Sashe 23
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 70-72
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Dr. Kashim ne ya katse su da
cewa "yawwa Affan ka zo ne?
Karaso ciki mana" cikin jin
kunya ya dan shafi sumarshi
ya karasa cikin office din ya
mika gaisuwarshi ga Dr.
Kashim, inda shi kuma a
hankali kwance ya ansa, ba
tare da ya dago ba, ya cigaba
da typing din da yake akan
laptop dinshi.
Kujeran da ke kallon ta Deedo
ya zauna, kura mata ido yayi,
inda a bangarenta itama ta
kasa tantance dalilin da yasa
take jin dadin kallon da yake
mata.
Dr. Kashim ya dago daga
kallon laptop din gabanshi,
yace "yawwa, Affan plz, wani
taimako za kai mun dan Allah"
ya maida dubanshi ga Dr. Yace
"na me fa? Hope dai ba aike
bane, cuz ina da class karfe
sha biyu" ya fada yana duban
kayataccen agogon hannunshi.
Dr. Yace "kai fa problem dina
da kai kenan, ka cika laziness
kaman, mace" murmushi Affan
yayi, ba tare da yace komai ba,
inda Dr. ya cigaba da magana..
"Wannan sister phrnd dina ce,
tazo registration ne, nd as yu
can see bani da time da zanyi
guiding dinta, kuma ba zai
yiwu na hada ta da Secretary
dina ba, plz ka taimaka mata
komai da za'a bukata tana
dashi, zaku je kuyi clearance
ku ansa admission, then sai ku
fara reg, plz my Lil bro" ya fada
yana kallonshi, inda shi kuma
ya dan dage giranshi tare da
kafada irin na big boys, yace
"alright then, I'll try my best"
sannan ya mike, ya cigaba da
kallon Deedo, yace "let's go
beautiful" murmushi tayi kawai,
ta mike ta yi wa Dr. godiya,
sannan ta fita.
Dr. Kashim ne ya kwala ma
Affan kira a yayin da yake
kokarin bin bayan Deedo, yace
"plz, ka kula da yarinyar nan,
amanan Dr. Nawap ne kana ji
na?" Juyawa yayi yana dan
bouncing yace "have no probz
bro.." yana dariya ya bar office
din, Dr. Ya girgiza kanshi,
sannan cikin zuciyarshi yace
"Affan the trouble maker"
Tare da taimakon Affan Deedo
ta kammala clearance dinta
tsab, ta anshi admission letter
dinta. Bayan sun fito ne tayi
deciding kiran Nawap ta fada
mashi, nan ta ci karo da 3
missed calls dinshi, sai da ta
duba taga ashe wayan silent ta
shiga lokacin da ta jefa ta cikin
jaka. Da sauri ta fara kiran
number har kuma ta katse bai
dauka ba, ta kara kira a karo na
biyu, nan ma shiru kake ji. Ba
tare da wata damuwa ba ta
maida wayan cikin jaka,
sannan ta cigaba da yan kalle
kallen yadda students suke
shawaginsu hankali kwance.
"Hey beautiful" taji an fada
cikin muryar nan tashi mai
dadin sauraro. Juyowa tayi
dauke da murmushi ba tare da
tace komai ba. Ya karaso ya
zuba mata idanu, sannan yace
"zamu je inyi lecture, idan na
fito sai muyi wani abun, zuwa
gobe kuma sai mu karasa ko?"
Ya fada yana mai cigaba da
kallon kyakkyawar fuskarta.
Bata iya yi mashi gardama ba,
dan haka suka mika zuwa
wurin da yayi parking suka
shige motan, sannan ya fara
k'ok'arin tadawa.
Bayan sun shiga motan sun
zauna ne, har ya tada, amma
sai bai tafi ba, kallonshi tayi
tare da alamar tambaya, nan ta
ci karo da shanyayyun
idanuwanshi na aiko mata wani
sako wanda har sai da
zuciyarta ta buga lokaci guda.
Dakyar ta daure tace "muje
mana" cikin wata irin murya ya
langab'ar da kanshi yace
"Feedo I can't hold it, to be
honest, you're beautiful nd
you've a beautiful smile too"
murmushi ne ya kwace mata,
inda tasa gyalenta ta dan rufe
fuskanta, a hankali ya furta
"OMG look at ha dimples, I love
them" ya dan ciji leb'enshi,
sannan ya daure yayi ma
motan key suka bar wurin.
Zaune take a gefenshi, inda ya
tattara hankalinshi gaba daya
yana kallonta ba tare da sanin
ta ba, kasancewar hankalinta
na kan game din da take yi a
wayanta. Wasu phrnds dinshi
ke ta tambayar inda ya samo
ta, amma yana ta basarwa, shi
a dole kada su samu fuskan yi
mata magana.
WANENE AFFAN?
Affan Taufiq, matashi ne mai
shekaru ashirin da biyar a
duniya, namiji dan gayu wanda
ya saba da hutu mai asalin zati
da kwarjini a wurin jama'a.
Kyakkyawa ne dai dai misali,
sai dai yana da wasu idanuwa
masu haske da walk'iya wanda
sune suke rikita duk wata
mace da tayi arba da kallonshi.
Iyayenshi Alh. Taufiq, da Haj.
Maryam yan asalin garin
mak'arfi ne ta jihar Kaduna,
amma Allah yayi masu rasuwa
tun Affan yana shekara goma a
duniya, wannan yasa rik'onshi
ya dawo hannun yayan
mahaifinshi, wato Daddyn su
Dr. Kashim.
Affan ya kasance masoyin
karatun likitanci kamar Deedo
tun daga k'uruciyarshi, wannan
yasa ya zama zakaran gwajin
dafi a gaba daya department
dinsu, tun ranar da ya fara har
izuwa yanzu da yake a final
year dinshi.
* *
Misalin karfe biyar na yamma a
gajiye liss Deedo ta koma gida,
a palo ta zube inda ta tarar da
Ummi, nan ta gaisheta, cikin
yanayi na tausayawa Ummi ta
ansa, sannan tace "makaranta
ba dadi ko auta?" Murmushi
Deedo tayi tace "a hankali zan
saba Ummi" ta mike saman 2
seater, can kuma tace "Ummi
ko Yaa Nawap ya kiraki?" "A'a
bai kira ba, ya akayi ne?"
"Munyi magana kafin na isa
skool, to na manta waya na
silent ashe ya kira, na kira
kuma bai dauka ba"
Ummi tace "may be aiki yake,
idan ya gani zai kira" bata kara
cewa komai ba, ta koma ta
kwanta luf, fuskan Affan ce ke
dawo mata, yadda yake
tsokananta da yadda yake
magana, abin na bala'in birgeta
murmushi ta saki, a dai dai
lokacin kuma wayanta ya fara
ruri,hakan yayi sanadiyyar
yankewar tunaninta.
Yaa Nawap ta gani, dan haka
tayi saurin dagawa, tana
kokarin gaishe da shi, taji yace
"haka muka yi dake? Wane irin
abu ne ban fada maki ba kafin
na tafi? Haka nace ki rink'a
dressing idan zaki je skool?
Wato kin raina ni ko? Ni ban
isa ince ga yadda zakiyi ba, kin
tashi kinyi uban kwalliya kin
tafi skool, a haka zaki
karatun?"
Kyarma hannunta ya fara yi, a
karon farko kuma ta saci kallon
kujeran da Ummi ke zaune
amma bata ganta ba, cikin
murya mai alaman ta kuka tace
"I'm sorry Yaa Nawap, wallahi
banyi dan na b'ata maka ba,
bazan sake ba in sha Allah"
wata muguwar tsawa ya daka
mata wadda ta sa yan hanjinta
motsawa lokaci guda, nan da
nan hawayen da suka mak'ale
suka gangaro saman fuskarta,
ba tare da ya jira me zata ce
ba ya datse wayan, sannan
yayi wurgi da ita saman kujerar
dake gefenshi..
ZUMA… 70-72
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Dr. Kashim ne ya katse su da
cewa "yawwa Affan ka zo ne?
Karaso ciki mana" cikin jin
kunya ya dan shafi sumarshi
ya karasa cikin office din ya
mika gaisuwarshi ga Dr.
Kashim, inda shi kuma a
hankali kwance ya ansa, ba
tare da ya dago ba, ya cigaba
da typing din da yake akan
laptop dinshi.
Kujeran da ke kallon ta Deedo
ya zauna, kura mata ido yayi,
inda a bangarenta itama ta
kasa tantance dalilin da yasa
take jin dadin kallon da yake
mata.
Dr. Kashim ya dago daga
kallon laptop din gabanshi,
yace "yawwa, Affan plz, wani
taimako za kai mun dan Allah"
ya maida dubanshi ga Dr. Yace
"na me fa? Hope dai ba aike
bane, cuz ina da class karfe
sha biyu" ya fada yana duban
kayataccen agogon hannunshi.
Dr. Yace "kai fa problem dina
da kai kenan, ka cika laziness
kaman, mace" murmushi Affan
yayi, ba tare da yace komai ba,
inda Dr. ya cigaba da magana..
"Wannan sister phrnd dina ce,
tazo registration ne, nd as yu
can see bani da time da zanyi
guiding dinta, kuma ba zai
yiwu na hada ta da Secretary
dina ba, plz ka taimaka mata
komai da za'a bukata tana
dashi, zaku je kuyi clearance
ku ansa admission, then sai ku
fara reg, plz my Lil bro" ya fada
yana kallonshi, inda shi kuma
ya dan dage giranshi tare da
kafada irin na big boys, yace
"alright then, I'll try my best"
sannan ya mike, ya cigaba da
kallon Deedo, yace "let's go
beautiful" murmushi tayi kawai,
ta mike ta yi wa Dr. godiya,
sannan ta fita.
Dr. Kashim ne ya kwala ma
Affan kira a yayin da yake
kokarin bin bayan Deedo, yace
"plz, ka kula da yarinyar nan,
amanan Dr. Nawap ne kana ji
na?" Juyawa yayi yana dan
bouncing yace "have no probz
bro.." yana dariya ya bar office
din, Dr. Ya girgiza kanshi,
sannan cikin zuciyarshi yace
"Affan the trouble maker"
Tare da taimakon Affan Deedo
ta kammala clearance dinta
tsab, ta anshi admission letter
dinta. Bayan sun fito ne tayi
deciding kiran Nawap ta fada
mashi, nan ta ci karo da 3
missed calls dinshi, sai da ta
duba taga ashe wayan silent ta
shiga lokacin da ta jefa ta cikin
jaka. Da sauri ta fara kiran
number har kuma ta katse bai
dauka ba, ta kara kira a karo na
biyu, nan ma shiru kake ji. Ba
tare da wata damuwa ba ta
maida wayan cikin jaka,
sannan ta cigaba da yan kalle
kallen yadda students suke
shawaginsu hankali kwance.
"Hey beautiful" taji an fada
cikin muryar nan tashi mai
dadin sauraro. Juyowa tayi
dauke da murmushi ba tare da
tace komai ba. Ya karaso ya
zuba mata idanu, sannan yace
"zamu je inyi lecture, idan na
fito sai muyi wani abun, zuwa
gobe kuma sai mu karasa ko?"
Ya fada yana mai cigaba da
kallon kyakkyawar fuskarta.
Bata iya yi mashi gardama ba,
dan haka suka mika zuwa
wurin da yayi parking suka
shige motan, sannan ya fara
k'ok'arin tadawa.
Bayan sun shiga motan sun
zauna ne, har ya tada, amma
sai bai tafi ba, kallonshi tayi
tare da alamar tambaya, nan ta
ci karo da shanyayyun
idanuwanshi na aiko mata wani
sako wanda har sai da
zuciyarta ta buga lokaci guda.
Dakyar ta daure tace "muje
mana" cikin wata irin murya ya
langab'ar da kanshi yace
"Feedo I can't hold it, to be
honest, you're beautiful nd
you've a beautiful smile too"
murmushi ne ya kwace mata,
inda tasa gyalenta ta dan rufe
fuskanta, a hankali ya furta
"OMG look at ha dimples, I love
them" ya dan ciji leb'enshi,
sannan ya daure yayi ma
motan key suka bar wurin.
Zaune take a gefenshi, inda ya
tattara hankalinshi gaba daya
yana kallonta ba tare da sanin
ta ba, kasancewar hankalinta
na kan game din da take yi a
wayanta. Wasu phrnds dinshi
ke ta tambayar inda ya samo
ta, amma yana ta basarwa, shi
a dole kada su samu fuskan yi
mata magana.
WANENE AFFAN?
Affan Taufiq, matashi ne mai
shekaru ashirin da biyar a
duniya, namiji dan gayu wanda
ya saba da hutu mai asalin zati
da kwarjini a wurin jama'a.
Kyakkyawa ne dai dai misali,
sai dai yana da wasu idanuwa
masu haske da walk'iya wanda
sune suke rikita duk wata
mace da tayi arba da kallonshi.
Iyayenshi Alh. Taufiq, da Haj.
Maryam yan asalin garin
mak'arfi ne ta jihar Kaduna,
amma Allah yayi masu rasuwa
tun Affan yana shekara goma a
duniya, wannan yasa rik'onshi
ya dawo hannun yayan
mahaifinshi, wato Daddyn su
Dr. Kashim.
Affan ya kasance masoyin
karatun likitanci kamar Deedo
tun daga k'uruciyarshi, wannan
yasa ya zama zakaran gwajin
dafi a gaba daya department
dinsu, tun ranar da ya fara har
izuwa yanzu da yake a final
year dinshi.
* *
Misalin karfe biyar na yamma a
gajiye liss Deedo ta koma gida,
a palo ta zube inda ta tarar da
Ummi, nan ta gaisheta, cikin
yanayi na tausayawa Ummi ta
ansa, sannan tace "makaranta
ba dadi ko auta?" Murmushi
Deedo tayi tace "a hankali zan
saba Ummi" ta mike saman 2
seater, can kuma tace "Ummi
ko Yaa Nawap ya kiraki?" "A'a
bai kira ba, ya akayi ne?"
"Munyi magana kafin na isa
skool, to na manta waya na
silent ashe ya kira, na kira
kuma bai dauka ba"
Ummi tace "may be aiki yake,
idan ya gani zai kira" bata kara
cewa komai ba, ta koma ta
kwanta luf, fuskan Affan ce ke
dawo mata, yadda yake
tsokananta da yadda yake
magana, abin na bala'in birgeta
murmushi ta saki, a dai dai
lokacin kuma wayanta ya fara
ruri,hakan yayi sanadiyyar
yankewar tunaninta.
Yaa Nawap ta gani, dan haka
tayi saurin dagawa, tana
kokarin gaishe da shi, taji yace
"haka muka yi dake? Wane irin
abu ne ban fada maki ba kafin
na tafi? Haka nace ki rink'a
dressing idan zaki je skool?
Wato kin raina ni ko? Ni ban
isa ince ga yadda zakiyi ba, kin
tashi kinyi uban kwalliya kin
tafi skool, a haka zaki
karatun?"
Kyarma hannunta ya fara yi, a
karon farko kuma ta saci kallon
kujeran da Ummi ke zaune
amma bata ganta ba, cikin
murya mai alaman ta kuka tace
"I'm sorry Yaa Nawap, wallahi
banyi dan na b'ata maka ba,
bazan sake ba in sha Allah"
wata muguwar tsawa ya daka
mata wadda ta sa yan hanjinta
motsawa lokaci guda, nan da
nan hawayen da suka mak'ale
suka gangaro saman fuskarta,
ba tare da ya jira me zata ce
ba ya datse wayan, sannan
yayi wurgi da ita saman kujerar
dake gefenshi..