Sashe 28
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 87, 88
& 89
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Da murmushi Ummi ta shiga
d'akin, wuri ta samu a bakin
gado ta zauna, sannan ta kai
dubanta ga Deedo wadda take
kuka bil hak'k'i da gaskiya. A
hankali ta furta "oh, auta ba
dai abinda wancen yayi miki
bane kike kuka?" Sai a sannan
Deedo ta san da shigowarta,
kasancewar kanta na kasa tayi
ruf da ciki. Ba tare da ta jira
ansarta ba ta cigaba "ke manta
mun da shi auta, babu wanda
zai miki dole kinji 'yar albarka,
dan haka tashi maza, ki wanke
fuskar nan taki bana son ganin
bacin ranki 'yar auta ta" cikin
jin kunya, Deedo tana sum
sum da kai ta mik'e ta shige
toilet, wanka tayi sosai, sannan
ta fito, amma bata tarar da
Ummi ba.
Shiryawa ta cigaba da yi dan
lokacin maghriba ta gabato,
kasancewar tana hutun sallah,
ga wani yunwa da yake
addabar cikinta yasa tayi
gaggawan sauka kasa domin
ta samu abinda zata ci. Zaune
ta tarar dashi a kujerar da ta
barsa ya k'ura wa halittar t.v
ido, amma daga dukkan alamu,
bai san abinda ke faruwa cikin
t.v din ba. Sad'af-sad'af tayi ta
shige kitchen, shi kam jin
kanshin turarenta yasa yayi
zumbur, ya dawo daga dogon
tunanin da yake.
Mik'ewa yayi yabi hanyar
kitchen din, can ya hango ta
tana faman daga manya
manyan food flask din da su
kan zuba abinci. A kofan
kitchen din ya harde
hannayrnsa, ya zuba mata
idanu wanda bata ma san
Allah yayi ajiyarsa a wurin ba.
Ta gama dibar abincinta, tana
k'ok'arin fitowa, amma ya kare
hanyar ta yadda baza ta iya
wucewa ba matuk'ar bai bata
hanya ba.
Ido ya k'ura mata sosai ta
yadda ba wani motsi da zata
iya yi. Take ta daburce, ta
nema natsuwarta ta rasa, bata
ta6a tunanin Nawap na da
kyau haka ba, ga wasu irin
idanunshi masu kamar yana jin
bacci, dak'yar ta sauke idonta
a kansa, cikin k'arfin hali tace
"zan wuce Yaa Nawap" bai ce
komai ba, sai ma gyara
tsayuwarsa da yayi, ya
fuskance ta sosai. Har ya daga
baki zai fara masifa, sai kuma
ya tuno da kalaman Ummi
wanda tace "mu mata mun fi
son lallami" sumarsa ya shafa,
cikin boron kunya ya daure
yace "Lil sis, yanzu haka kike
ganin ya dace ace munyi
dake?"
Bata ansashi ba, dan haka ya
cigaba "ban son yadda akai na
kamu da soyayyarki ba, haka
na tashi na tsinci kaina a
cikinta, amma a tunanina, baza
ki ta6a gujewa duk wani abu
da ya shafe ni ba, matuk'ar ba
sa6on Allah bane." Ya ja
gauron numfashi sannan ya
cigaba "soyayyarki ta riga ta yi
mani mugun kamu, wanda in
har ban samu goyon bayanki
ba, komai zai iya faruwa,
amma idan kina ganin zan
takura ki, fine, kina da 'yancin
da zaki zabar ma kanki dukkan
abinda kike so, amma kafin
kiyi saurin yanke hukunci, ina
son kiyi nazari, duk shawarar
da kika yanke, zan aminta da
ita, matuk'ar abin zai zama
farin ciki a gare ki."
Ya gyara mata hanya, yace
"zaki iya wucewa" bata ce
uffan ba, ta bi gefensa ta wuce
palon, yayin da shi kuma ya
fito ya kwashe wayoyinsa,
sannan ya wuce part dinshi.
Juyawa spoon din hannunta
kawai ta cigaba da yi, ita dai ta
san bata k'in Yaa Nawap, dan
shine mutun na farko da ya
daga darajarta a lokacin da
bata da wani gata balle kuma
'yanci, shine wanda ya inganta
rayuwarta da farin cikin da ta
dade tana mafarkin samu. To
amma ya zata yi da Affan
wanda ko wane bugun
zuciyarta yake fita da son shi
da k'aunarshi? Ya za ta yi da
shak'uwa da karamcin da ya
nuna mata a cikin dan
k'ank'anin lokacin da ta san
shi? "Ya Allah ga ni gare ka"
shine abinda ta furta, tare da
ture plate din da yake gabanta
zuwa gefe.
Wayanta ne ya fara ruri alamar
text yana shigo mata, hannu ta
sa ta ciro shi a aljihun dake
jikin rigarta, text din ta fara
dubawa kamar haka "Hope
you're fine Feedo na?"
Murmushin k'arfin hali ta saki,
sannan ta fara typing mashi
ansa "I'm good, kayi hak'uri da
abinda ya faru dazu fa"
Take ta ji ansar shi ta dawo
mata, "never mind dear, but
wanene shi a wurin ki?"
"Cousin dina ne" ta maida
mashi ansa itama.
Dam! Zuciyar Affan ta buga, ba
don komai ba sai don jin
dangantakar dake tsakanin
Nawap da Deedo, shi dai yana
son ta, har cikin ransa, amma
ya san aure tsakanin su abu ne
mai matuk'ar wahala, domin ko
ga Dr. Kashim nan har yanzu
bai yi aure ba, ya san da kunya
ya kai batun nashi auren daga
gama skool dinshi, sannan
yanayin da Nawap ya shiga a
yau, ya tabbatar mashi da
cewar yana k'aunar Feedo fiye
da yadda yake son ta, kuma ko
bakomai zai so mata abinda
yake mafi alkairi ne a gare ta,
dan haka yana jin zai iya
sadaukarwa Nawap da
soyayyar da yake wa Feedo ba
don komai ba sai dan
cancantar shi da ya gani.
Jin shiru bai dawo mata da
ansa ba yasa ta k'ara tura
mashi "are you there?"
Shigowar message din ne ya
katse tunanin shi, a hankali ya
share zufanda ta karyo mashi,
sannan ya fara rubuta mata
ansa "ki fada mun gaskia kina
son shi ko?"
Kamar daga sama ta ji
tambayar, haka dai ta daure
tace "I can't say Affan, but,
shine mutumin da ya 'yanta ni,
ya mayar da ni abinda nake a
yau"
"Ok, na fahimce ki, ki kwantar
da hankalinki, zamu yi magana
anjima kinji?"
"Alright, take care" ta tura
masa, sannan ta mik'e a
3seater ta cigaba da tunanin
halin da take ciki.
Number Hally ta fara kira
amma har ta katse shiru bata
daga ba, dan haka ta shafa
mata lafia, don ta san indai ta
gani, to zata kira ta.
BA’A SHAN
ZUMA… 90&91
NALUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tunani kam tayishi harta gaji,
ta rasa me zatayi, don tasan ba
karamin butulci bane tace taki
jinin ummi,
Shikuwa acikin kwanakin
yakara daburcewa yadawo wani
iri har Ummi tagane saidai bata
ce masa komi yadawo baya ko
kulata ayayinda shikuma Affan
yariga da ya cire abun aransa
yasawa kansa cewa ya hakura
kawai, tunda tamishi bayanin
komi na rayuwanta da nawap,
randa taje makaranta lectures
ma sun zauna anan yace mata
"ina ga zan baki zabi ne, kije
kiduba kiga wa kika fi so,
zanzama mai farin ciki da
bayaninki, zan kuma yarda da
kaddara, saidai kisani cewa
inasonki ba kuma zan hadaki
da wata ba, niyyata na aureki"
Har ya idar da bayaninsa
batace komi ba, ita dai ta shiga
rudani gashi shareta da nawap
keyi yakara sata awani
damuwan.
Nawap a gida yasamu ummi ya
ce yana son magana da ita, ta
ce "toh" sannan ta zauna
yafara sosa keya sannan yace
"Ummi na zauna nayi tunani
ne, wlh inason Feedo ba kadan
ba, don Allah ummi ki mana
aure" tunda ya fadi kalmomin
sa tasan cewa tabbas dagaske
yanason feedo din tunda tasan
shi mutum ne mai balain
kunya, bai taba tunkararta da
magana shige irin wannan ba
tayi murmushi sannan tace
"Ai dole sai yar tawa ta
Amince, zan mata auren dole
ne aka gaya ma?"
Yayi shiru don bai tabbatar
tana sonshi ba yace " zata
cemiki tanason wani ne, wlh
ummi kar ki yarda, yaro ne
yaudaranta zaiyi" itadai ta zura
mishi ido aranta kuwa kaman
ta juye ruwa a kasa tasha don
murna, tadade tana adduan
Allah yanuna mata wannan
rana da zata hadasu aure,
shikenan tuwonta maiyanta,
Feedo kuwa bayan tagama
tunaninta duk ansa daya ta
kare dashi, wato nawap takeso,
takira Affan tace inta gama
lectures suhadu nan ya
amince, ko da yazo yazauna
akan kujera a dept dinsu
datake jiranshi, ta ce "ni dai
nasan randa nafara soyayya
dakai, bantaba yi don ranka
yabaci ba, banyi don na
yaudareka ko na rabu dakai
daga baya ba, ban yi da zuciya
biyu ba, anma kasan dan adam
ajizi yau an wayi gari bakai din
zancigaba da so ba, maganan
gaskiya yaa nawap nafara so
arayuwata, shi ya maidani
mutum har ka ganni kakeso,
shi ya taimakamin kuma yana
kai, mahaifiyarsa ita tarikeni da
zuciya daya, ban mata adalci
ba ace dan cikinta guda yace
yana sona naki yarda, ba zata
ji dadiba duk da zata nunamin
ba komi anma danka naka ne,
kayi hakuri ka gafarceni" tana
fada ta share hawayenta,
shima kallonta yake har ransa
tausayinta yake ji, yace
"bakomi wallahi, na fahimceki
sosai ubangiji Allah ya sa
hakan shiyafi alheri, nima Allah
hadani da wata" nan suka
danyi tadi sannan ta mike don
komawa aji
ZUMA… 87, 88
& 89
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Da murmushi Ummi ta shiga
d'akin, wuri ta samu a bakin
gado ta zauna, sannan ta kai
dubanta ga Deedo wadda take
kuka bil hak'k'i da gaskiya. A
hankali ta furta "oh, auta ba
dai abinda wancen yayi miki
bane kike kuka?" Sai a sannan
Deedo ta san da shigowarta,
kasancewar kanta na kasa tayi
ruf da ciki. Ba tare da ta jira
ansarta ba ta cigaba "ke manta
mun da shi auta, babu wanda
zai miki dole kinji 'yar albarka,
dan haka tashi maza, ki wanke
fuskar nan taki bana son ganin
bacin ranki 'yar auta ta" cikin
jin kunya, Deedo tana sum
sum da kai ta mik'e ta shige
toilet, wanka tayi sosai, sannan
ta fito, amma bata tarar da
Ummi ba.
Shiryawa ta cigaba da yi dan
lokacin maghriba ta gabato,
kasancewar tana hutun sallah,
ga wani yunwa da yake
addabar cikinta yasa tayi
gaggawan sauka kasa domin
ta samu abinda zata ci. Zaune
ta tarar dashi a kujerar da ta
barsa ya k'ura wa halittar t.v
ido, amma daga dukkan alamu,
bai san abinda ke faruwa cikin
t.v din ba. Sad'af-sad'af tayi ta
shige kitchen, shi kam jin
kanshin turarenta yasa yayi
zumbur, ya dawo daga dogon
tunanin da yake.
Mik'ewa yayi yabi hanyar
kitchen din, can ya hango ta
tana faman daga manya
manyan food flask din da su
kan zuba abinci. A kofan
kitchen din ya harde
hannayrnsa, ya zuba mata
idanu wanda bata ma san
Allah yayi ajiyarsa a wurin ba.
Ta gama dibar abincinta, tana
k'ok'arin fitowa, amma ya kare
hanyar ta yadda baza ta iya
wucewa ba matuk'ar bai bata
hanya ba.
Ido ya k'ura mata sosai ta
yadda ba wani motsi da zata
iya yi. Take ta daburce, ta
nema natsuwarta ta rasa, bata
ta6a tunanin Nawap na da
kyau haka ba, ga wasu irin
idanunshi masu kamar yana jin
bacci, dak'yar ta sauke idonta
a kansa, cikin k'arfin hali tace
"zan wuce Yaa Nawap" bai ce
komai ba, sai ma gyara
tsayuwarsa da yayi, ya
fuskance ta sosai. Har ya daga
baki zai fara masifa, sai kuma
ya tuno da kalaman Ummi
wanda tace "mu mata mun fi
son lallami" sumarsa ya shafa,
cikin boron kunya ya daure
yace "Lil sis, yanzu haka kike
ganin ya dace ace munyi
dake?"
Bata ansashi ba, dan haka ya
cigaba "ban son yadda akai na
kamu da soyayyarki ba, haka
na tashi na tsinci kaina a
cikinta, amma a tunanina, baza
ki ta6a gujewa duk wani abu
da ya shafe ni ba, matuk'ar ba
sa6on Allah bane." Ya ja
gauron numfashi sannan ya
cigaba "soyayyarki ta riga ta yi
mani mugun kamu, wanda in
har ban samu goyon bayanki
ba, komai zai iya faruwa,
amma idan kina ganin zan
takura ki, fine, kina da 'yancin
da zaki zabar ma kanki dukkan
abinda kike so, amma kafin
kiyi saurin yanke hukunci, ina
son kiyi nazari, duk shawarar
da kika yanke, zan aminta da
ita, matuk'ar abin zai zama
farin ciki a gare ki."
Ya gyara mata hanya, yace
"zaki iya wucewa" bata ce
uffan ba, ta bi gefensa ta wuce
palon, yayin da shi kuma ya
fito ya kwashe wayoyinsa,
sannan ya wuce part dinshi.
Juyawa spoon din hannunta
kawai ta cigaba da yi, ita dai ta
san bata k'in Yaa Nawap, dan
shine mutun na farko da ya
daga darajarta a lokacin da
bata da wani gata balle kuma
'yanci, shine wanda ya inganta
rayuwarta da farin cikin da ta
dade tana mafarkin samu. To
amma ya zata yi da Affan
wanda ko wane bugun
zuciyarta yake fita da son shi
da k'aunarshi? Ya za ta yi da
shak'uwa da karamcin da ya
nuna mata a cikin dan
k'ank'anin lokacin da ta san
shi? "Ya Allah ga ni gare ka"
shine abinda ta furta, tare da
ture plate din da yake gabanta
zuwa gefe.
Wayanta ne ya fara ruri alamar
text yana shigo mata, hannu ta
sa ta ciro shi a aljihun dake
jikin rigarta, text din ta fara
dubawa kamar haka "Hope
you're fine Feedo na?"
Murmushin k'arfin hali ta saki,
sannan ta fara typing mashi
ansa "I'm good, kayi hak'uri da
abinda ya faru dazu fa"
Take ta ji ansar shi ta dawo
mata, "never mind dear, but
wanene shi a wurin ki?"
"Cousin dina ne" ta maida
mashi ansa itama.
Dam! Zuciyar Affan ta buga, ba
don komai ba sai don jin
dangantakar dake tsakanin
Nawap da Deedo, shi dai yana
son ta, har cikin ransa, amma
ya san aure tsakanin su abu ne
mai matuk'ar wahala, domin ko
ga Dr. Kashim nan har yanzu
bai yi aure ba, ya san da kunya
ya kai batun nashi auren daga
gama skool dinshi, sannan
yanayin da Nawap ya shiga a
yau, ya tabbatar mashi da
cewar yana k'aunar Feedo fiye
da yadda yake son ta, kuma ko
bakomai zai so mata abinda
yake mafi alkairi ne a gare ta,
dan haka yana jin zai iya
sadaukarwa Nawap da
soyayyar da yake wa Feedo ba
don komai ba sai dan
cancantar shi da ya gani.
Jin shiru bai dawo mata da
ansa ba yasa ta k'ara tura
mashi "are you there?"
Shigowar message din ne ya
katse tunanin shi, a hankali ya
share zufanda ta karyo mashi,
sannan ya fara rubuta mata
ansa "ki fada mun gaskia kina
son shi ko?"
Kamar daga sama ta ji
tambayar, haka dai ta daure
tace "I can't say Affan, but,
shine mutumin da ya 'yanta ni,
ya mayar da ni abinda nake a
yau"
"Ok, na fahimce ki, ki kwantar
da hankalinki, zamu yi magana
anjima kinji?"
"Alright, take care" ta tura
masa, sannan ta mik'e a
3seater ta cigaba da tunanin
halin da take ciki.
Number Hally ta fara kira
amma har ta katse shiru bata
daga ba, dan haka ta shafa
mata lafia, don ta san indai ta
gani, to zata kira ta.
BA’A SHAN
ZUMA… 90&91
NALUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tunani kam tayishi harta gaji,
ta rasa me zatayi, don tasan ba
karamin butulci bane tace taki
jinin ummi,
Shikuwa acikin kwanakin
yakara daburcewa yadawo wani
iri har Ummi tagane saidai bata
ce masa komi yadawo baya ko
kulata ayayinda shikuma Affan
yariga da ya cire abun aransa
yasawa kansa cewa ya hakura
kawai, tunda tamishi bayanin
komi na rayuwanta da nawap,
randa taje makaranta lectures
ma sun zauna anan yace mata
"ina ga zan baki zabi ne, kije
kiduba kiga wa kika fi so,
zanzama mai farin ciki da
bayaninki, zan kuma yarda da
kaddara, saidai kisani cewa
inasonki ba kuma zan hadaki
da wata ba, niyyata na aureki"
Har ya idar da bayaninsa
batace komi ba, ita dai ta shiga
rudani gashi shareta da nawap
keyi yakara sata awani
damuwan.
Nawap a gida yasamu ummi ya
ce yana son magana da ita, ta
ce "toh" sannan ta zauna
yafara sosa keya sannan yace
"Ummi na zauna nayi tunani
ne, wlh inason Feedo ba kadan
ba, don Allah ummi ki mana
aure" tunda ya fadi kalmomin
sa tasan cewa tabbas dagaske
yanason feedo din tunda tasan
shi mutum ne mai balain
kunya, bai taba tunkararta da
magana shige irin wannan ba
tayi murmushi sannan tace
"Ai dole sai yar tawa ta
Amince, zan mata auren dole
ne aka gaya ma?"
Yayi shiru don bai tabbatar
tana sonshi ba yace " zata
cemiki tanason wani ne, wlh
ummi kar ki yarda, yaro ne
yaudaranta zaiyi" itadai ta zura
mishi ido aranta kuwa kaman
ta juye ruwa a kasa tasha don
murna, tadade tana adduan
Allah yanuna mata wannan
rana da zata hadasu aure,
shikenan tuwonta maiyanta,
Feedo kuwa bayan tagama
tunaninta duk ansa daya ta
kare dashi, wato nawap takeso,
takira Affan tace inta gama
lectures suhadu nan ya
amince, ko da yazo yazauna
akan kujera a dept dinsu
datake jiranshi, ta ce "ni dai
nasan randa nafara soyayya
dakai, bantaba yi don ranka
yabaci ba, banyi don na
yaudareka ko na rabu dakai
daga baya ba, ban yi da zuciya
biyu ba, anma kasan dan adam
ajizi yau an wayi gari bakai din
zancigaba da so ba, maganan
gaskiya yaa nawap nafara so
arayuwata, shi ya maidani
mutum har ka ganni kakeso,
shi ya taimakamin kuma yana
kai, mahaifiyarsa ita tarikeni da
zuciya daya, ban mata adalci
ba ace dan cikinta guda yace
yana sona naki yarda, ba zata
ji dadiba duk da zata nunamin
ba komi anma danka naka ne,
kayi hakuri ka gafarceni" tana
fada ta share hawayenta,
shima kallonta yake har ransa
tausayinta yake ji, yace
"bakomi wallahi, na fahimceki
sosai ubangiji Allah ya sa
hakan shiyafi alheri, nima Allah
hadani da wata" nan suka
danyi tadi sannan ta mike don
komawa aji