Sashe 4
Baa Shan Zuma Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
BA’A SHAN
ZUMA… 09
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Deedo ce ita kadai tsaye
gaban borehole tana ta faman
buga famfo tun karfin ta, ga
kiraye kirayen sallar maghriba
ana ta kwadawa, amma bata da
yadda zata yi, dole ta debi
ruwan nan, in ba so take taci
na jaki a wurin goggo ba. Daga
gefe taji ana cewa "shine kika
zo kina ba kanki wahala bayan
nace ki daina buga famfon nan
zai iya yi miki illa a matsayin ki
na diya mace mai karancin
shekaru" ta juyo da dan
murmushin ta, tace "bana son
kullun ina sanya ka cikin
matsalolin rayuwa ta, nagode
da kulawar ka" Ado ya karaso
gaban ta yace "wuce ki zauna,
bara na ida cika miki" ganin
fuskan shi ba alaman wasa
yasa Deedo ta koma baya, ya
ida cika bahon ya dauko, yana
gaba tana bin shi a baya, dan
yanzu kullun shi yake dauko
mata ruwa, da sun zo zauren
gidan goggo, sai ya dora mata
ta shige. Haka nan kuma yaji
Allah ya dora mashi masifar
tausayin yarinyar, wani lokacin
har kudi yake bata amma bata
ansa, haka zai gaji ya maida
yan kudin shi cikin aljihu. Suna
karasowa zauren yace "to
matso ki ansa" ta matso ta
miko kanta, shi ma ya matso
zai dora mata, basu tantance
ba suka ji muryar goggo ta
fasa wani mugun ihu, Ado da
ya daga bahon ruwa zai
dorawa Deedo bai san lokacin
da bahon ya subuce ya fadi
kasa ba, goggo wani irin ihun
munafunci take kurmawa tana
salati tana cewa "Deedo daman
abinda kike yi kenan? Jama'a
ku taimaka mun na shiga ukku
na lalace, wayyo Allah na yan
iska har cikin zauren gida na"
kafin wani cikin su ya ce wani
abu, tuni wurin ya cika dam da
mutane masu zuwa masallaci,
yara da manya..
BA’A SHAN
ZUMA… 10-11
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Shidai Ado tsayawa yayi yana
mamaki, ikon Allah bata
karewa, gwaggo ta tara musu
jama'a sannan takiyin shiru
balle su fahimci me ake ciki,
cikin sanyin murya yace "ba
abunda kike tunani bane,
taimaka mata kawai nayi"
Ta katse shi da karfi tareda
cewa "kaidin banza kaidin wofi,
meya hadaka da ita? Lalata ka
zatayi don yanzu idonta a bude
yake gwara kadena bata
lokacinka"
Wata makwabciyarsu tace
"Kaga kai ado duk da taimako
kakeyi, amma kaga wa ita kake
jawa balai, donhaka ka kiyaye
kawai"
Kansa akasa ya amsa, nan
akadan fara watsewa gwaggo
kuwa tariko kunnen deedo
sannan tayi cikin gida da ita,
rufeta tayi adaki tasa shehu ya
tsinko bulali, ta sa ta kwanta,
ta zuba mata ruwan sanyi
tashiga zuba mata bulalinnan,
tas suka karye ajikinta, deedo
bata iya tashiba don
mazaunanta kumbura sukayi
tum, nan da nan jikinta yayi
jajur, sai hadiye numfashi
takeyi, domin kuwa kukanma
guduwa yayi yabarta ahaka,
Da ja jiki ta isa daki, tayi kuka
tagode Allah, takuma roki Allah
daya gaggauta fitar da ita cikin
wannan kangin datake ciki,
sallama taji tundaga tsakar
gida, muryar haly donhaka taji
gabanta yafadi, don zuwa
gidansu ba aladan haly bane,
gashi dare yarufa sosai,
gwaggo ce ta tareta tareda
cewa "mekuma kikazo yimata?"
"Assighnment fa aka bamu, toh
tabat nata shine nakawo mata
tana sauri zataxo gyda"
"Kokuma tana sauri taje gydan
saurayinta ba, dake a ke hada
baki ai"
"A a wlh gida fa kawai take
zuwa, bata tsayawa"
"Toh koma dai meye, ki tattara
kiyi kibar gydannan, minti biyu
nabaki"
Itadai haly jikinta narawa
tashigo , da tocinta ahannu
ganin halin da deedo take ciki
tasaka kara…
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Gwaggo tashigo tareda cewa
"meye kuma?"
" naganta kamar ta mutu ne,
gwaggo kitaimaka akaita asibiti
wlh zata mutu"
Ganin haly zata bata mata rai
yasa tajanyeta ta wullata waje
tarufo kofan, dakinta tawuce
batare tadamu da halin da
deedo take ciki ba
Haly akofar gidan hankalinta a
tashe tarasa wazatayiwa
magana, kuka nabin idonta
donhaka gida takoma tana
addua wa kawar tata,
Haka deedo takwana da asuba
kuwa gwaggo tashigo da
ruwan sanyinta, ta kwara mata
anma bata motsa ba, hakan
yasa taji jikinta yayi sanyi
tafara jijjiga deedo,harsai da ta
juyo fuskanta, jini tagani
naxuba, bashiri tamike tace
"shehu jeka kiramin malam
audu(likitam gargajiya),
shegiya tsinanniyar yarinya
zata tonsmin asiri, ta Allah
bataki ba "
Da gudu yafita, mituna kadan
saigashi yashigo
"Malam tayar min da yarinyyan"
"Anma dai kinsan cewa yaune
na hudu dana ke xuwa don
ceto rayuwarta, idan har bazaki
iya riketaba kikaita gidan
marayu mana"
"Kai tsaya banson raini!, kana
abu ba lissafi, ni meruwana da
mutuwarta ko ranta,ai inta
mutu zanfi kowa jin dadi,
damuwana kawai karta mutu
ahannuna"
Girgiza kai yayi donganin
jahilci a filin Allah
Ya dubata yaga dogon suma
ne, nan da nan yayi dabarunsa
sannan tafara tari, saidai jikin
baya motsawa, yajuyo yakalleta
sannan yace "tafarka saidai
dole kibari tayi jinyan jikin"
"Badamuwa naji" ficewa yayi
don bazai iya kallon wannan
bakim cikiba,
Yana ficewa tariko kunnen
deedo
"Bari ingayamiki ba mutuwa ko
hadiye ranki kikayi bazaki
mutuba, don wlh bazanje
prison akan yar mage ba.
Shegiya tsintacciya,
laananniyar ya, ido kamam na
mayu," hawaye ne kawai
yakebin idon deedo,
"Sannan kitashi kisan yadda
zakiyi kidebo ruwa yarana
zasuyi wanka!"
Tafice tanata guna guni, deedo
tayi godiya wa Allah kamar
yadda musulunci ta bukaci
kowani dan adam yake godewa
Allah bayana tir da halin
dayake ciki ba, musamman in
kashiga wani Hali, kamata yayi
kasa hakuri dangana kasaka
cewa Allah kadai zai taimakeka
yarufa maka asiri, shikadai
keda iko akanka , shike baka
jarabawa, kowani hali kake ciki
akwai wanda yafika wahala, sai
ka godemishi daya barka da
ranka. Wani yanemi rai
baisamuba , hakan nakara
karfin imani, donkuwa koda tayi
godiyan tariko bango, tabi
bango har jikin ginin sannan
tariko bahon tana bi da bango
harta isa bakin zauren jitayi
anhakadata dakarfi ta tsinci
kanta akasa
BA’A SHAN
ZUMA… 12
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tayi baya luu zata zube, Allah
ya taimaka tana dab da bango
ta dafa shi tun karfi har saida
hannun ta yayi kara, cikin
bacin rai goggo tace
"tsinanniya, ni zaki ja wa
sharri? Iyii? Zaki fita kina wani
bin bango kamar kadangaruwa,
wlh ko ki mike ki dauka bahon
nan ko na kwada miki wannan
iccen a gadon baya" ta nuna
mata wani katon icce da yake
rike a hannun ta. Bata jira taji
mai zata Kara cewa ba, ta
warci bahon, tayi waje cikin
sauri. Saida ta danyi nesa da
gidan sannan ta samu wuri ta
zauna ta dan huta, sannan ta
dau bahon ta karasa gaban
famfon ta fara tukawa, ta cika
shi, ta kinkimo ta dora a
kanta, ta fara zabga sauri zuwa
gaban goggo. Tana isa ta tarar
da tulin bargunan fitsarin
shehu, tana aje ruwan goggo
tace ta kama su ta wanke ta
shanya. Duk mai imani idan
yaga halin da Deedo take ciki a
wannan lokacin dole ya
tausaya mata, amma goggo da
yake ta kwashe kayan ta daga
gaban manzo, ko kallon ta bata
yi balle taji tausayin ta. Haka
yarinyar nan ta wanke kayan
nan, ta shanya, ga wata rawar
sanyi tana yi, Jikin ta yayi zafi
rau, haka ta cigaba da bauta a
cikin gidan nan, tana gamawa
ta lallaba ta shige dan akurkin
dakin ta, yau bata ma jin zata
iya zuwa makaranta, dan haka
ta dan shingida a saman
tabarmar kabar ta, tasa
hannuwan ta ta tallabe kanta,
saboda azabar ciwo da yake
mata. Muryar hally taji tana
kwada sallama, goggo tayi
caraf ta fito tace "ke ko
almunayar yarinyar nan, ba jiya
na kore ki ba, shine kika
lallabo kika dawo" ta dan galla
mata harara, sannan tace "nazo
ganin jikin Deedo ne, kuma ma
in kika yi hakuri ni ba nan zan
kwana ba" muryar Hadiza suka
jiyo tana cewa "ke wlh kar ki
wa mutane rashin kunya anan
kisha shegen duka" bata tanka
ta ba, ta bi ta gefen goggo zata
shiga dakin Deedon, ta ko jawo
kunnen ta, tace "wannan ya
zama shine zuwan ki na karshe
gidan nan, dan na kula ke kike
koya wa waccen shegiyar
iskanci, in ba haka ba wlh kika
kara zuwa sai na karya wannan
shegun kafafuwan naki masu
kama da na sauro" tasa kara,
tace "ni dai sake mun kunne
gaskia" goggo ta hankada ta,
tayi gaba, tana yi mata Allah ya
isa cikin zuciyar ta.
ZUMA… 09
NA
LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Deedo ce ita kadai tsaye
gaban borehole tana ta faman
buga famfo tun karfin ta, ga
kiraye kirayen sallar maghriba
ana ta kwadawa, amma bata da
yadda zata yi, dole ta debi
ruwan nan, in ba so take taci
na jaki a wurin goggo ba. Daga
gefe taji ana cewa "shine kika
zo kina ba kanki wahala bayan
nace ki daina buga famfon nan
zai iya yi miki illa a matsayin ki
na diya mace mai karancin
shekaru" ta juyo da dan
murmushin ta, tace "bana son
kullun ina sanya ka cikin
matsalolin rayuwa ta, nagode
da kulawar ka" Ado ya karaso
gaban ta yace "wuce ki zauna,
bara na ida cika miki" ganin
fuskan shi ba alaman wasa
yasa Deedo ta koma baya, ya
ida cika bahon ya dauko, yana
gaba tana bin shi a baya, dan
yanzu kullun shi yake dauko
mata ruwa, da sun zo zauren
gidan goggo, sai ya dora mata
ta shige. Haka nan kuma yaji
Allah ya dora mashi masifar
tausayin yarinyar, wani lokacin
har kudi yake bata amma bata
ansa, haka zai gaji ya maida
yan kudin shi cikin aljihu. Suna
karasowa zauren yace "to
matso ki ansa" ta matso ta
miko kanta, shi ma ya matso
zai dora mata, basu tantance
ba suka ji muryar goggo ta
fasa wani mugun ihu, Ado da
ya daga bahon ruwa zai
dorawa Deedo bai san lokacin
da bahon ya subuce ya fadi
kasa ba, goggo wani irin ihun
munafunci take kurmawa tana
salati tana cewa "Deedo daman
abinda kike yi kenan? Jama'a
ku taimaka mun na shiga ukku
na lalace, wayyo Allah na yan
iska har cikin zauren gida na"
kafin wani cikin su ya ce wani
abu, tuni wurin ya cika dam da
mutane masu zuwa masallaci,
yara da manya..
BA’A SHAN
ZUMA… 10-11
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Shidai Ado tsayawa yayi yana
mamaki, ikon Allah bata
karewa, gwaggo ta tara musu
jama'a sannan takiyin shiru
balle su fahimci me ake ciki,
cikin sanyin murya yace "ba
abunda kike tunani bane,
taimaka mata kawai nayi"
Ta katse shi da karfi tareda
cewa "kaidin banza kaidin wofi,
meya hadaka da ita? Lalata ka
zatayi don yanzu idonta a bude
yake gwara kadena bata
lokacinka"
Wata makwabciyarsu tace
"Kaga kai ado duk da taimako
kakeyi, amma kaga wa ita kake
jawa balai, donhaka ka kiyaye
kawai"
Kansa akasa ya amsa, nan
akadan fara watsewa gwaggo
kuwa tariko kunnen deedo
sannan tayi cikin gida da ita,
rufeta tayi adaki tasa shehu ya
tsinko bulali, ta sa ta kwanta,
ta zuba mata ruwan sanyi
tashiga zuba mata bulalinnan,
tas suka karye ajikinta, deedo
bata iya tashiba don
mazaunanta kumbura sukayi
tum, nan da nan jikinta yayi
jajur, sai hadiye numfashi
takeyi, domin kuwa kukanma
guduwa yayi yabarta ahaka,
Da ja jiki ta isa daki, tayi kuka
tagode Allah, takuma roki Allah
daya gaggauta fitar da ita cikin
wannan kangin datake ciki,
sallama taji tundaga tsakar
gida, muryar haly donhaka taji
gabanta yafadi, don zuwa
gidansu ba aladan haly bane,
gashi dare yarufa sosai,
gwaggo ce ta tareta tareda
cewa "mekuma kikazo yimata?"
"Assighnment fa aka bamu, toh
tabat nata shine nakawo mata
tana sauri zataxo gyda"
"Kokuma tana sauri taje gydan
saurayinta ba, dake a ke hada
baki ai"
"A a wlh gida fa kawai take
zuwa, bata tsayawa"
"Toh koma dai meye, ki tattara
kiyi kibar gydannan, minti biyu
nabaki"
Itadai haly jikinta narawa
tashigo , da tocinta ahannu
ganin halin da deedo take ciki
tasaka kara…
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Gwaggo tashigo tareda cewa
"meye kuma?"
" naganta kamar ta mutu ne,
gwaggo kitaimaka akaita asibiti
wlh zata mutu"
Ganin haly zata bata mata rai
yasa tajanyeta ta wullata waje
tarufo kofan, dakinta tawuce
batare tadamu da halin da
deedo take ciki ba
Haly akofar gidan hankalinta a
tashe tarasa wazatayiwa
magana, kuka nabin idonta
donhaka gida takoma tana
addua wa kawar tata,
Haka deedo takwana da asuba
kuwa gwaggo tashigo da
ruwan sanyinta, ta kwara mata
anma bata motsa ba, hakan
yasa taji jikinta yayi sanyi
tafara jijjiga deedo,harsai da ta
juyo fuskanta, jini tagani
naxuba, bashiri tamike tace
"shehu jeka kiramin malam
audu(likitam gargajiya),
shegiya tsinanniyar yarinya
zata tonsmin asiri, ta Allah
bataki ba "
Da gudu yafita, mituna kadan
saigashi yashigo
"Malam tayar min da yarinyyan"
"Anma dai kinsan cewa yaune
na hudu dana ke xuwa don
ceto rayuwarta, idan har bazaki
iya riketaba kikaita gidan
marayu mana"
"Kai tsaya banson raini!, kana
abu ba lissafi, ni meruwana da
mutuwarta ko ranta,ai inta
mutu zanfi kowa jin dadi,
damuwana kawai karta mutu
ahannuna"
Girgiza kai yayi donganin
jahilci a filin Allah
Ya dubata yaga dogon suma
ne, nan da nan yayi dabarunsa
sannan tafara tari, saidai jikin
baya motsawa, yajuyo yakalleta
sannan yace "tafarka saidai
dole kibari tayi jinyan jikin"
"Badamuwa naji" ficewa yayi
don bazai iya kallon wannan
bakim cikiba,
Yana ficewa tariko kunnen
deedo
"Bari ingayamiki ba mutuwa ko
hadiye ranki kikayi bazaki
mutuba, don wlh bazanje
prison akan yar mage ba.
Shegiya tsintacciya,
laananniyar ya, ido kamam na
mayu," hawaye ne kawai
yakebin idon deedo,
"Sannan kitashi kisan yadda
zakiyi kidebo ruwa yarana
zasuyi wanka!"
Tafice tanata guna guni, deedo
tayi godiya wa Allah kamar
yadda musulunci ta bukaci
kowani dan adam yake godewa
Allah bayana tir da halin
dayake ciki ba, musamman in
kashiga wani Hali, kamata yayi
kasa hakuri dangana kasaka
cewa Allah kadai zai taimakeka
yarufa maka asiri, shikadai
keda iko akanka , shike baka
jarabawa, kowani hali kake ciki
akwai wanda yafika wahala, sai
ka godemishi daya barka da
ranka. Wani yanemi rai
baisamuba , hakan nakara
karfin imani, donkuwa koda tayi
godiyan tariko bango, tabi
bango har jikin ginin sannan
tariko bahon tana bi da bango
harta isa bakin zauren jitayi
anhakadata dakarfi ta tsinci
kanta akasa
BA’A SHAN
ZUMA… 12
NA LUBABATU MAITAFSIR &
BENAXIR OMAR
Tayi baya luu zata zube, Allah
ya taimaka tana dab da bango
ta dafa shi tun karfi har saida
hannun ta yayi kara, cikin
bacin rai goggo tace
"tsinanniya, ni zaki ja wa
sharri? Iyii? Zaki fita kina wani
bin bango kamar kadangaruwa,
wlh ko ki mike ki dauka bahon
nan ko na kwada miki wannan
iccen a gadon baya" ta nuna
mata wani katon icce da yake
rike a hannun ta. Bata jira taji
mai zata Kara cewa ba, ta
warci bahon, tayi waje cikin
sauri. Saida ta danyi nesa da
gidan sannan ta samu wuri ta
zauna ta dan huta, sannan ta
dau bahon ta karasa gaban
famfon ta fara tukawa, ta cika
shi, ta kinkimo ta dora a
kanta, ta fara zabga sauri zuwa
gaban goggo. Tana isa ta tarar
da tulin bargunan fitsarin
shehu, tana aje ruwan goggo
tace ta kama su ta wanke ta
shanya. Duk mai imani idan
yaga halin da Deedo take ciki a
wannan lokacin dole ya
tausaya mata, amma goggo da
yake ta kwashe kayan ta daga
gaban manzo, ko kallon ta bata
yi balle taji tausayin ta. Haka
yarinyar nan ta wanke kayan
nan, ta shanya, ga wata rawar
sanyi tana yi, Jikin ta yayi zafi
rau, haka ta cigaba da bauta a
cikin gidan nan, tana gamawa
ta lallaba ta shige dan akurkin
dakin ta, yau bata ma jin zata
iya zuwa makaranta, dan haka
ta dan shingida a saman
tabarmar kabar ta, tasa
hannuwan ta ta tallabe kanta,
saboda azabar ciwo da yake
mata. Muryar hally taji tana
kwada sallama, goggo tayi
caraf ta fito tace "ke ko
almunayar yarinyar nan, ba jiya
na kore ki ba, shine kika
lallabo kika dawo" ta dan galla
mata harara, sannan tace "nazo
ganin jikin Deedo ne, kuma ma
in kika yi hakuri ni ba nan zan
kwana ba" muryar Hadiza suka
jiyo tana cewa "ke wlh kar ki
wa mutane rashin kunya anan
kisha shegen duka" bata tanka
ta ba, ta bi ta gefen goggo zata
shiga dakin Deedon, ta ko jawo
kunnen ta, tace "wannan ya
zama shine zuwan ki na karshe
gidan nan, dan na kula ke kike
koya wa waccen shegiyar
iskanci, in ba haka ba wlh kika
kara zuwa sai na karya wannan
shegun kafafuwan naki masu
kama da na sauro" tasa kara,
tace "ni dai sake mun kunne
gaskia" goggo ta hankada ta,
tayi gaba, tana yi mata Allah ya
isa cikin zuciyar ta.