Sashe 5
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 13
NA LUBABATU MAITAFSIR
&BENAXIR OMAR
Yadda taga Deedo ta takure
wuri daya tana wata irin
kyarmar sanyi, abin ya bala'in
bata tausayi, nan take taji wata
muguwar tsanar goggo ta kara
shiga ranta, wasu kwalla masu
zafi suka zubo mata, ta karasa
gaban ta, tana yi mata sannu,
Deedo kasa magana tayi,
hawaye ne kawai yake anbaliya
a fuskan ta. Hally ta ciro rigar
sanyin jikin ta, ta sanya mata
sannan ta tayar da ita zaune, ta
bude skool bag dinta ta fito da
biredi da shayi a cikin roban
coke, ta mika mata, kamar
tasan abinda yake damun ta,
ba tare da bata lokaci ba
Deedo ta ansa ta fara yagar
bread din nan, bata saurara ba
saida ta gama cinye shi tas,
sannan ta kora da ruwan
shayin tayi gyatsa, hally da
hawaye suka cika idon ta, ta
share ta fito da paracetamol ta
mika mata tasha. Sannan tace
"ki kwanta ki huta, zan fada ma
form master baki da lafia,
anshi sauran maganin nan ki
boye in anjima ki kara shan
guda biyu, kiyi hakuri Deedo ki
dauka wannan bakomai bane,
wata rana sai dai ki bada labari
in sha Allah,kinsan ita rayuwa
daman ta gaji haka, kuma BA'A
SHAN ZUMA SAI AN SHA
HARBI, ina ji a jikina akwai
ranar da goggo zata bukace ki,
ranar da bata da wani
mataimaki bayan ke, Allah ya
sauwake kinji" ta dago
idanuwan ta cike da kwalla,
bakin ta na kyarma tace
"nagode hally, Allah ya saka
maki da alkairi, ke kadai kike
sona duk fadin duniyar nan,
Allah ya biya ki da gidan
aljanna" ta rufe mata baki da
hannun ta, sannan ta share
mata hawayen, ta dau jakan ta
tayi mata sallama, ta fito ko
kallon inda goggo da ya'yan ta
suke bata yi ba, ta wuce ta bar
gidan.
Deedo na nan kwance kamar
gawa, dan ko motsin kirki bata
iyawa, goggo ta leka dakin,
tana kiran sunan ta amma
shiru, ta karasa gaban ta tasa
kafa ta hankada ta, cikin gigin
bacci tayi firgigit ta mike tana
zara idanu…
BA’A SHAN
ZUMA… 14
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Kafin ta karasa washewa taji
goggo ta damko gashin kanta
tayi waje da ita. Cikin kuka tace
"Dan Allah goggo kiyi hakuri,
wlh ban san mai nai miki ba"
ta watsar da ita a kasa tace
"yanzu zaki sani dan uban ki"
dakin ta ta wuce ta fito da
almakashi tace "bara na aske
wannan shegen kan, sai inga
ta karyar iskanci. Har ni zaki
bazawa wani banzan gashin ki
kina ji ina kira amma kika yi
shiru" ta fara ihu ta tashi ta
runtuma da gudu tayi hanyar
zaure, goggo ma ko bata yi
kasa a gwiwa ba ta daddage ta
cafko ta, Deedo tasa hannuwan
ta ta lullube gashin ta dasu,
amma ena goggo ta riga ta
damko wani gefe na gashin
mai uban yawa, bata yi wata
wata ba tasa almakashin ta
datse. Deedo ganin gashin ta
mai uban yawa a kasa yasa ta
kurma wani gagarumin ihu,
wanda hatta goggo saida ta
razana. Malam Ilu ne ya shigo
gidan da sauri, ganin abinda
goggo ta aikata yasa ya karasa
shigowa da gudu, sai da ya
daddage sannan ya hankadar
da goggo ta fadi kasa warwas!
Cikin daga murya yace "Ke
Batula kiji tsoron Allah, wlh ina
jiye miki ranar da alhakin
wannan yarinyar zai tambaye
ki, ke yanzu duk uban dukan
da kikai mata jiya bai ishe ki
ba, dan bakin ciki shine yau
har da aske mata gashi, ke
baki tunanin wata rana zaki
mutu ki bar abinda kika haifa?
Ya zaki ji idan wani ya rinka
cuzkuna musu irin yadda kike
wa wannan marainiyar Allahn,
in baki iya rike ta ki kai ta
gidan marayu mana.." kafin
mallam Ilu ya rufe bakin shi
goggo ta daddage ta cilla mai
almakashin da yake hannun ta,
bai tsaya a ko ina ba sai a
saman goshin shi, kafin yayi
wani motsi jini ya riga ya
wanke mashi fuska tasss!
BA’A SHAN
ZUMA… 15
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Ihu Deedo ta saka ganin jini ya
wanke wa mal. Ilu fuska, da
gudu ta ruga ta warto wani
kallabi na goggo da yake
shanye akan igiya tana kokarin
daure mai wurin, cikin gadara
da rashin nadamar abinda
goggo ta aikata ta taso da
sauri ta warce kallabin, tace
"wato iskanci naki har da irin
wannan kucakan kike yi? Mei
zaki samu a jikin wannan
tsohon? Lallai Deedo, daman
na dade ina zargin ku, sai
gashi zato na ya tabbata" ta
juya ta kalli mal. Ilu da yake
raba idanuwa tace "to wlh baku
isa ba daga kai har ita, kuma
idan ma kashe ta nake tana
farkowa akwai abinda ya
shalleh ka ne? Ince zama na
take yi a gidan ko? Ko ko
daman dan kuna labewa kuna
iskancin ku shine har zaka zo
ka tare mata, to ni Batula ba
kanwar lasa bace, duk wanda
yace zai ja dani wlh sai jikin
shi ya gaya mishi, wannan ma
da na maka kadan ne, dan a
ciki na so in caka maka
almakashin ka mutu kowa ma
ya huta dan banga amfanin da
kake tsinanawa wani ba a cikin
gidan nan" tana kaiwa nan, ta
bi ta gefen su, tasa kafa ta
hanbare Deedo ta kara gaba
abin ta..
Deedo wadda tausayin mal.
Ilu yasa ta manta da tata
larurar, tace "kayi hakuri baba,
ka lallaba kaje chemist a gyara
maka wurin kar wata cutar ta
shiga" yace "kar ki damu
Firdausi, dunia ce, ta ishi
Batula riga da wando har ma
da mayafi" ya mike dakyar yana
ganin jiri, ya wuce ya fita ya
bar gidan.
Allah mai iko, ashe wannan fita
ita ce fitar mal. Ilu ta karshe,
yaje zai tsallaka titi ba tare da
ya kula ba wani mai mota ya
banje shi, nan take ya ce ga
garin Ku nan.. Kulli nafsi
za'katul maut! Allah ya jikan
mal. Ilu da rahma amen!
BA’A SHAN
ZUMA… 16
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Hakika deedo taji rasuwan mal.
Ilu , tana tuna kalmominsa na
karshe akanta,gwaggo batayi
nadama ko kadan ba, don
taaziya ma sau daya ta leka,
Deedo kuwa harta rame, tafada
takara baki, asatin tafara zuwa
makaranta, cikin ikon Allah
saigashi wani malami yashigo
ajin, yadebi masu kokari uku,
ciki harda deedo sukaje ofishin
principal, nan ya sanar dasu
cewa gasa zasuyi wanda akwai
baki daga kaduna zasuxo don
su ga wannan gasa, akwai
kyaututtuka masu tsoka dazaa
raba, deedo tayi farin ciki
sosai, nan da nan akabasu
topic na debate
FEMALE EDUCATION IS MORE
USEFUL THAN MALE
EDUCATION IN THE SOCIETY,
inda ita zatayi supporting,
zuwa tayi tasami malamin
turancinn su tabashi don
yarubuto mata hujja dazata
kare kanta, yakuwa karba,
Ranan da tadawo gida duk
bakin cikin da gwaggo ke son
tusa mata, deedo taki bata rai
sai faraa take abun harya
damu gwaggo, washegari
dawurwuri tadebo ruwanta. Duk
da bayanta baigama warkewa
ba tanufi makaranta tanajira,
hally tayi mamakin ganinta
dawuri haka, malamin na isowa
takarba, tafara haddacewa, har
ajiye haly tayi tana koya
agabanta, dahaka tahaddace
komi akanta takuma yi
murajaan yadda zata fita
tabada tsokacinta
Ran jumaa aka taru a hall na
makaranta duk dalibai suntaru
don ganin wannan ranan da
zaaraba kyaututtuka, karfe
takwas na safe aka bukaci
suje, agyda kuwa tunda shehu
yazo yasanar da gwaggo
abunda zai faru , gwaggo ta
tsiri aiki ranan, harda sa deedo
wankin bango, deedo tanayi
zata fita tadauko ruwan kayan
miya tabata wai tafitar, tsabar
nauyinsa saidaya bata mata
kaya gashi batada wani
uniform din sawa, dawuri tafice
agydan don isa makaranta
BA’A SHAN
ZUMA… 17
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Hakika deedo taji rasuwan mal.
Ilu , tana tuna kalmominsa na
karshe akanta,gwaggo batayi
nadama ko kadan ba, don
taaziya ma sau daya ta leka,
Deedo kuwa harta rame, tafada
takara baki, asatin tafara zuwa
makaranta, cikin ikon Allah
saigashi wani malami yashigo
ajin, yadebi masu kokari uku,
ciki harda deedo sukaje ofishin
principal, nan ya sanar dasu
cewa gasa zasuyi wanda akwai
baki daga kaduna zasuxo don
su ga wannan gasa, akwai
kyaututtuka masu tsoka dazaa
raba, deedo tayi farin ciki
sosai, nan da nan akabasu
topic na debate
FEMALE EDUCATION IS MORE
USEFUL THAN MALE
EDUCATION IN THE SOCIETY,
inda ita zatayi supporting,
zuwa tayi tasami malamin
turancinn su tabashi don
yarubuto mata hujja dazata
kare kanta, yakuwa karba,
Ranan da tadawo gida duk
bakin cikin da gwaggo ke son
tusa mata, deedo taki bata rai
sai faraa take abun harya
damu gwaggo, washegari
dawurwuri tadebo ruwanta. Duk
da bayanta baigama warkewa
ba tanufi makaranta tanajira,
hally tayi mamakin ganinta
dawuri haka, malamin na isowa
takarba, tafara haddacewa, har
ajiye haly tayi tana koya
agabanta, dahaka tahaddace
komi akanta takuma yi
murajaan yadda zata fita
tabada tsokacinta
Ran jumaa aka taru a hall na
makaranta duk dalibai suntaru
don ganin wannan ranan da
zaaraba kyaututtuka, karfe
takwas na safe aka bukaci
suje, agyda kuwa tunda shehu
yazo yasanar da gwaggo
abunda zai faru , gwaggo ta
tsiri aiki ranan, harda sa deedo
wankin bango, deedo tanayi
zata fita tadauko ruwan kayan
miya tabata wai tafitar, tsabar
nauyinsa saidaya bata mata
kaya gashi batada wani
uniform din sawa, dawuri tafice
agydan don isa makaranta
ZUMA… 13
NA LUBABATU MAITAFSIR
&BENAXIR OMAR
Yadda taga Deedo ta takure
wuri daya tana wata irin
kyarmar sanyi, abin ya bala'in
bata tausayi, nan take taji wata
muguwar tsanar goggo ta kara
shiga ranta, wasu kwalla masu
zafi suka zubo mata, ta karasa
gaban ta, tana yi mata sannu,
Deedo kasa magana tayi,
hawaye ne kawai yake anbaliya
a fuskan ta. Hally ta ciro rigar
sanyin jikin ta, ta sanya mata
sannan ta tayar da ita zaune, ta
bude skool bag dinta ta fito da
biredi da shayi a cikin roban
coke, ta mika mata, kamar
tasan abinda yake damun ta,
ba tare da bata lokaci ba
Deedo ta ansa ta fara yagar
bread din nan, bata saurara ba
saida ta gama cinye shi tas,
sannan ta kora da ruwan
shayin tayi gyatsa, hally da
hawaye suka cika idon ta, ta
share ta fito da paracetamol ta
mika mata tasha. Sannan tace
"ki kwanta ki huta, zan fada ma
form master baki da lafia,
anshi sauran maganin nan ki
boye in anjima ki kara shan
guda biyu, kiyi hakuri Deedo ki
dauka wannan bakomai bane,
wata rana sai dai ki bada labari
in sha Allah,kinsan ita rayuwa
daman ta gaji haka, kuma BA'A
SHAN ZUMA SAI AN SHA
HARBI, ina ji a jikina akwai
ranar da goggo zata bukace ki,
ranar da bata da wani
mataimaki bayan ke, Allah ya
sauwake kinji" ta dago
idanuwan ta cike da kwalla,
bakin ta na kyarma tace
"nagode hally, Allah ya saka
maki da alkairi, ke kadai kike
sona duk fadin duniyar nan,
Allah ya biya ki da gidan
aljanna" ta rufe mata baki da
hannun ta, sannan ta share
mata hawayen, ta dau jakan ta
tayi mata sallama, ta fito ko
kallon inda goggo da ya'yan ta
suke bata yi ba, ta wuce ta bar
gidan.
Deedo na nan kwance kamar
gawa, dan ko motsin kirki bata
iyawa, goggo ta leka dakin,
tana kiran sunan ta amma
shiru, ta karasa gaban ta tasa
kafa ta hankada ta, cikin gigin
bacci tayi firgigit ta mike tana
zara idanu…
BA’A SHAN
ZUMA… 14
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Kafin ta karasa washewa taji
goggo ta damko gashin kanta
tayi waje da ita. Cikin kuka tace
"Dan Allah goggo kiyi hakuri,
wlh ban san mai nai miki ba"
ta watsar da ita a kasa tace
"yanzu zaki sani dan uban ki"
dakin ta ta wuce ta fito da
almakashi tace "bara na aske
wannan shegen kan, sai inga
ta karyar iskanci. Har ni zaki
bazawa wani banzan gashin ki
kina ji ina kira amma kika yi
shiru" ta fara ihu ta tashi ta
runtuma da gudu tayi hanyar
zaure, goggo ma ko bata yi
kasa a gwiwa ba ta daddage ta
cafko ta, Deedo tasa hannuwan
ta ta lullube gashin ta dasu,
amma ena goggo ta riga ta
damko wani gefe na gashin
mai uban yawa, bata yi wata
wata ba tasa almakashin ta
datse. Deedo ganin gashin ta
mai uban yawa a kasa yasa ta
kurma wani gagarumin ihu,
wanda hatta goggo saida ta
razana. Malam Ilu ne ya shigo
gidan da sauri, ganin abinda
goggo ta aikata yasa ya karasa
shigowa da gudu, sai da ya
daddage sannan ya hankadar
da goggo ta fadi kasa warwas!
Cikin daga murya yace "Ke
Batula kiji tsoron Allah, wlh ina
jiye miki ranar da alhakin
wannan yarinyar zai tambaye
ki, ke yanzu duk uban dukan
da kikai mata jiya bai ishe ki
ba, dan bakin ciki shine yau
har da aske mata gashi, ke
baki tunanin wata rana zaki
mutu ki bar abinda kika haifa?
Ya zaki ji idan wani ya rinka
cuzkuna musu irin yadda kike
wa wannan marainiyar Allahn,
in baki iya rike ta ki kai ta
gidan marayu mana.." kafin
mallam Ilu ya rufe bakin shi
goggo ta daddage ta cilla mai
almakashin da yake hannun ta,
bai tsaya a ko ina ba sai a
saman goshin shi, kafin yayi
wani motsi jini ya riga ya
wanke mashi fuska tasss!
BA’A SHAN
ZUMA… 15
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Ihu Deedo ta saka ganin jini ya
wanke wa mal. Ilu fuska, da
gudu ta ruga ta warto wani
kallabi na goggo da yake
shanye akan igiya tana kokarin
daure mai wurin, cikin gadara
da rashin nadamar abinda
goggo ta aikata ta taso da
sauri ta warce kallabin, tace
"wato iskanci naki har da irin
wannan kucakan kike yi? Mei
zaki samu a jikin wannan
tsohon? Lallai Deedo, daman
na dade ina zargin ku, sai
gashi zato na ya tabbata" ta
juya ta kalli mal. Ilu da yake
raba idanuwa tace "to wlh baku
isa ba daga kai har ita, kuma
idan ma kashe ta nake tana
farkowa akwai abinda ya
shalleh ka ne? Ince zama na
take yi a gidan ko? Ko ko
daman dan kuna labewa kuna
iskancin ku shine har zaka zo
ka tare mata, to ni Batula ba
kanwar lasa bace, duk wanda
yace zai ja dani wlh sai jikin
shi ya gaya mishi, wannan ma
da na maka kadan ne, dan a
ciki na so in caka maka
almakashin ka mutu kowa ma
ya huta dan banga amfanin da
kake tsinanawa wani ba a cikin
gidan nan" tana kaiwa nan, ta
bi ta gefen su, tasa kafa ta
hanbare Deedo ta kara gaba
abin ta..
Deedo wadda tausayin mal.
Ilu yasa ta manta da tata
larurar, tace "kayi hakuri baba,
ka lallaba kaje chemist a gyara
maka wurin kar wata cutar ta
shiga" yace "kar ki damu
Firdausi, dunia ce, ta ishi
Batula riga da wando har ma
da mayafi" ya mike dakyar yana
ganin jiri, ya wuce ya fita ya
bar gidan.
Allah mai iko, ashe wannan fita
ita ce fitar mal. Ilu ta karshe,
yaje zai tsallaka titi ba tare da
ya kula ba wani mai mota ya
banje shi, nan take ya ce ga
garin Ku nan.. Kulli nafsi
za'katul maut! Allah ya jikan
mal. Ilu da rahma amen!
BA’A SHAN
ZUMA… 16
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Hakika deedo taji rasuwan mal.
Ilu , tana tuna kalmominsa na
karshe akanta,gwaggo batayi
nadama ko kadan ba, don
taaziya ma sau daya ta leka,
Deedo kuwa harta rame, tafada
takara baki, asatin tafara zuwa
makaranta, cikin ikon Allah
saigashi wani malami yashigo
ajin, yadebi masu kokari uku,
ciki harda deedo sukaje ofishin
principal, nan ya sanar dasu
cewa gasa zasuyi wanda akwai
baki daga kaduna zasuxo don
su ga wannan gasa, akwai
kyaututtuka masu tsoka dazaa
raba, deedo tayi farin ciki
sosai, nan da nan akabasu
topic na debate
FEMALE EDUCATION IS MORE
USEFUL THAN MALE
EDUCATION IN THE SOCIETY,
inda ita zatayi supporting,
zuwa tayi tasami malamin
turancinn su tabashi don
yarubuto mata hujja dazata
kare kanta, yakuwa karba,
Ranan da tadawo gida duk
bakin cikin da gwaggo ke son
tusa mata, deedo taki bata rai
sai faraa take abun harya
damu gwaggo, washegari
dawurwuri tadebo ruwanta. Duk
da bayanta baigama warkewa
ba tanufi makaranta tanajira,
hally tayi mamakin ganinta
dawuri haka, malamin na isowa
takarba, tafara haddacewa, har
ajiye haly tayi tana koya
agabanta, dahaka tahaddace
komi akanta takuma yi
murajaan yadda zata fita
tabada tsokacinta
Ran jumaa aka taru a hall na
makaranta duk dalibai suntaru
don ganin wannan ranan da
zaaraba kyaututtuka, karfe
takwas na safe aka bukaci
suje, agyda kuwa tunda shehu
yazo yasanar da gwaggo
abunda zai faru , gwaggo ta
tsiri aiki ranan, harda sa deedo
wankin bango, deedo tanayi
zata fita tadauko ruwan kayan
miya tabata wai tafitar, tsabar
nauyinsa saidaya bata mata
kaya gashi batada wani
uniform din sawa, dawuri tafice
agydan don isa makaranta
BA’A SHAN
ZUMA… 17
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Hakika deedo taji rasuwan mal.
Ilu , tana tuna kalmominsa na
karshe akanta,gwaggo batayi
nadama ko kadan ba, don
taaziya ma sau daya ta leka,
Deedo kuwa harta rame, tafada
takara baki, asatin tafara zuwa
makaranta, cikin ikon Allah
saigashi wani malami yashigo
ajin, yadebi masu kokari uku,
ciki harda deedo sukaje ofishin
principal, nan ya sanar dasu
cewa gasa zasuyi wanda akwai
baki daga kaduna zasuxo don
su ga wannan gasa, akwai
kyaututtuka masu tsoka dazaa
raba, deedo tayi farin ciki
sosai, nan da nan akabasu
topic na debate
FEMALE EDUCATION IS MORE
USEFUL THAN MALE
EDUCATION IN THE SOCIETY,
inda ita zatayi supporting,
zuwa tayi tasami malamin
turancinn su tabashi don
yarubuto mata hujja dazata
kare kanta, yakuwa karba,
Ranan da tadawo gida duk
bakin cikin da gwaggo ke son
tusa mata, deedo taki bata rai
sai faraa take abun harya
damu gwaggo, washegari
dawurwuri tadebo ruwanta. Duk
da bayanta baigama warkewa
ba tanufi makaranta tanajira,
hally tayi mamakin ganinta
dawuri haka, malamin na isowa
takarba, tafara haddacewa, har
ajiye haly tayi tana koya
agabanta, dahaka tahaddace
komi akanta takuma yi
murajaan yadda zata fita
tabada tsokacinta
Ran jumaa aka taru a hall na
makaranta duk dalibai suntaru
don ganin wannan ranan da
zaaraba kyaututtuka, karfe
takwas na safe aka bukaci
suje, agyda kuwa tunda shehu
yazo yasanar da gwaggo
abunda zai faru , gwaggo ta
tsiri aiki ranan, harda sa deedo
wankin bango, deedo tanayi
zata fita tadauko ruwan kayan
miya tabata wai tafitar, tsabar
nauyinsa saidaya bata mata
kaya gashi batada wani
uniform din sawa, dawuri tafice
agydan don isa makaranta