen din, ta dawo hannunta
dauke da dan tray, da jug, da
kuma cup a sama.
A gaban Deedo ta dire shi,
tace "kinyi sa'a ko, dazun nan
muka hada zo6on nan ni da
Hajiya, kinga har ya dau ra6a
kuwa" tsiyayawa Deedo tayi, ta
kai bakinta yayin da taji wata
nutsuwa ta sauko mata, ga
wani gard'i da dad'i da zo6on
ke da shi, sai da ta kara cika
wani cup din, ta sha kaman
rabi, sannan tace "lallai zo6on
nan yayi dad'i Saude, wai ina
Ummin take ma?"
"Tana ciki, ga dukkan alamu
sallah take"
"Ok, bara na shiga, nagode
Saude"
Yayin da ta mik'e ta haye
saman, ta wuce dakin Ummin
straight.
A zaune ta tarar da ita tana
duba wani littafi mai sunan
(You can be the Happiest
Woman in the world) na Dr.
A'id al-Qarni. Saida ta gama
karanta bayan littafin, sannan
tayi murmushi, ta zauna gefen
ta.
"Sannu da gida Ummi"
Da fara'arta ta dago, ta cire
medical glass din da yake
idonta, sannan ta kalle ta,
"Yawwa auta, ya exams din?"
"Alhamdulillah Ummi, amma fa
ta yau sai hamdala, ku dai taya
mu da addu'a"
"Ana ta yi ai, Allah dai ya baku
sa'a"
Tace "amin" sannan ta dukar
da kanta bakinta na motsi, da
alama akwai abinda take son
fada.
"Ya akayi ne amarya?" Ummi
ta tambaya, tana kallon ta da
alamar tsokana.
Rufe idonta tayi da duk
hannunta, tana dariya, sannan
tace "ehnmm, Ummi dama zan
ce ne dan Allah idan na gama
exams ina son zuwa ganin
Goggo, in masu bankwana"
Murmushin jin dadi Ummi tayi,
tace
"Ahaf, kin hutar da ni kenan,
dan ni ina nan na shirya irin
lallashin da zan maki akan kije
kuyi bankwana, dan ba dadi
haka kawai suji an miki aure,
ashe 'yar tawa mai hankali ce
da hakuri da kuma maida
komai ba komai ba, amma naji
dadin kasancewarki haka,
domin haka ake son dan Adam
ya kasance, duk wanda yayi
maka sharri, kai kuma ka saka
mashi da alkairi, sai kiga kai
kuma Allah yayi maka sakayya
ta wani 6angaren"
Hannunta ta rike, "Allah yayi
maki albarka Deedo, ya kuma
kare ki daga ko wane irin
sharri kinji"
Da murmushinta, ta ansa da
"amin Ummi, Allah yayi maku
sakayya da gidan aljanna
kuma"
"Amin, kinga next week zanyi
tafiya, kuma Hafsat (kanwar
Nawap) tace mun jibi zasu zo,
sai ku zauna dasu, ga Saude
kuma, idan kin gama exams, ke
kuma sai kuje da driver, nasan
kafin nan na dawo, zan zo sai
mu dawo tare, da su din ma,
tunda na san zasu zo bikin
suma"
"To shikenan, Ummi, duk
yadda kika ce haka za'ayi"
"yawwa autalle, tashi kije ki
danyi wanka ki huta kinji" ta
mik'e ta wuce dakin ta, sannan
Ummi ta maida tabaranta ta
cigaba da karatun ta.
BA'A SHAN ZUMA… 106
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Tana shiga, kiran Nawap ya
shigo mata, da murmushi ta
ansa wayar, suna firarsu ta
masoya, nan take shaida masa
zata je ganin su Goggo, yace
"yaushe kuma keda kike
exams"
"Sai na gama fa, kuma Ummi
ma tace naje ai" ta fada tana
tura bakinta gaba, kamar yana
kallon ta.
"To ke banda abinki, Ummi ce
mijinki ko ni? Idan nace a'a fa,
ya zakiyi?"
"Tafiya zanyi mana, tunda dai
Ummi ta barni, kai kuma sai ka
bari idan na zo gidanka ka juya
ni yadda ka so"
Dariya mai sauti ya saki, yace
"Yarinya kina da aiki, ai tun
yanzu zan fara ba sai kin zo
ba"
Ba tace komai ba, tayi shiru
tana saurarensa. Sai da ya
gama tsokanarta sannan yace
"I'm just kidding kinji, na san
by then na samu hutu, kinga
idan na zo sai muje tare kawai.
"Thanks hun" ta fada, bakinta
kunshe da murmushi, nan suka
cigaba da firan su har suka
gama, sannan ta mike ta fada
toilet.
* —****
Ranar da Ummi tare da
kanwarta zasu wuce Dubai,
domin hado lefen Deedo, da
kuma siyayyar wasu abubuwa
daga cikin kayan dakin ta, kiran
ta tayi, sukai sallama, inda ta
kara da cewar "duk in mun
dade, to sati guda ne, ke kam
ai jibi kike gama jarabawan
ko?"
Deedo ta girgiza kai, Ummi
tace "yawwa, kinga washegari
sai ku wuce da driver, idan na
dawo na dan huta, zan zo sai
mu dawo tare"
"Ya Nawap yace zai zo sai
muje tare wai"
"To ai shikenan ma, amma
abinda za ayi shine, to ku tafi
da Hafsat da yaranta, su sai su
dawo tare da shi, ke kuma su
baro ki can"
"To shikenan Ummi, Allah ya
tsare, ya kuma dawo daku
lafia"
Tace "amin" yayin da ta mika
mata kudi, tace "kya yi masu
tsaraba."
Gaba dayansu suka fito
domin yi masu rakiya, yayin da
driver ya dauki su Ummi zuwa
Abuja, kasancewar ta can zasu
tashi.
Bayan sun shiga Abuja,
waya sukai ma Nawap, yaje ya
samesu, nan sukai bankwana,
yayin da shi kuma ya dauko
hanyar Kd, tare da driver,
zuciyarsa fari kal yana ta
faman sharta gudu kaman zai
tashi sama.
Deedo wadda tuni suka saba
da Hafsat, tare suka shiga
kitchen suka cigaba da tanadar
mashi dad'ad'an abincin kala
kala.
ZUMA…
104-106
BA'A SHAN ZUMA… 104
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Deedo wadda tunda aka fara
maganar kanta yake kasa, tana
jin wani sabon canji a jikinta,
domin yanayinta na yau, yasha
ban ban dana kullun. Mik'ewa
tayi ta zuzzuba masu abincin
cikin jin kunyar mugun kallon
da Nawap ya tsare ta dashi.
Bayan sun gama Ummi taga
abin nasu ba mai k'arewa
bane, dan haka ta wuce sama,
inda a zuciyarta take cewa "oh
ni Fatima, yaran zamani sai a
bar su, ko dan kunyar idona
ba'a ji, uhunmm" ta haura
sama, ta haye dan gadonta
tana tunanin yadda zata aurar
da ya'ya har biyu.
Deedo da Nawap wanda
soyayya tasa suka manta ko
sallar isha'i basuyi ba ne suka
ankare da lokaci, yayin da ta
sauke idanunta kan tafkekiyar
agogon bangon dake manne a
palon, k'arfe goma har da minti
ashirin da biyu (10:22pm).
Mik'ewa tayi ba wai dan ta so
ba, ta kalli Nawap wanda ya
marairaice fuska kaman zai
saki hawaye yana mata kallon
ban gaji da ganin ki ba. Alama
ta mashi da ido, abin nufin ya
kalla agogo. Wadda ke daure a
hannunsa ya duba, bai ma san
lokaci ya ja haka ba, dan haka
ya dan wara idanunsa, sannan
ya mike, hannuwansa duk
biyun cikin aljihu, ya kalli
Deedo yace "it's ok yan mata
na, ki shiga ciki, I'll call kafin ki
bacci"
Murmushin itama ta sakan
mashi, sannan ta juya tana
tafiya, sai da ta hau stairs din,
kafin ta juyo tace "don't keep
me waiting plz" cikin shagwaba
mai narkar da zuciya tayi
maganar, dan haka Nawap ya
sandare a wurin, ya kasa
motsa koda yatsan k'afarshi,
har ta haye tana mai dariya.
Girgiza kansa yayi, sannan
ya juya ya wuce side dinsa,
inda a zuciyarsa yake cewa
"tabbas ka so a so ka ma wani
babban abu ne mai tattare da
farin ciki a duniyar masoya"
* ***—-******
Soyayyar Nawap da Deedonsa
soyayya ce wadda suka
shimfid'a a kan gaskiya da
amana, soyayya mai cike da
so, tattali, da kuma kula da
junansu, wanda hakan ya basu
damar sanar da magabatansu
domin cika burin masoya.
A ranar yau, wadda tayi dai
dai da juma'a ishirin da ukku
ga watan ifirilu (23 Apr,) aka
sanya ranar auren Deedo da
Nawap dinta, wata ukku cif cif,
wanda ya kama sati daya dai
dai gama jarabawarta ta aji
hud'u (400L). Bayyana farin
cikin da masoyan suke ciki,
b'ata baki ne, domin ko suna
cikin tsananin farin cikin da ni
Lubiee ba zan iya fasalta shi
ba, lokaci kawai muke jira mu
sakata mu wala, sannan kuma
mu 6arje guminmu.
BA'A SHAN ZUMA… 105
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
BAYAN WANI LOKACI
A gajiye liss ta shigo gidan, ta
zube akan kujera tana kwala
kiran Saude wadda ta rugo da
dan saurinta tana cewa "sannu
da zuwa uwar dakina, ya
jarabawar?" Idonta a lumshe
tace "Alhamdulillah, taimaka
mun da abu mai sanyi, baki ji
ranar da na kwaso ba" "to, to
bari inzo" Saude ta fada,
sannan ta mik'e ta koma
kitchen din, ta dawo hannunta
dauke da dan tray, da jug, da
kuma cup a sama.
A gaban Deedo ta dire shi,
tace "kinyi sa'a ko, dazun nan
muka hada zo6on nan ni da
Hajiya, kinga har ya dau ra6a
kuwa" tsiyayawa Deedo tayi, ta
kai bakinta yayin da taji wata
nutsuwa ta sauko mata, ga
wani gard'i da dad'i da zo6on
ke da shi, sai da ta kara cika
wani cup din, ta sha kaman
rabi, sannan tace "lallai zo6on
nan yayi dad'i Saude, wai ina
Ummin take ma?"
"Tana ciki, ga dukkan alamu
sallah take"
"Ok, bara na shiga, nagode
Saude"
Yayin da ta mik'e ta haye
saman, ta wuce dakin Ummin
straight.
A zaune ta tarar da ita tana
duba wani littafi mai sunan
(You can be the Happiest
Woman in the world) na Dr.
A'id al-Qarni. Saida ta gama
karanta bayan littafin, sannan
tayi murmushi, ta zauna gefen
ta.
"Sannu da gida Ummi"
Da fara'arta ta dago, ta cire
medical glass din da yake
idonta, sannan ta kalle ta,
"Yawwa auta, ya exams din?"
"Alhamdulillah Ummi, amma fa
ta yau sai hamdala, ku dai taya
mu da addu'a"
"Ana ta yi ai, Allah dai ya baku
sa'a"
Tace "amin" sannan ta dukar
da kanta bakinta na motsi, da
alama akwai abinda take son
fada.
"Ya akayi ne amarya?" Ummi
ta tambaya, tana kallon ta da
alamar tsokana.
Rufe idonta tayi da duk
hannunta, tana dariya, sannan
tace "ehnmm, Ummi dama zan
ce ne dan Allah idan na gama
exams ina son zuwa ganin
Goggo, in masu bankwana"
Murmushin jin dadi Ummi tayi,
tace
"Ahaf, kin hutar da ni kenan,
dan ni ina nan na shirya irin
lallashin da zan maki akan kije
kuyi bankwana, dan ba dadi
haka kawai suji an miki aure,
ashe 'yar tawa mai hankali ce
da hakuri da kuma maida
komai ba komai ba, amma naji
dadin kasancewarki haka,
domin haka ake son dan Adam
ya kasance, duk wanda yayi
maka sharri, kai kuma ka saka
mashi da alkairi, sai kiga kai
kuma Allah yayi maka sakayya
ta wani 6angaren"
Hannunta ta rike, "Allah yayi
maki albarka Deedo, ya kuma
kare ki daga ko wane irin
sharri kinji"
Da murmushinta, ta ansa da
"amin Ummi, Allah yayi maku
sakayya da gidan aljanna
kuma"
"Amin, kinga next week zanyi
tafiya, kuma Hafsat (kanwar
Nawap) tace mun jibi zasu zo,
sai ku zauna dasu, ga Saude
kuma, idan kin gama exams, ke
kuma sai kuje da driver, nasan
kafin nan na dawo, zan zo sai
mu dawo tare, da su din ma,
tunda na san zasu zo bikin
suma"
"To shikenan, Ummi, duk
yadda kika ce haka za'ayi"
"yawwa autalle, tashi kije ki
danyi wanka ki huta kinji" ta
mik'e ta wuce dakin ta, sannan
Ummi ta maida tabaranta ta
cigaba da karatun ta.
BA'A SHAN ZUMA… 106
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
®NWA
Tana shiga, kiran Nawap ya
shigo mata, da murmushi ta
ansa wayar, suna firarsu ta
masoya, nan take shaida masa
zata je ganin su Goggo, yace
"yaushe kuma keda kike
exams"
"Sai na gama fa, kuma Ummi
ma tace naje ai" ta fada tana
tura bakinta gaba, kamar yana
kallon ta.
"To ke banda abinki, Ummi ce
mijinki ko ni? Idan nace a'a fa,
ya zakiyi?"
"Tafiya zanyi mana, tunda dai
Ummi ta barni, kai kuma sai ka
bari idan na zo gidanka ka juya
ni yadda ka so"
Dariya mai sauti ya saki, yace
"Yarinya kina da aiki, ai tun
yanzu zan fara ba sai kin zo
ba"
Ba tace komai ba, tayi shiru
tana saurarensa. Sai da ya
gama tsokanarta sannan yace
"I'm just kidding kinji, na san
by then na samu hutu, kinga
idan na zo sai muje tare kawai.
"Thanks hun" ta fada, bakinta
kunshe da murmushi, nan suka
cigaba da firan su har suka
gama, sannan ta mike ta fada
toilet.
* —****
Ranar da Ummi tare da
kanwarta zasu wuce Dubai,
domin hado lefen Deedo, da
kuma siyayyar wasu abubuwa
daga cikin kayan dakin ta, kiran
ta tayi, sukai sallama, inda ta
kara da cewar "duk in mun
dade, to sati guda ne, ke kam
ai jibi kike gama jarabawan
ko?"
Deedo ta girgiza kai, Ummi
tace "yawwa, kinga washegari
sai ku wuce da driver, idan na
dawo na dan huta, zan zo sai
mu dawo tare"
"Ya Nawap yace zai zo sai
muje tare wai"
"To ai shikenan ma, amma
abinda za ayi shine, to ku tafi
da Hafsat da yaranta, su sai su
dawo tare da shi, ke kuma su
baro ki can"
"To shikenan Ummi, Allah ya
tsare, ya kuma dawo daku
lafia"
Tace "amin" yayin da ta mika
mata kudi, tace "kya yi masu
tsaraba."
Gaba dayansu suka fito
domin yi masu rakiya, yayin da
driver ya dauki su Ummi zuwa
Abuja, kasancewar ta can zasu
tashi.
Bayan sun shiga Abuja,
waya sukai ma Nawap, yaje ya
samesu, nan sukai bankwana,
yayin da shi kuma ya dauko
hanyar Kd, tare da driver,
zuciyarsa fari kal yana ta
faman sharta gudu kaman zai
tashi sama.
Deedo wadda tuni suka saba
da Hafsat, tare suka shiga
kitchen suka cigaba da tanadar
mashi dad'ad'an abincin kala
kala.