← Book details Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 36

Sashe 10

Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

BA’A SHAN
ZUMA… 30, 31&
32
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Acikin Gida kuwa goggo takalli
deedo sannan tace "kinji
abunda yace!, tsintacciyar
mage wacce bata gaji arziki ba,
albarkacinki daya karna miki
dukan tsiya kisamu illa yafasa
daukanki, donhaka kije kina
hutawa," takamo kunnenta
sannan tace "saura kuma da
gigin wasa kice bazakijeba,
kokuma inkinje su koroki, wlh
saina hallakaki" deedo dai
shiru tayi, tana ganin goggo ta
shige daki, itama ta mike ta
shige akurkin ta, ta cire
uniform dinta sannan ta fito
tayi alwala ta koma ciki.
Zuwan nawap gidan goggo ba
karamin alkhairi bane yajawo a
rayuwar kuncin da Deedo take
ciki, domin kuwa tadenaa
aiki,harta kai ko tsintsiya ta
dauka, goggo ta fara zagin ta
tana cewa zata janyo musu
asaran arziki, hakan yabata
daman yin karatu, hatta a
makaranta sukansu sun lura da
zuwa dawuri datakeyi, hally har
zolayen ta takeyi, tana cewa "
Allah ya yi abin, inji mafadin
aure. kekuma aidole kidawo
shalele, kudi saan kowa,
mutuncin kowa, mu dai muna
godewa Allah daya taimakemu
yakawo karshen wahala duk da
bauta zakijeyi" itadai Deedo ta
kan rasa abin cewa, duk da
tana son ta rabu da azabar
goggo, amma kuma bata son
bin mutumen da bata san daga
ina yake ba.
* **Nawap kuwa koda ya fito
gidan goggo, gudu ya rinka yi
sosai, har ya isa garin kaduna.
Ta Alkali road ya bi, sannan ya
shiga cikin Isah Kaita road,
gida mai No. 55 ya danna horn
mai gadin cikin uniform ya
rugo da gudu ya bude mashi,
bai jira komai ba ya kunna kan
motar ciki. Parking yayi ya
shiga gidan a gajiye, saida yayi
wanka yayi sallah sannan
yafito. Mahaifiyar tasa na
zaune a falo yazauna yana
sosa kai, kallon shi tayi, ta dan
yi murmushi sannan tace
"meya faru?" Ya dan gyara
zama, ya dukarda kanshi kasa
yace "Wlh ummi wata nasamu
a wani kauye da aka taba kaini
aiki, taban tausauyi sosai,
yarinyar tana cikin wani hali,
inason nataimaka mata, don
Allah inason kawota nan, ko
aiki tana dan tabawa" ummi
tayi murmushi ganin cewan
halin nan nashi na taimakon
mutane da tausayi, bai canja
ba, tace "bakomi, ai shi da' ai
na kowa ne, kakawota mana"
yasan daman ba zai taba
samun matsala da ummin shi
ba, kasancewar ita ta dora shi
akan wannan kyakkaywar
tarbiyya ta tausayi da jin kai.
Dan haka cikin farin ciki ya
wuce dinning ya ci abincin shi
yayi kat, sannan ya koma side
din shi dan ya dan huta..
BAYAN GAMA WAEC ND
NECO….. Ranana da Deedo
tagama exams dayamma tana
zaune, wani murna takeyi
tamkar zata shiga aljanna, ta
godewa Allah sannan tanemi
albarkan karatun agunsa,
sallama taji saiga shehu ya
rugo da gudu yana kiran
goggo, da sauri tafito tana
cewa "mei kuma ka samo mana
yau?" Ya wangale baki yana
cewa "Goggo nawabu ne yazo"
Idonta ta zaro sannan tace
"yana ina?" Yace"yana waje," da
gudu gudu goggo ta koma
tacanja zanin jikinta, ta jawo
wani sabon mayafi ta buga
sannan ta fito, yara ta gani
sunata shigowa da carton
carton da buhhuna da manyan
ledoji, ta washe baki tana cewa
"Nawabu sarkin kokari, baya
gajiya da hidima, ku aje nan"
tace da yaran, sannan dasauri
goggo ta shige daki taciro wata
atamfa sabuwa kal, dakin
Deedo ta shiga tabata tare da
cewa "ungo wannan, yi sauri
kisa, yaganki fes fes abunki,
kozamu samu da tsoka" ita dai
ansa kawai tayi tasa ba tare da
ta fahimci abinda goggo ke
nufi ba. Da sallama ya shigo
cikin gidan, goggo na jin shi
tayi saurin fita suka gaysa, sai
a sannan Deedo ta fahimci
abinda ke faruwa, Dam taji
gaban ta ya fadi lokacin data
jiyo shi yana cewa yazo tafiya
da ita ne. Goggota gyara
zaman mayafin ta, tace "Ah
itakam dasauki ai, kaga kuma
yau tagama jarabawa sai farin
ciki take" bai ce komai ba, dan
bai yadda da goggo ba, burin
shi dai yaga Deedo sannan ya
tabbatar da abinda take fada,
jin da tayi yayi shiru yasa ta
kwala mata kira, Deedo ta fito
jiki ba kwari, fuskan ta ba yabo
ba fallasa, gashi kuma ta dan
yi kumari, ga wani dan haske
da tayi abin ta. Juyawa yayi ya
kalla goggo, sannan yace "ai
babu wata matsala ko?" Goggo
ta wangale baki, tace "babu
komai Nawabu, tafiya kawai ya
rage muku" yasa hannun shi
aljihu ya fito da kudi masu
yawa ya mika mata, sannan ya
mike tsaye yace "idan ta gama
ta same ni a mota" yasa kai ya
fice kofar gidan
Goggo na ganin fitar shi, ta
kwashe kudin da ya bata, ta
kama bakin zanin ta ta daure
su tam, sannan ta juyo inda
Deedo take tsugunne bata da
niyyar tashi. Kunnen ta ta
damka, tayi daki da ita, tace
"kinsan Allah, idan kika yi
abinda mutumen nan yasa
yace ya fasa tafiya dake, sai
dai uwar ki ta dawo daga lahira
ta haifa wata, dan wlh sai na
hallaka ki, shegia wadda bata
gaji arziki ba" ta wurga ta, ta
ce "maza hada inaki inaki ki
wuce ku tafi, kuma ko da ganin
gida kar ki sake ki dawo mun
nan" Deedo ta dan matse
kwalla, ta shiga tattara yan
kayan ta, ta daure a dankwali,
ta matse a hammata, sannan ta
fito. Shehu da goggo suna
kofan dakin suna jiran ta,
Hadiza kuwa tunda Nawap ya
fita ta bi bayan shi tana
karairaya wai ita dole don ya
ganta ya kyasa, wanda shi bai
ma taba tunanin Allah yayi
halittan ta ba a wurin. Shehu
ya buga ihu yace "yau zamu
yar da dajar mangwaro mu
huta da kuda" goggo tace "kai
dai bari mana kar ya jiyo ka"
haka suka tasa keyar Deedo
gaba suna binta a baya, shehu
har dan jawo mata kullin kayan
ta yake yana cewa "tsintacciyar
mage bata mage" sai ya
kyalkyale da daria, a haka har
suka iso gaban motar. Deedo
ta bude gidan baya ta shiga,
goggo kuma ta koma ta side
din Nawap tana cewa "Allah ya
tsare Nawabu, sai na ji sako
na" wani kallo mai tattare da
tsana ya watsa mata, sannan a
zuciyan shi yace "zaki ga sako
ganin idon ki" a fili kuma ya
dan daga mata kai, alaman sai
ta ji shi din, sannan yai ma
motar key suka dau hanya.
Suna fitowa layin gidan goggo,
Deedo dake matse yan kwalla
daga bayan mota, tace "dan
Allah ina son in yima hally
sallama" ba tare da ya kalle ta
ba yace "ina me gidan?"
Kwanar ta gwada mashi ya
shiga, suka so har kofar gidan,
sannan ta fita ta shige gidan
su hally. Ta gaishe da maman
su, sannan ta wuce dakin hally,
ta same ta zaune ta gama
sallan la'asar, ta zauna a gefen
gado tace "nazo yi maki
sallama ne, yanzu zan tafi"
hally ta mike suka rungume
juna suna dan kuka, a haka
suka fito har bakin motan,
suka yi sallama, tare da
alkawarin baza su taba manta
juna ba har abada. Tana shiga
ko, ya ja motan sai garin
kaduna..
Chapter 10 · 0% Book details